Thursday 23 August 2018

HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN (40) KASHI NA 6 - HIKAYAR TA DAUKI HANKULAN DUNIYA SOSAI

Tura Wannan Zuwa
Lokacin da shugaban barayi ya koma cikin daji wajen 'yan uwansa, ya shaida musu cewa ya gane gidan Ali Baba. Dabarar da za su yi su kashe shi, ba tare da sun ja hankalin jama'ar garin ba ita ce, yana so su tafi inda suke boye dabbobinsu, su zo da jakai goma sha tara, sannan su shiga cikin kasuwar garin su siyo jakunkuna na fata, wadan da ake dura wa mai, manya-manya wadan da mutum zai iya shiga cikinsu, guda talatin da takwas.



Ya ci gaba da cewa, "Idan muka hada wadan nan dabbobi da kuma jakunkunan dura mai, kowane mutum daya zai shiga cikin jaka daya da takobinsa, jaka dayar da za ta rage, zan dura man girki a cikinta. Zan dora ku gaba daya a kan jakai, duk mutum biyu jaki daya. Mutum na karshe zan dora shi tare da jakar da take da mai. Ni kuma zan yi shigar farke, na kora jakunan nan zuwa cikin gari. Zan dakata har zuwa faduwar rana sannan na shiga cikin gari, na je gidan mutumin na shaida masa cewa ni farke ne, na kawo man girki ne, ga shi dare ya yi ban samu shiga kasuwa ba. Ina so ya taimaka mini da wurin da zan sauke kayana a gidansa, idan gari ya waye sai na dauka na shiga kasuwa."

Shugaban barayi ya ci gaba da cewa, "Na san cewa zai yarda da bukatata. To, zan sauke ku na bar ku a wajen. Idan na ji gari ya yi shiru, kowa ya yi barci, zan zo na rika taba kowace jaka, duk wanda ya ji na taba jakarsa to sai ya fito, lokaci ya yi ke nan da za mu aikata abin da za mu aikata. Mu kashe shi da iyalinsa duka, sannan mu kwashe dukan dukiyar da take gidan, mu dora wa dabbobin nan mu koro su mu dawo. Ina fatar kun fahimce ni."

Sauran barayi suka ce sun fahimta. Ya rarraba su, ya aika wasu su zo da jakai, sannan ya aika wasu su tafi cikin gari su siyo jakunan dura mai da kuma man da zai cika jaka daya. Duka suka tafi neman abin da shugabansu ya umurce su da samowa.
Bayan kwana biyu barayin nan suka gama shirinsu tsaf. Kowane barawo ya shiga cikin jaka daya rike da takobinsa. Da suka gama shiga gaba daya. Shugaban barayi ya yi sadi da su a kan jakai, duk jaki daya ya dauki barawo biyu a cikin jaka. Jaki na karshe ya dauki barawo daya da jakar mai.

Shugaban barayi ya canja kamanninsa, ya yi shiga kamar farke, ya kora jakai dauke da barayi suka nufi cikin gari. Bayan tafiyar wani dan lokaci, suka isa bakin gari, dab da rana za ta fadi. Da shigarsu cikin gari, shugabn barayi ya kora dabbobin nan ya nufi gidan Ali Baba da su. Yana isa kuwa ya yi sa'a da Ali Baba ya dawo daga kasuwa, zai shiga gida ke nan, barawo ya dakatar da shi.

Bayan sun gaisa, sai barawo ya ce wa Ali Baba, "Ni farke ne, na zo da man girki ne domin kai wa kasuwa na sayar, ga shi dare ya yi mini ban samu shiga kasuwar ba, ko zan samu alfarmar masauki a wurinka da kuma wurin da zan sauke kayana kafin gobe da safe na shiga kasuwa?"
Ali Baba ya ce, "Wa zai ki bako? Ai bako rahama ne. Babu komai, shigo da kayanka daga ciki ka sauke kafin Allah ya kai mu gobe. Zan dawo na nuna maka dakin da za ka kwana idan ka gama sauke kayan." Barawo ya yi ta godiya, kamar mutumin kirki. Ali Baba kuwa ya wuce cikin gida, ya bar barawo ya na sauke kayansa a farfajiyar gidan.

Da Ali Baba ya shiga cikin gida, sai ya fada wa matarsa da kuyangarsa Murjanatu cewa ya yi bako. Ya ce, "Farke ne ya zo da man girki zai kai kasuwa ya siyar amma dare ya yi masa, don haka zai kwana a nan gidan tare da kayansa zuwa gobe da safe. Yanzu zan fita zuwa farfajiyar gidan mu kara gaisawa da shi, a kai mini abinci na can, za mu ci tare." Suka amsa masa da to. Ya fita.
Ko da ya fita ya tarar da shugaban barayi ya gama sauke kayansa. Ali Baba ya nuna masa dakin da zai kwana. Barawo ya kara yin godiya, sannan ya ce wa Ali Baba yana so ya nuna masa cikin gari domin bude ido, tun da shi bako ne. Ali Baba ya ce masa to, amma ya dakata sai sun ci abinci tukuna.
Murjanatu ta kawo musu abinci, har ta juya za ta tafi sai Ali Baba ya ce da ita, "Idan mun gama cin abinci za mu shiga cikin gari ni da bakona, akwai kifi na nan na siyo, ina so ki soya mana shi kafin mu dawo daga cikin gari." Murjantu ta amsa cikin girmamawa, ta tafi.

