Sunday 3 June 2018

KARANTA YANZU KASHA MAMAKI: HIKAYAR TSUNTSUWAR SIHIRI KOKILA

Tura Wannan Zuwa


Marubuci Sadiq Tukur Gwarzo, RN.
08060869978

A wani tsohon zamani daya gabata, anyi wata alkarya a gefen tsaunin Sontolo, sunan birnin Gazarwa, sunan sarkin su kuwa Riji.

Birnin Gazarwa birni ne mai daɗin zama da lambuna masu korayen ganyaye da ingantattun kayayyakin marmari. Ga koramu na kwaranyuwa, abin gwanin ban sha'awa.

Haka kuma sarki Riji ya kasance mai adalci ne ga mutanensa.

Mutanen wannan birni, sun camfa cewar duk wannan zaman lafiyar da walwalar da suke ciki gami da albarkar lambunansu, ya samu ne saboda wata tsuntsuwa mai suna Kokila.

Kokila na rayuwa ne bisa wata bishiya babba, wadda take a cikin wani ni'imtaccen lambu.

Lambun kuwa yana daf ne da fadar sarki Riji.

Kokila tsuntsuwa ce makauniya, amma tana da murya mai zaki, kuma gwana ce wurin rera wakoki irin nasu na tsuntsaye.
Bisa camfin mutanen Gazarwa, wakar da kokila ke rerawa ke kunshe da sihirin samar da zama lafiya gami da ni'ima awannan gari nasu.

To, acan bayan tsaunin Sontolon kuma dai, akwai wani garin har ila yau mai suna Maladawa.

Sunan sarkin Maladawa Jangero, kuma ya kasance mai aikata zalunci ga mabiyansa, saboda haka ma garin nasa ya kasance sam babu lumana da zama lafiya, kowa kagani a garin cikin ɓacin rai yake da fushi, don haka da zarar ka taɓa shi zakuyi husuma da faɗa, sannan amfanin gonarsu kuma ko kyau ba yayi.

Watarana sarki Jangero ya shirya tafiya izuwa wani wuri, akan hanyarsa ta dawowa sai ya ratsa ta Kasar Gazarwa, ai kuwa sai ya kamu da shaukin ni'imar dake gonakin wannan kasa.

Ko daya dawo gida, sai yake ta santi, har yana burin inama kasarsa zata kasance kamar Gazarwa.

Nan take Sarki Jangero ya kira wazirinsa, yace masa Tun da nake jin labarin Gazarwa, ban taɓa sanin haka take ba sai lokacin dana ratsa ta cikinta, don haka inaso kayi mini binciken hanyar da Sarkinsu yabi wajen mayar da daular kamar haka.

A wannan rana, wazirin Jangero bai kwana gida ba, sai ya ɓadda kama izuwa siffar fatake, ya nufi garin Gazarwa.

Da isarsa, sai ya rinka tambayar al'ummar garin fahimtarsu game da wannan ni'ima da suke ciki acikin hikima, yana kuma zagaye garin yana ta dube-dube abinsa.
Daga karshe, bayan ya kammala tattara bayanai, sai ya komo gida.

"Ran sarki ya daɗe, na samo sirrin bunkasar kasar Gazarwa" waziri ya faɗa ga Sarki Jangero cikin russunawa a sanda ya same shi a fada.

"Yawwa, yi maza ka sanar dani.." Jangero ya umarci wazirinsa.
Waziri yace "Ai wannan sirri yana jikin wata tsuntsuwar sihiri ne dake garin, sunanta Kokila".
Daga nan ya kwashe labarin duk hanyar da yabi izuwa Gazarwa, da kuma zantukan da mutanen kasar suka sanar masa.
Sarki Jangero yayi shiru yana tunani bayan yaji wannan labari, sannan yace "to kuwa idan haka ne, dole ne na maido da wannan tsuntsuwar izuwa masarauta ta"
Sannan ya kalli yankin da fadawansa ke zaune, ya nuna na tsakiya yana mai cewa "Sarkin yaki, yi maza kaje ka soma shirya dakaru, zamuje yaki Gazarwa domin kwato wannan tsuntsuwa mai sihiri"
Waziri yayi gyaran murya, sannan ya sake rankwafawa gaban sarki, yana cewa "Ranka ya daɗe, ban tari numfashin kaba, amma ina ganin matsawar mukayi yaki da Gazarwa, mune da Asara"
 Daga nan sai Yayi shiru yana jiran umarnin sarki, amma da yaji sarkin baice komai ba, sai yaci gaba da cewa
"Kasancewar akwai adawa da rashin zama lafiya a tsakanin sojojin mu akoda yaushe, hamayya tayi yawa tsakankaninsu, sojojin kasar da zamu kaiwa yaki kuwa cike suke da kaunar juna da haɗin kai, don haka ban jin zamuyi nasara a yanzu"

Sarki ya gyaɗa kansa sama yana mai cewa "haka ne waziri, amma menene abinyi".
Waziri yaci gaba da cewa "inaganin zaifi kyau ka nemi Sarki Riji ya baka aron wannan tsuntsuwa na tsawon wasu kwanaki cikin maslaha, nasan shi mai karimci ne, zaiyi wuya ya hanaka".
 "Shikenan, haka nan za'ayi". Sarki Jangero ya faɗa.
 Daga nan aka cigaba da fadanci, ba'a sake tayar da maganar ba har aka tashi fada.
Sati ɗaya da faruwar wannan lamari, Sarki Jangero ya haɗa tawaga sannan ya nufo Gazarwa. A tare dashi kyaututtuka me masu tarin yawa.

