Wednesday 20 November 2019

KARANTA INGANTACCIYAR HANYAR YIN MU'AMALA DA MUTANE

Tura Wannan Zuwa
Haƙiƙa Addinin Musulunci yazo mana da dukkan yadda zamu rayu cikin wannan duniyar cikin maslaha matukar muka bi dokokin ALLAH kuma muka bi umurnin Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) ta hanyar yin koyi da shi.

Hanyar Yin Mu'amala da Mutane

Marubuciya: Faridah Bintu Salis

Addinin Musulunci kamar yadda muka sani addini ne kammalalle, kuma addini ne wanda ya koyar damu dukkan yadda zamu rayu a wannan duniyar ta hanyar da zamu yi aiki acikinta sannan mu samu sakamako ranar gobe kiyama.

Hanyar Yin Mu'amala da Mutane

Al-Kur'ani da sunnah sun zo mana da bayanai daban-daban. Amma a takaicen takaitawa na takaita wannan dan rubutun ne domin tunatar da 'Yan-uwa game da HANYAR MU'AMALA DA MUTANE.

Wajibi ne mutum yasan hanyoyin da zai ringa mu'alantar 'Yan-uwa, domin ya kiyaye fadawa cikin hakkokin su kasancewar idan kayi wasa da hakkin mutane ta hanyar da bata dace ba toh hakika zaka yi dana sani, domin ALLAH (SWT) baya yafe Hakkin da ke tsakanin wani da wani face sai idan su suka yafi junan su.

Hanyar Yin Mu'amala da Mutane

Da wannan nake tunatar da 'Yan-uwa wasiyoyi guda tara (9) acikin suratul Hujurat dan kula dasu wajen mu'amala:

1. Bincike idan anzo maka da wani labari.

2. Sulhu a tsakanin mutane.

3. Yin adalci yayin yanke ko wani hukunci.

4. Kada ka ringa yiwa mutane izgilanci.

5. Kada ka aibata wani.

6. Kada ka ringa yiwa mutane Lakabi da sunayen banza.

7. Ka guji mummunan zato.

8. Kada ka ringa bibiyar wani kan dole sai ka gano aibinsa.

9. Kada ka ringa giban mutane (wato gulma).

MAKALOLI MASU ALAKA:

Karanta Amfanin Sada Zumunta Guda 20

Karanta Muhimman Abubuwan da Yakamata Ku sani Kafin ku Fara yin Taimako

Karanta Muhimman Abubuwa 10 da Yakamata Kowanne Miji ya Kula dasu Idan Zai Yi Magana da Matar Sa

Duk wanda ya kiyaye wadannan abubuwan a cikin mu'amalar sa da mutane, toh hakika zai rayu dasu cikin fahimtar juna da walwala.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user