Saturday 14 April 2018

Karanta Kaji: Ba Don Su Kwankwaso Ba Da Buhari Bai Zama Shugaban Kasa Ba - Sule Lamido

Tura Wannan Zuwa

Tsohon gwamnman jihar Jigawa Alhaji Sule Lamido ya ce taron da PDP ta yi a jihohin Jigawa da Katsina ne ya firgita APC har shugabannin jam'iyyar suka roki Shugaba Muhammadu Buhari ya fito ya ayyana cewa zai sake yin takara.

A wata hira da ya yi da BBC Sule Lamido ya ce : ''Ai taron da aka yi a Jigawa da na Katsina shi ya firgita su, suka ce ranka ya dade gara fa ka zo, domin yadda aka yi taron nan na Jigawa da Katsina, idan ba ka zo ka ce za ka yi takara ba mun shiga uku...''

A ranar Litinin ne Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana aniyyarsa ta kara tsayawa takara a zaben 2019.

Tsohon gwamnan ya kara da cewa APC da Buharin sun yi hakan ne domin su samu dan hutu na ''Tsunamin'' da PDP ta yi a jihohin biyu a tarukanta.

Ya ce sai ma jam'iyyar tasu ta yi irin taron a Sokoto da Kaduna da Kebbi kafin kuma ta yi na Abuja lokacin da hankalin shugaban da jam'iyyarsa za su fi tashi.

Tsohon ministan harkokin wajen ya ce ba su da wata fargaba kan ayyanawar da Shugaban ya yi cewa zai sake yin takara.

"Domin ai 'yan PDP ne suka haife APC, saboda haka Buhari jikansu ne, kuma ''don zai yi takara mene ne abin damuwa?''

Sule Lamido ya ce tun da Buhari yake tsayawa takara sau uku ko hudu bai taba cin zabe ba.

Ya ce sai da gwamnonin PDP biyar da "wasu jiga-jiganta irin su Atiku da Wamakko da Goje da Abdullahi Adamu da Kwankwaso da Bukola da sauransu suka mara masa baya."

Kuma ya ce ko da ma Buharin zai sake takara ai wadanda suka mara masa baya ya ci zabe a yanzu sun bar APC sun koma gidansu PDP, don haka ba su da wata fargaba a kan takararsa.

"Domin daman shi a karan-kansa bai taba cin zabe ba," in ji shi

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: