Friday 31 May 2024

Falalar Riga Liman Zuwa Masallacin Juma'a

Tura Wannan Zuwa Ga

Manzon Allah (SAW) ya ce: "Idan ranar Juma'a ta zo, a kowane ƙofar masallaci akwai Mala'iku , suna rubuta sunayen mutane ɗaya bayan ɗaya (gwargwadon lokutan da suka zo, daga wane sai wane a zuwa, to haka falalar da za su samu ya danganta da sammakonsu), idan Liman ya zauna sai su ɗage takardunsu, su zo su saurari huɗuba" Muttafaƙun alaih.


Falalar Riga Liman Zuwa Masallacin Juma'a
Hoto: NBC NEWS


{Wanda duk bai zo ba har sai bayan liman ya hau mimbari ya fara huɗuba, kenan bai samu shiga wannan rigista ba, to shi kam ya yi hasaran wannan falalar da waɗancan za su samu}.


A hanzarta a yi sammako domin a samu a shiga cikin rijistar Mala'iku.


Tushe/Asali: Zauran Ɗaliban Ilimi

TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user