Sunday 10 November 2019

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN JIHAR BAUCHI KASHI NA FARKO

Tura Wannan Zuwa
Kashi na ɗaya

ASALIN SUNAN BAUCHIN YAKUBU

Kafin muji asalin Bauchi, zamu fara ne da sanin sarkin Bauchi Yakubu wanda sunan sa yafi shahara tare dana ƙasar.

Tarihin Jihar Bauchi a Arewacin Nigeria


Marubuci: SADIQ TUKUR GWARZO

Ance a karni na goma sha takwas daf da soma yakin jihadi a kasar Hausa, wasu malamai biyu masu suna Mallam Adamu da Mallam Isyaku suka tashi daga Borno zuwa Ganjuwa, inda suka zauna ƙarƙashin kulawar sarkin garin na wasu ƴan shekaru.

Bayan nan sai suka tashi suka koma Kufu da zama, daga nan kuma sai suka ƙarasa Jetar.

Anan Jetar ne Mallam Isyaku yayi abota da wani mutum da ake kiransa da suna Daɗi. Shikuwa yana zaune ne a wani wuri da ake kira Tirwin.

Mallam Isyaku ya kan ziyarci abokinsa Daɗi a Tirwin, sai rannan Mallam Isyaku ya tafi wirin Daɗi inda ya tarar dashi tare da yaron sa mai suna Yakubu.

Bayan sun gaisa sun soma firar duniya, sai Daɗi yace masa "Wannan yaro da ka gani ɗa ne gareni, kuma shi ne idanuna, Allah kuwa ya sanya sonsa da yawa cikin zuciyata. Ina da ƴaƴa da yawa banda shi amma ina so Allah ya albarkace shi a inda yake duka. Yanzu kuwa na baka shi, ka zama uba da shugaba a gareshi, shi kuma ya zama ɗanka mai-yi-maka hidima, domin ya sami albarkar ka. Inda kake so duka ka tafi dashi, dukkan abinda kake so ya yi maka duka ka sanya shi yayi, domin kuwa ɗanka ne, kai ne mahaifinsa".

Abinda akayi kenan. Mallam Isyaku ya tafi gidansa tare da Yakubu ya cewa matar sa "Ga ɗanki nan".

Duk inda Mallam Isyaku zashi Yakubu na tare dashi, suna cikin haka har labarin Shaihu Usmanu ɗan Hodiyo ya zo musu. Mallam Isyaku ya tafi tare da Yakubu zuwa wurin Shehu Usmanu, ya zauna acan shekara da Shekaru yana karatun ilim.

Rannan sai Mallam Isyaku yayi niyyar tafiya ganawa da iyalinsa, amma baya da niyyar jimawa acan. Don haka ya tsammaci cewar idan ya tafi da Yakubu zai hana shi dawowa da sauri, hakan yasa ya shaidawa Shaihu Usmanu muradinsa tare da barin Yakubu a hannunsa. Daga nan sai yayi wa Yakubu bayani sannan ya tafi..

MAKALOLI MASU ALAKA:

Karanta Jerin Abinci Hausawa Kafin Zuwan Shinkafa 'Yar Kasashen Waje

KARANTA TARIHIN YADDA TURAWA SUKA AZABTAR DA AL'UMMAR YANKIN AREWACIN NIGERIA

KARANTA GUSHEWAR TSOFFIN AL'ADUN MU NA HAUSA A WANNAN ZAMANIN DA MUKE CIKI

Allah da ikonsa, sa'ar da Mallam Isyaku ya riski wani gari mai suna Yalwan ɗan Ziyal dake ƙasar Kano, sai cutar ajali ta ka ma shi, anan ya rasu. Don haka sai Yakubu ya cigaba da zama wurin shehu yana karatu, ya zama tamkar ɗa a gidan shehu. Har ma shehu ya aurar masa da ɗiyar abokinsa Mallam Bazamfare watau Yaya.

Zamu Ci gaba Insha Allah.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user