Friday 20 December 2019

'YAN AREWA SUN KAFA TARIHI A YANKIN KUDU MASO KUDANCIN NIGERIA SUN GINA JAMI'AR KIMIYA DA FASAHA

Tura Wannan Zuwa
Wannan shine hoton ginin katafariyar cibiya na horarwa a kan fasahar sadarwa wanda hukumar NITDA ta gina a cikin jami'ar jihar Rivers dake birnin Fatakwal, kwanaki biyu da suka gabata Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami yaje ya kaddamar da cibiyar a madadin gwamnatin Nigeria.

Yayin Bude Makarantar Kimiya da Fasaha


Marubuci: Datti Assalafy

Abin farin ciki garemu masoya Malam Dr Isah Ali Ibrahim Pantami, shine mutum na farko da ya fara gina wannan katafariyar cibiya a tsakiyar kudu maso kudancin Nigeria, sannan sai amintaccensa wato Malam Kashif Inuwa yazo ya karasa, wannan wani abu ne na tarihi.

An yiwa cibiyar lakabi a turance da "The Information Technology Innovation and Incubation Park Building" an kashe miliyoyin Naira kafin a gina cibiyar, mutanen yankin kudu maso kudancin Nigeria gaba dayansu sune zasu amfana da cibiyar.

Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Pantami a gurin kaddamar da cibiyar yace; lokacin da nake shugabancin hukumar NITDA, shugabanta na yanzu Kashif  Inuwa yana matsayin mai bani shawara akan harkokin gudanarwan ma'aikatar, na kawo batun gina irin wannan cibiya a kusurwa shida na fadin tarayyar Nigeria ta yanda za'a samarwa matasa aiki, a farfado da tattalin arzikin kasa.

Yayin Bude Makarantar Kimiya da Fasaha

Maigirma Ministan yayi la'akari da gurin da yafi dacewa a fara gina wannan cibiya saboda yawan masana'antu da yankin ke dashi, wanda zai inganta tattalin arzikin Nigeria, sai ya fara a yankin kudu maso kudancin Nigeria ba tare da la'akari da ya fara a yankinsa ba, saboda kyakkyawar manufa da kishin Nigeria.

Ministan yaci gaba da cewa, na tabbata idan aka gudanar da wannan cibiya bisa gaskiya da rikon amana yadda ya dace, cibiyar zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Nigeria, shugaban Kasa Buhari yayi alkawarin yin adalci a kowani sassa na Nigeria, shiyasa hukumar NITDA zata tabbatar da wannan muradi na shugaban kasa wajen gina irin wannan cibiya a kusurwa shida na fadin tarayyar Nigeria.., inji Ministan

A nasa jawabin, shugaban hukumar bunkasa fasahar sadarwan zamani na Nigeria (NITDA) Malam Kashif Inuwa  a gurin kaddamar da cibiyar, yace an gina wannan cibiyar ne a cikin jami'ar Portharcourt don daliban ilmi, manyan masana'antu da kanana, 'yan kasuwa da sauransu akan manufa na inganta tattalin arzikin Nigeria .

Malam Kashif Inuwa yaci gaba da cewa, gwamnatin tarayyar Nigeria karkashin shugabancin Muhammad Buhari tun a shekarar 2016 ta kafa kwamitin kwararru a harkokin kasuwanci da aka yiwa lakabi da "Presidential Enabling Business Environment Council" tare da taimakon bankin duniya (World Bank) domin kwamitin ya cimma matsaya akan abubuwa guda uku, na farko; a farfado da tattalin arzikin kasa, na biyu: a gina hanyoyin inganta tattalin arzikin kasa, sannan a gina al'umma.

Gwamnati ta fahimci cewa kimiyyar fasahar sadarwan zamani zai iya kawo mafita ga matsalolin tattalin arzikin kasa, shiyasa ta bada muhimmanci a kai, a sakamakon haka, yanzu bangaren bunkasa fasahar sadarwa a Nigeria ya wuce man fetur da gas wajen inganta tattalin arzikin kasa.., a cewar Malam Kashif Inuwa shugaban hukumar bunkasa fasahar sadarwan zamani na Nigeria (NITDA).

MAKALOLI MASU ALAKA:

Kalli Yadda Soyayya ta sa Wani Bawan Allah ya Sauya Sunan Shi Zuwa na Shugaban Kasa Muhammadu Buhari

Kalli Yadda Wani Dan Sanda Ya Harbi Wani Matashi Dalibin Computer Science Har Lahira

SHIN TA YA YA KAKE JIN MAGANAR DA WANI KE FURTAWA?

Ina kira ga 'yan uwana na arewacin Nigeria mu dinga sanya wadanann bayin Allah cikin addu'ah na fatan samun nasaransu, manufarsu mai kyau ce, babu shakka akan sun rike amanar da shugaba Buhari ya damka musu da gaskiya.

Muna rokon Allah Ya daukaka darajarsu, Ya sa dukkan jama'ar  Nigeria su amfana da rayuwarsu Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode





TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user