Bayan Ali Baba da barawo sun gama cin abinci, sai suka tashi suka nufi cikin gari. Ita kuma kuyanga Murjanatu ta dauko kifi ta nufi dakin dafa abinci domin soyawa kamar yadda aka umurce ta. Bayan ta hura wuta, ta dora tasar suya, sai ta jawo jakar da ake ajiye mai a ciki, sai ta ji ta kwambar babu komai a ciki. Ashe ta manta sauran man ne ta yi abinci da shi. Ga shi dare ya yi ballantana a tafi kasuwa a siyo. Nan take sai ta tuna, "Af! Shin bakon maigida mai ne ya zo da shi domin siyarwa kasuwa ba? Bari na je wurin da ya sauke man, na debo wanda zan soya musu kifin da shi, alabashi idan maigida ya dawo sai in fada masa, sai ya saye jakar man da na diba gaba daya."
Ta dauki abin dibar mai ta nufi inda shugaban barayi ya sauke kaya. Tana zuwa sai ta taba jakar mai daya za ta bude, sai ta ji an ce, "Lokaci ya yi ne?" Sai abin ya bata mamaki, nan da nan ta gane abin da ake shirin kulla wa maigidanta, sai ta canja murya kamar namiji ta ce, "Da saura!"
Ta nufi wata jakar za ta buda, sai ta ji an ce, "Lokaci ya yi ne?" Ta kara canja murya ta ce, "Da saura!" Sai da ta bi duka jakunkunan nan guda talatin da bakwai, ta gane duka mutane ne a cikinsu, sai guda daya ce kurum ta ke dauke da mai. Ta ciccibi jakar da take da mai, ta nufi dakin girki.

Da isarta dakin girki, sai ta sauke tasar suyar kifi ta dora babbar tukunya, ta juye man nan gaba daya a cikin tukunyar. Ta tafasa man sosai har sai da ya tafasa. Ta diba yadda za ta iya dauka, ta dauki shantu ta tafi wurin barayin nan. Idan ta je ga jaka sai ta tura shantu a ciki, ta dura tafasasshen mai a cikin jakar, tun barawo na motsi har sai ta ji ya yi shiru, ya mutu. Haka ta bi su daya bayan daya, tana kashe su da tafasasshen mai, har ta kashe su duka. Sannan ta soya kifin da aka ce ta soya.
Lokacin da Ali Baba da shugaban barayi suka dawo daga yawo cikin gari, Murjanatu ta kawo musu kifi suka ci. Da suka gama suka yi sai-da-safe da juna, barawo ya shige dakinsa, bai san abin da ake ciki ba, shi ma Ali Baba ya shige cikin gida.

Ita kuwa Murjanatu da ta shiga dakinta ta rufe kofa, sai ta bude taga tana kallon abin da zai faru a farfajiyar gidan idan shugaban barayi ya gane an kashe masa mutane.
Can da dare ya tsala, gari kowa ya yi tsit, sai Murjanatu ta ga shugaban barayi ya bude dakinsa a hankali ya fito, ya nufi inda jakunkunan mai suke. Ta ga ya taba daya, ya jira bai ji motsi ba. Ya kara taba wata, babu motsi. Ya bi su gaba daya ya taba, babu mai motsi. Sai ya bude daya, domin ya ga ko barci ne ya dauke su. Sai Murjanatu ta ga ya ja da baya cikin alamun jin tsoro. Daga nan sai ta ga ya yi sauri ya nufi kofar fita daga gidan, ya bude, ya arce.


Murjanatu ta mayar da tagar dakinta ta rufe, ta tabbata cewa maigidanta ya tsallake wannan tarko, sai dai ba ta san da wane shiri wancan barawon da ya tsallake zai dawo ba, ko wane irin tarko zai sake kafa wa Ali Baba? Ta kwanta kan gadonta tana jiran gari ya waye ta fada wa Ali Baba halin da ake ciki.


Ga waɗanda Basu samu damar Karanta Hikaya ta Biyar ba to ga tanan mun kawo Muku..

HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN (40) KASHI NA 5 - HIKAYAR TA DAUKI HANKULAN DUNIYA SOSAI

Za mu ci gaba....Ranar  Alhamis Insha Allah

Ku ci gaba da Kasancewa da Mu  a www.MuryarHausa24.com.ng domin samun ci gaban wannan ƙayataccen Labarin...

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.muryarhausa24.com.ng
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user