Sarkin Gazarwa Riji ya taryi bakonsa cikin karramawa, ya shirya masa bukukuwa don kayatar dashi tare da gabato masa da abinci kala-kala.

Bayan an natsa, sarakunan biyu suka ware domin tattaunawa.
"Mai martaba Sarkin Gazarwa, gani nayi muna kusanci da juna, amma bamu taɓa kawowa juna ziyara ba, wannan yasa na fara kawo ziyara gareka.."
Inji Sarki Jangero.

"Ai kuwa ka kyauta Mai martaba, wannan ziyara ta sada zumunci matuka a tsakanin mu" Sarki Riji ya faɗa cikin annushuwa.
"Sai dai kuma, na kamu da wata bukata yayin shigowa ta gareka.." Inji sarki Jangero.

"Haba ɗan uwa.." sarki Riji ya katse shi. "Faɗi bukatar ka kowacce irice, zaka sameta a gareni".

" Ina son ka bani aron Kokila." inji Sarki Jangero.
"Kokila???"

 Sarki Riji ya tambaya cikin kaɗuwa..
"Kwanaki kaɗan kurum zatayi a gareni.. Ina son sihirinta ya samarwa kasata zaman lafiya da yalwar arziki, gami da farin ciki... Ka taimakeni ya Maimartaba Sarki.."
Sarki Jangero ya faɗa yana mai magiya ga Sarki Riji.

 "Shikenan.." Sarki Riji ya amsa masa. "Zan baka arom kokila"
Abinda ya faru kenan, da Sarki Jangero ya shirya komawa gida aka haɗo masa kyaututtuka tare kuma da tsuntsuwar sihiri Kokila.

Amma dai, zuciyar sarki Riji cike take da sosuwar rabuwa da wannan tsuntsuwa, har ma sai daya zubda hawaye daga idanuwansa. Don haka ya umarci wasu amintattun bayinsa su biyar dasu tafi tare da sarki Jangero izuwa kasarsa Maladawa, su zamo masu hidima ga Kokila, kuma su tabbatar tana samun matukar kulawar daya kamata a koda yaushe.

Koda Sarki Jangero ya isa gida, bai tsaya wata-wata ba ya karɓe Kokila daga hannun bayin Sarki Riji, sannan yasanya aka cusata cikin wani keji na bakin karfe aka rufe.
Shugaban bayin Sarki Riji ya rugo da gudu gaban sarki Jangero, ya faɗi yana afi, yana cewa "Ranka ya daɗe, ina rokonka ka fitar da tsuntsuwar nan daga wannan kejin, domin hakan zai kuntata mata ne duba da yadda ta saba rayuwa cikin sakewa a lambu".

"Kai shashasha, rufe mini bai!" Sarki Jangero ya daka masa tsawa.
Sannan yaci gaba da cewa "Yanzu kokila mallaki nace, dole nayi abinda naso da ita".
Daga nan ya juya ga wazirinsa, yace "ina umartar daka sanya min waɗannan bayi a kurkuku, anan zasu ruɓe har tsawon rayuwarsu, kokila kuwa babu mai raba ni da ita".

Waziri ya russuna gaban sarki, yace "Ran sarki ya daɗe, a lura da abinda za'a aikata.. Ina ganin matukar kayi haka, sarki Riji ba zai kyale ba"
"Ai kuwa ba zai iya kawo mana hari ba akan tsuntsuwa. Nasan shi mutum ne mai son zama lafiya, bana tunanin zai sanya rayuwar dubun nan mutane cikin haɗari akan tsuntsuwa guda ɗaya tak.."
 Inji Sarki Jangero.

A karshe, babu yadda Waziri ya iya, dole yabi umarnin takadirin sarkinsa.
Sai dai kuma Kokila ta rasa walwala, duk da cewar an kawo mata 'ya'yan itatuwa da furanni kala-kala, amma taki yin wakar data saba balle ayi tsammanin sihirinta zai soma aiki.

Don haka a kullum, tashin hankula kurum ake samu a wannan kasa, k'ararraki suka yawaita a kotuna, fursunoni kuma suka cika dankam..

