Tuesday 24 July 2018

Karanta Cikakken Tarihin Mesut Ozil: Abubuwan da Yakamata Ku sani dangane da Rayuwar Dan Wasan Kwallon Kafa Mesut Ozil - Hotuna da Cikakken Tarihi

Tura Wannan Zuwa
Ko Dan Ni Musulmi Ne Ake Kalubalanta Ta A Kungiyar Kwallon Kafa Ta Jamus?, Cewar Ozil


Mesut Ozil ya bayyana hakan ne bayan ya ajiye bugawa kasar Jamus wasa bisa kalubalantar sa da hukumar kwallon kafa ta kungiya da wasu magoya bayan kungiyar kasar suke yi don ya gana da shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan.

TARIHIN RAYUWAR MESUT OZIL A TAKAICE

An haifi dan kwallon ne wanda ya fito daga tsatson Turkawan da suka yi kaura zuwa Jamus a garin Gelsenkirchen, kuma yana cikin tawagar kasar da ta lashe gasar kofin duniya a 2014.

Ya buga wa kasar wasa sau 92 sannan sau biyar magoya baya na zabarsa gwarzon dan kwallon kasar tun daga shekarar 2011.
Sai dai tawagar kasar ta kasa kai wa zagaye na biyu a gasar kofin duniya ta Rasha, duk da cewa suna daya daga cikin wadanda aka yi hasashen za su lashe kofin.

Asalin sabanin

Ozil da Ilkay Gundogan na Manchester City dukkaninsu jamusawa kuma 'yan asalin Turkiyya sun sha suka daga hukumar kwallon kafa ta Jamus bayan ganawarsu da Recep Tayyip Erdogan a watan Mayu.

A cikin wata sanarwa, Ozil ya ce, "ziyarar ba ta shafi siyasa ba ko wani zabe."

"Ina da zuciya biyu, daya a Jamus daya kuma a Turkiyya", kamar yadda Ozil ya wallafa a Twitter.

"Wannan ni ya shafa na wakiltar ofishi mafi girma a kasar iyaye na."


Ozil, wanda mahaifiyarsa 'yar kasar Turkiya ce, ya kara da cewa "a lokacin da muka ci kofin duniya a 2014, sun dauke ni tamkar dan Jamus amma saboda wannan karon ba mu yi nasara ba, sai suka soma nuna min wariya. Ga abokan wasana irin su Close da Podiski su ma ruwa biyu ne amma ba a kalubalantarsu".


"Ni dan kasar Jamus ne a wurinsu a lokacin da muka yi nasara, amma ni dan ci-rani ne idan muka sha kashi," a cewar Ozil.

Ozil ya ce lokacin da yana karami, mahaifiyarsa ta horar da shi a kullum ya kasance mai girmamawa kuma kada ya taba manta asalinsa.

Daga baya kuma Ozil ya sake wallafa wani sako yana mai kalubalantar kafofin watsa labaran Jamus da suka dauki laifin rashin nasarar da kasar ta yi a gasar cin kofin duniya suka dora a kan hotunansa da shugaban Turkiya.


Ya ce "ba su soki rawar da na taka ba da kuma tawagarmu ba amma sun soki asali na da kuma yadda nake girmama shi.
"Wannan ya keta iyakar da bai kamata a keta ba, inda jaridu suka nemi dora alhakin kasar Jamus a kai na."


Bayan dan wasan ya gana da Erdogan a wani taro a Landan, inda Ozil ya ce sun tattauna game da kwallon kafa, sai jam'iyyar AK mai mulki a Turkiyya ta wallafa hotuna ana dab da zaben da Erodogan ya lashe.

'Yan siyasar Jamus da dama sun soki Ozil da Gundugan, suna masu bayyana shakku kan amincinsu ga mutunta tsarin dimokuradiyar Jamus.


Jamus ta soki shugaba Erdogan kan yadda yake murkushe abokan hamayyar siyasa bayan murkushe wani yunkuri na yi ma sa juyin mulki.

Ozil ya ce ba ruwansa da wanda ke shugaban kasa, ko dan Turkiyya ne ko Jamus, tunaninsa ba zai sauya ba.

Dan wasan Arsenal Mesut Ozil ya yi ritaya daga buga wa Jamus kwallon kafa yana mai cewa an nuna masa banbancin launin fata tare da cin zarafinsa saboda ya dauki hoto da shugaban kasar Turkiyya.



Nan bada dadewa ba cikakken Tarihin sa yana zuwa gare ku , kawai bayan 24 hours Ku sake bude wannan Post domin Karanta Cikakken Tarihin Saboda a halin yanzu Muna kokarin tattara Tarihin waje daya

Dubban Magoya bayan shi a shafin Twitter sun kalubanci lamarin.

Tarihin Ahmed Musa: Abubuwan da Yakamata Ku sani dangane da Rayuwar Dan Wasan Kwallon Kafa Ahmed Musa - Hotuna da Cikakken Tarihi

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Domin samun Labarai,Nishadi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, FADAKARWA,NISHADANTARWA, LABARIN WASANNI, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika sakon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun sakon ka/ki Mungode

Source: www.muryarhausa24.com.ng

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user