Tuesday 20 November 2018

Karanta Kaji: Zan Fitar da Talakawa Miliyan 50 daga Kangin Talauci cikin Shekaru 2 - Atiku Abubakar

Tura Wannan Zuwa
Ɗan takarar shugaban kasa karkashin jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya fara yakin neman zabenshi yau, Litinin ta shafinshi na sada zumunta inda ya fara da bayar da labarin cewa ya taso maraya kuma har sayar da itace yayi.



Yace ya sayar da itace a kan titunan garin Jada dake Adamawa amma Allah, ta sanadiyyar Najeriya ya daukakashi.

Yace idan Najeriya ta bashi irin wannan damar ya kai yanda yake a yanzu to shima yana da aikin gyara Najeriyar yanda zata baiwa kowane danta irin waccan dama.

Yayi kira ga 'yan Najeriya da su bishi akan wannan tafiya ta samar da rayuwa me kyau.

Yace idan aka zabeshi zai taimakawa kananan da matsakaitan masana'antu miliyan 50.

Yace wannan tsari zai samar da ayyuka miliyan 2.5 sannan cikin shekaru 2 mutane miliyan 50 zasu fita daga kangin talauci.

Yace kuma akwai wani tsari da zai fito dashi na horas da mata da maza miliyan daya duk shekara akan sana'o'i daban-daban.

Yace akan maganar shirinshi na canja fasalin Najeriya kuma zai samar da yanayin da jihohi da gwamnatin tarayya zasu samu kudin shiga fiye da da.

Ya kara da cewa ga wanda ke so ya karanta tsare-tsaren nashi zai iya yin haka a shafinshi na Atiku.org.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Hutu Dole

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user