Sunday 1 September 2019

Karya Kake Ka ce Jihar Ribas ta Kiristoci ce - Martanin Asari Dokubo ga Gwamna Wike

Tura Wannan Zuwa
Mujahid Dokubo-Asari ya fito fili a shafin sa na sada zumunta ya yi Allah wadai da abinda Wike ya aikata.


Mujahid Dokubo-Asari


Marubuci: Bangis Yakawada

“Abinda ka aikata abin kunya ne, kuma bari na jaddada maka. Jihar Rivers ba ta kiristoci bace, kuma har abada ba za ta zama tasu ba. Karya kake yi kai ba ma Kirista bane''. Kalaman da Dokubo ga gwamnan Ribas.

Wannan ya biyo bayan rushe masallacin da gwamnan yayi ne, sannan ya fito bainar jama'a yace jihar ta kiristoci ce kuma bai san inda wani masallaci yake ba balle ace ya rusa.

A maida martain da Mr Dokubo ya yi ya ce, ''Indai da gaske ba masallacin to me ya kawo  ka wajen? Ni ɗin nan memba ne na Masallacin Trans-Amadi, a nan nake yin Sallolina tare da duk iyalina, don haka karya kake kace babu masallaci a wurin''.

Dokubo ya tabbatar da cewa su suka hada kuɗi suka sai filin masallacin a hannun Chief Edward Sotonye Amadi, kuma suna da takardun shaidar sayen wurin.

Tsohon tsageran na Niger Delta ya zargi gwamnan da salwantar da kudin jihar wajen daukar nauyin takarar Gwamnan Sokoto, Aminu Tambuwal, wanda shi musulmi ne, amma kuma saboda munafunci ya zo yana nuna kiyayya ga Musulmin jihar Ribas.

LABARAI MASU ALAKA:

KALLI YADDA A SAKI HAUSAWAN DA AKA KAME A JIHAR LAGOS

Karanta Jadawalin Sunayen Ministocin Buhari 43 da Ma'aikatun Su

KALLI YADDA 'YAN NIGERIA SUKAI ABIN KUNYAR DA BA A TABA YI BA A TARIHIN DUNIYA

“Ka yi amfani da kudin Ribas ka ginawa kiristoci cibiyar ibada da kudin mu mun yi shiru ba mu ce komai ba, duk da muma a matsayin mu na 'yan jiha muna da hakki, saboda muma mun taimaka wajen gina wannan jihar''. Dokubo ke janyo hankalin Wike.

Yaci gaba da cewa ''Don haka wajibi ne Wike ya san cewa ba shi da ikon zabawa mutanen Rivers addinin da za su yi, kuma masallacin da ka rusa namu ne mu 'yan jiha, don haka ba za mu zura ido mu kyale ka ba''.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user