Wannan yasa Sarki Jangero yasa anemo masa mafarautan tsuntsaye, suka duba masa kokila amma sam basu samu wata lalura daga gareta ba.

Ana haka sai labari ya riski Sarki Jangero na wani tsoho mai suna Baba, mai shekaru sama da ɗari, wanda akace shi gwani ne a siddabaru da kuma gane matsaloli ko waɗanne iri ne.

Rannan sai ya kira wazirinsa yace yazo ya rakashi ga Baba domin a duba masa matsalolin dake damun kasarsa.
Bayan sun ɗanyi tafiya gefen gari akan dawakai suka iske sashin wata bukka, sannan daga nesa Waziri ya nunawa sarkin cewa ga inda Baba yake can.

Don haka Sarki Jangero ya sauko daga kan dokinsa, ya nufi cikin bukkar kai tsaye.
Da isarsa, wani tsoho ya gani zaune, ko wanne gashi na jikinsa yayi fari saboda tsufa, amma sam babu alamar rakwarkwaɓewa ajikinsa.

Sarki Jangero ya gabatar da kansa ga Baba, sannan ya sanar masa duk labarin sa.
"yanzu kai ka gamsu da cewar akwai sihiri a sautin tsuntsuwa kokila wanda yake samar da zama lafiya a kasa?"
Baba ya tambayi sarki bayan ya gama jin labarin sa.

"Kwarrai kuwa", inji sarkin. "Abinda kowa ke cewa kenan, gashi kuma na kawo ta masarautata don na samu biyan bukata amma takiyin sauti ko kaɗan".

"Amma dai Kai shashasha ne.." Inji Baba.
Sarki Jangero ya daka masa tsawa, "kai tsoho!!!", yayin daya mike tsaye zumbur cikin fushi yana kokarin zare takobinsa "nine fa Sarkin Maladawa Jangero, duk garin nan babu wanda baya shakka ta, kayi kaɗan ka kira ni da shashasha.."

Ko kallansa Baba baiyi ba, amma sai shima ya dakawa sarkin tsawa yana mai cewa "Yi mana shiru!!! Ka zauna kurum kaji abinda zan faɗa maka"
Aikuwa babu shiri, kwarjinin muryarƁBaba ta sanyayawa Jangero jiki, sai ya koma ya zauna.

"Kayi sani cewa Babu wani siddabaru a jikin tsuntsuwa kokila dake sanya zama lafiya a Gazarwa.
Wannan sirri yana tare da adalcin sarki Riji ne.. Yadda yake kyautatawa talakawansa, yake watsa soyayya da albarka ga mabiyansa, shiyasa kowannen su koyi daga gareshi har ni'ima take kwarara a garesu daga sama".

Baba yaci gaba da cewa "yanzu kwana nawa kokila tayi a tare dakai?". Sarkin yace "wata ɗaya".
ƁBaba yace "to na horeka kaje kaga Gazarwa, zaka samu babu abinda ya sauya daga ni'imar cikinta da zaman lafiyar dake gareta".
Saboda haka, zaifi kyau ka mayarwa da Sarki Riji tsuntsuwar sa ka kuma nemi yafiya, inyaso sai ka koyo sirrin halayensa na tafiyar da mulki".
Sarki Jangero yayi godiya ga Baba, sannan ya koma gida.
Kashe gari ya sake shiri saboda rashin natsuwa dangane da halin rashin zama lafiya da kasarsa take ciki yasa aka fito masa da bayin sarki Riji dake garkame a kurkuku, aka fito da tsuntsuwa kokila, sannan ya nufi Gazarwa da hanzari. Babban Burinsa shine aminci ya wanzu a masarautarsa.

Da zuwansa kuwa ya nemi afuwar sarkin Gazarwa Riji bayan ya kwashe gaskiyar labari ya faɗa masa.
Sarki Riji yace "haba ɗan uwa, ai wannan ba komai bane. Hakika kana da damar gyara kasar ka ta zama amintacciya kamar wannan".

Daga nan suka shiga tattauna hanyoyin wanzar da soyayya gami da adalci a kasa.
Tun daga nan, Sarki Jangero ya saduda, ya daina zaluntar talakwansa, ya zama abin kauna a garesu, kuma kafin wani lokaci sai da zaman lafiya ya samu a ko ina a kasarsa, albarkar noma ta wanzu duk shekara.. Har ma iskar kasar sai data sauya daga mai zafi izuwa iska mai daɗin shaka...

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin aiki Tukuru don jin dadin ku Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin website din akwai "Home" sai ku shiga,

mungode

Muryarhausa24.com Zata Kasance Babbar Kafar Yada Labarai aduk fadin Duniya domin Bunkasa Harshen Hausa, domin Zafafan Labarai ziyarci www.muryarhausa24.com

Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin Muryarhausa24.com aduk inda kuke a fadin Duniya farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24.com shine ta fito da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi
me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@
gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki daya Amin

Source by ©Muryarhausa24.com
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user