Monday 25 November 2019

Shin Zan Iya Zama Sanadin Shiriyar Abokina?

Tura Wannan Zuwa
Lallai kai ba ka isa ka shiryar da wani ba, sai dai kayi iya ƙoƙarinka wajen tunatarwa da jan hankali ga 'Yan uwa musulmai domin tunatarwa yana amfanar wa.

Allah ne yake Shiryar da Wanda Ya So

Marubuciya: Faridah Bintu Salis

Sau da dama wasu daga cikin ma'abota da'awa wajen da'awarsu ga bayin ALLAH su kan sanyawa kansu ƙunci har ma wasu sukan kauracewa da'awar a dalilin sunyi kira ba amsa ba, Toh kada kayi bakin ciki ka roka musu shiriya awajen ALLAH (SWT) domin ka sani baka isa ka shiryar da wani bawa zuwa ga hanya madaidaiciya ba face sai idan ALLAH ne ya shiryar dashi.

Domin lallai ALLAH (SWT) shi yake shiryar da wanda ya nufe shi da falalarsa kuma yake batar da Wanda ya riske shi da adalcinsa.

Kuma ALLAH (SWT) Ya fada acikin Alkur'ani Maigirma cewa: "Lallai kai ba ka shiryar da wanda kake so, sai dai ALLAH ne yake shiryar da wanda yake so." [Suratul Kasas aya ta 56]

Kuma ALLAH (SWT) ya fada acikin Alkur'ani Maigirma cewa: "Sannan Wanda ALLAH Yayi nufin shiryar dashi sai ya buda kirjinsa ga musulunci, kuma wanda yayi nufin ya batar dashi sai ya sanya kirjinsa ya zama mai kunci matsatstse, kamar yana takawa zuwa sama, kamar haka ne ALLAH yake sanya kazanta ga wadanda basa yin imani." [Suratul An'am aya ta 125]

Wannan Ayoyin suna kara tabbatar mana da cewa lallai ALLAH (SWT) shine mai shiryarwa ga Wanda yaso.

Hakanan Annabi (ﷺ) Yace: "Wanda ALLAH Ya shiryar dashi babu mai batar dashi, kuma wanda ya batar babu mai shiryar dashi."

Mutum Bai Isa Ya
Yahiryar da Wanda yake So ba

Don haka duk sonka da kaunarka ga wani naka ko dan'uwanka musulmi yabi hanyar shiriya bazai taba bi ba face sai idan ALLAH ne yaso, domin daga cikin Annabawan ALLAH akwai wanda mahaifinsa akwai wanda matarsa ne akwai wanda dansa ne amma basu bi wannan hanya ta shiriya ba saboda ALLAH (SWT) bai tabbatar da hakan ba.

Haka kuma mafificin Halitta Annabi (ﷺ) Ya sowa Bappansa Abu-dalib ya cika da wannan shiriya ta addinin ALLAH yayin mutuwarsa amma ALLAH (SWT) bai bashi sa'ar amsawa ba.

Kamar yadda yazo acikin ingantaccen Hadisi daga Musayyab daga Babansa yace: "Lokacin da mutuwa tazo wa Abu-dalib sai Manzon ALLAH (ﷺ) yazo masa kuma awajen akwai Abdullah Dan Abu-umayyah da Abu-jahl, sai yace masa: "Ya Bappana kace LA'ILAHA ILLALLAH, Kalma ce wacce zanyi maka hujja da ita a gaban ALLAH." Sai suka ce masa: yanzu ka bar addinin Abdul-mudallib?. Sai Annabi (ﷺ) ya maimaita masa, su ma suka maimaita masa, karshen abunda ya fada shine: yana kan addinin Abdul-Mudallib, yaki cewa La'ilaha illallah. Sai Annabi (ﷺ) Yace:

"Wallahi zan roka maka gafara matukar ba a hana ni ba."

Sai ALLAH Mai girma da buwaya ya saukar da ayar da take cewa: "Ba ya kasancewa ga Annabi da wadanda suka yi imani su nemar wa mushirkai gafara." [Taubah aya ta 113]

Kuma ya saukar game da Abu-Dalib ayar da take cewa: "Lallai kai ba ka shiryar da wanda kake so, sai dai ALLAH ne yake shiryar da wanda yake so." [Suratul Kasas aya ta 56] [Bukhari 1360 da Muslim 24 suka ruwaito]

Tarihi ya bayyana mana irin kulawar da Abu-Dalib yayi ga Annabin ALLAH da gudumawarsa ga musulunci amma ALLAH (SWT) bai bashi ikon furta wannan kalma ta "La'ilaha illallah" ba.

Da wannan ya kamata duk mai kira zuwa ga Shiriya zuwa ga hanyar ALLAH ya sani cewa ALLAH ne yake shiryar da wanda yaso kuma Ya sani shima ba wayonsa bane haka kuma ba dabararsa bace ALLAH Ya shiryar dashi ya batar da waninsa ba, sai dai hakki ne akansa yayi kira zuwa ga shiriyar ALLAH kuma ya tunatar kuma yayi addu'a ya roki ALLAH Ya dawwamar dashi akan shiryar, kuma ya shiryar da wadanda suka karkace daga hanyar ALLAH, kada kayi fushi kuma kada kayi bakin ciki, Lallai ALLAH ya kasance mafi sani  ga abunda yafi dacewa.

MAKALOLI MASU ALAKA:

Karanta Muhimman Abubuwan da Yakamata Ku sani Kafin ku Fara yin Taimako

KARANTA MUHIMMAN ABUBUWAN DA YAKAMATA KU SANI KAFIN KU FARA LALATA 'YA'YAN MUTANE

KARANTA INGANTACCIYAR HANYAR YIN MU'AMALA DA MUTANE

Ya ALLAH ka shirya damu cikin wadanda ka Shiryar bisa hanya madaidaiciya, kuma ka buda kirjinmu ga Musulunci, kuma kada ka sanya mu daga cikin wadanda zuciyarsu tayi kunci kuma ta Matse. (Ameen).

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user