Monday 19 August 2019

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN SHEIKH ABUBAKAR MAHMUD GUMI

Tura Wannan Zuwa
Sheikh Abubakar Mahmud Gumi, an haife shi ranar Juma’ar karshen watan Ramadhan na shekara ta 1343 ko 1345 Hijiriyya, wanda ya yi daidai da 1922 ko 1923 Miladiya, a garin Gumi a karamar hukumar Gumi cikin jihar Zamfara a tarayyar Nijeriya.


TARIHIN SHEIKH ABUBAKAR MAHMUD GUMI


Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya ba da gudummawarsa a fagen ilimi da ilimantarsa.

Kadan daga wallafaffun littafansa akwai littafi mai suna Nazamul Kadidatu Lamiya wacce ya yi don ta’aziyyar Abdullahi Bayero Sarkin Kano.

Da wata kasida ta Kafiya wacce ya yi ta a lokacin da yake dalibta a kasar Sudan mai baitoci 34.

Kuma ya yi tafsiri mai Suna RADDUL-AZHAN ILA MA’ANIL-KUR’AN, da kuma littafinsa mai suna AKIDATUSSAHIHATBI MUWAFAKATUS SHARI’A wanda shi ne ma muka fassara a cikin wannan littafin.

Da kumalittafinsa mai suna WURDINL-AZIM MINAL KUR’ANIL KARIM WAL-AHADISIL SHARIF.

Sheikh Abubakar Mahmud Gumi

Haka kuma akwai Tarjamar Al-Kur’ani Zuwa Harshen Hausa. Da kuma Tarjamar littafin Arba’una Hadis, zuwa harshen Hausa. Da kuma Tarjamar littafin Usuluddeen da Tauhid zuwa harshen Hausa, da kuma wani littafi maisuna Mir’atul Dullab Fee Masnadil Abwab, da dai sauransu.

Kuma ya fassara wasu littattafai masu yawa a cikin kasakasai da sidi da DVD kamar irin su Ahdari, Ashmawi, Iziyya da Risala da Mukhtasar Halil da Bukhari da Fatahul Majid da sauransu.

Tarihin Sheikh Abubakar Mahmud Gumi


Kuma ya sami kyauttuka na girmamawa a lokacin rayuwarsa kamar Malamin nan mutumin Siriya (Sham) mai suna Shaikh Sa’ad Yaseem-Assuri, wanda Malam (Sheikh Abubakar Mahmud Gumi) ya koyi karatun Kur’ani da Tajwid a wurinsa ya ba shi Shahada, da kuma Firimiyaan Arewa, Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakwato ya ba shi lambar yabo saboda da shi ne mai yi masa tarjama in ya je kasashen Larabawa a lokacin da yake raye.

Kuma Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ba shi lambar girmamawa ta kasa mai suna (C.F.R), haka kuma Jami’ar Islamiyah da ke Madina a kasar Sa’udi Arabiya ta sa shi daga cikin Malamai masu ba ta shawara har sau uku. Haka nan mai girma Jamal Abdulnasir wanda yake shugaban hadin kan kasashen Larabawaa lokacin da yake mulki, ya ba shi takardar girmamawa saboda yada addinin Musulunci a duniya.

Haka kuma Malik Faisal na kasar Sa’udi Arabiya ya ba shi takardar girmamawa saboda yada addinin Musulunci da ya yi a duniya.

Wadannan kadan ne daga cikin irin girmamawar da Allah ya yi masa.

MUTUWARSA

Sheikh Abubakar Mahmud ya rasu ranar Juma’a 11 ga watan 9 a shekarar 1992, sakamakon rashin lafiya.

Shugabanni da yawa sun halarci Jana’izar sa wanda aka yi a garin Kaduna, kamar su shugaban kasa Janar Ibrahim Badamasi Babangida, da Ministoci da Sarakuna da Talakawa na kasar nan da kuma ketare.

DUBA WADANNAN:

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN IMAM MALIK BN ANAS

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN SHEIKH JA'AFAR MAHMOUD ADAM

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN DR. ZAKIR NAIK

Karanta Takaitaccen Tarihin Mal. Aminu Ibrahim Daurawa

Ya rasu ya bar mata hudu da ‘ya’ya 30, maza da mata, da jikoki 60, maza da mata.

Zamu ci gaba Insha Allah.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode









TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user