Tuesday 23 June 2020

Karanta Wadanda Yin Zakka Ya Wajaba A Kan Su

Tura Wannan Zuwa
Malamai sun haɗu a kan cewa Zakka tana wajaba a kan Musulmi, Baligi, Mai Hankali, kuma wanda ya mallaki Nisabi, tare da cika sauran sharuɗa.

Waɗanda Zakka Ta Wajaba akan Su

Amma sun yi saɓani a kan Yaro da Mahaukaci, wasu sun ce ba ta wajaba a kansu ba, wasu kuma suka ce tana wajaba, amma magana ta biyu ita tafi ƙarfi, saboda hadisai ingantattu da aiwatarwar sahabbai a kan haka.

Dabarani ya rawaito hadisi, kamar haka;-

"عن أنس بن مالك قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم، اتجروا في أموال اليتامى، لا تأكلها الزكاة.

Wato daga Anas (R.A) ya ce, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ku yi ciniki da dukiyar Marayu, domin kada Zakka ta cinye ta”. (Duba FiKhuz Zakkat juz’i na 1, sh:95 – 112.)

Wannan ya nuna cewa za a fitar da Zakka daga dukiyar yaro da ta mahaukaci.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Tushe/Asali: www.muryarhausa24.com.ng
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user