Wednesday 4 October 2017

Maganar Gaskiya Ya kamata Buhari ya rika mutunta ni-Patience Jonathan

Tura Wannan Zuwa

Uwargidan tsohon shugaban Najeriya, Patience Jonathan ta bukaci shugaba Muhammadu Buhari da ya rika mutunta ta kamar yadda mai gidanta ke mutunta A’isha Buhari bayan kayin da suka sha a zaben 2011.

Patience Jonathan ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin, in da kuma ta koka kan yadda hukumar yaki da cin hanci da rashwa, EFCC ta sanya ta a gaba saboda zargin al’mundahana.

Mrs. Jonathan ta ce, hukumar EFCC na binciken ta ne saboda rawar da ta taka a lokacin shirye-shiryen zaben 2015 da ya kawo karshen mulkinsu a karkashin jam’iyyar PDP.
Gabanin gudanar da zaben dai, Patience Jonathan ta bayyana shugaba Buhari a matsayin mutum mai raunin kwakwaluwa.

Uwargidan ta kara da cewa, abin da ya faru a lokacin yakin neman zaben, bai kamata ya zama silar musguna ma ta ba a yanzu.
Har ila yau, Patience Jonathan ta bukaci Buhari da ya ja kunnen mukaddashin shuganam hukumar EFCC, Ibrahim Magu da ta ce, ya fito ne don ganin bayan iyalinta.

A cewar Patience, ya kamata Buhari ya dauki darasi daga salon shugabancin Donald Trump na Amurka, wanda ta ce, bai damu da sha’anin uwargidan Barack Obama ba da ya mika ma shi mulki.

.
Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka  dadinkowa24.blogspot.com mungode
.
Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com
.
Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri
.
ALLAH yabar Zumunci Amin🙏
.
.
Source By ©Abdurrahman Gambo Ahmad

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: