Wednesday 1 August 2018

Karanta Dalilin da yasa aka yankewa Cristiano Ronaldo Hukuncin Ɗaurin Shekara 2

Tura Wannan Zuwa
Ronaldo zai biya tarar dala miliyan 3.7, bayan daurin shekaru biyu da kotu ta yi masa. 


Sai dai kuma ba zai zauna gidan kurkuku ba

Wannan ya zo karshen kiki-kakar da ake da shi a kotu na tsawon lokaci inda mahukuntan kasar Spain suka zarge shi da kin biyan haraji a lokacin da ya ke wasa a Real Madrid.

Ronaldo dai ya musanta zargin da ake masa. An yanke masa wannan hukunci ne ranar Juma’a.

An zargi Ronaldo da kin biyan haraji har na Yuro milyan 5.7

Ronaldo mai shekara 3 a duniya, ba zai je gidan kurkuku ba, saboda dokar kasar Spain ta ce ko da an yanke wa mai laifi irin wannan hukuncin dauri, matsawar a karon farko ne, to ba zai je gidan yari ba, sai dai ya biya tarar kawai.

Amma kuma maimakon dauri, zai rika biyan wani sabon haraji na Yuro 250 a kowace rana har tsawon shekaru biyun da aka yanke masa, a madadin zaman gidan kurkuku.

Bayan wanna, Ronaldo zai biya tarar dala miliyan 3.7 da kuwa zunzurutun Yuro milyan 5.7 wadanda tun da farko ya ki biya a matsayin tarar da ta sa aka maka shi kotu.

Akwai kuwa tarar wata Yuro milyan daya da zai biya, a matsayin kudin ruwan da suka taru a hannun sa, a tsawon lokacin da ya ki biyan harajin.

Gaba daya dai Ronaldo zai biya tarar Yuro miliyan 19, wadanda idan aka auna su a sikelin naira, bilyoyin nairori ne masu yawa.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki Mungode

Source: Premium Times Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user