Thursday 12 September 2019

Karanta Dalilin da Yasa ake Tsare da Sarkin Waka Nazir M. Ahmad a Gidan Yari

Tura Wannan Zuwa
Wata kotu a jihar Kano ta tsare Naziru Ahmed Sarkin Wakar Sarkin Kano a gidan yari sakamakon rashin tantance wadanda za su tsaya masa.

Sarkin Waka Nazir M. Ahmad

Yanzu shahararren mawakin yana tsare ne a gidan yari na unguwar Goron Dutse da ke Kano.

Tun da fari dai kotun ta bayar da belinsa a ranar Alhamis bisa sharadin kawo wandada za su tsaya masa da tare da bayar da naira 500,000 da kuma kawowa kotu fasfonsa na fita kasashen ketare.

Gurfanar da fitaccen mawakin na zuwa ne bayan da rundunar 'yan sandan jihar Kano da ke Najeriya ta gurfanar da shi a gaban kuliya.

Lauyan Nazir Ahmad Barista Sadik Sabo Kurawa ya shaida wa BBC cewar da zarar sun kammla matakan tantancewar zuwa gobe Juma'a za a saki wanda suke karewa.

Ana tuhumar Naziru ne kan wasu wakoki da ya yi kusan shekaru hudu da suka gabata.

Wakokin sun hada da Gidan Sarauta da Sai Hakuri.

An kama mawakin, wanda shi ne sarkin waka na Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ranar Laraba da yamma.
Ranar Alhamis ne kotun ta bayar da belinsa bisa sharadin cewa zai bayar da fasfo dinsa da kuma samar da mutanen da zasu tsaya masa.

Mutanen sun hada da dagacin unguwar da yake zaune da ma'aikatan gwamnati biyu, kuma zai biya kudi ₦500,000.

Kakakin rundunar 'yan sandan, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya  shaida wa BBC cewa sun kama mawakin ne "saboda kalaman batanci" da ya yi a cikin wasu wakoki.

Ko da yake bai yi cikakken bayani kan kalaman da suke zargin mawakin da yi ba, ya bukaci wakilin BBC ya bi su kotu inda za a gurfanar da Naziru M. Ahmad domin samun cikakken bayani.

Sai dai Malam Aminu Saira, dan uwan mawakin, ya sanar da BBC cewa 'yan sanda sun sanar da su cewa gwamnatin jihar Kano ce ta sa aka kama shi ta hannun hukumar tace fina-finai ta jihar Kano.

A cewarsa, "An kama Naziru ne saboda fitar da wani kundin waka da ya yi mai suna 'Gidan Sarauta' da kuma 'Sai Hakuri'. Mun yi kokari a ba mu belinsa jiya [Laraba] da daddare amma an ki."

Sai dai hukumar tace fina-finai ta jihar Kano bata ce komai a kan batun ba, domin kokarin da muka yi na ji daga gare ta kawo yanzu ya ci tura.

Dan uwan nasa ya kuma ce jami'an 'yan sanda sun je gidan mawakin, kuma sun yi bincike amma babu abin da suka dauka.

Masu lura da al'amurn yau da kullum a jihar Kano na ganin akwai siyasa cikin lamarin, ganin cewa Sarkin Waka Naziru mai ra'ayin Kwankwasiya ne, wadda kungiyar siyasa ce da ke adawa da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Kano.

Wasu kuma sun ce akwai wata waka da Nazirun ya rera, wadda a cikinta suka ce ya yi kalaman da suka bata sunan gwamnan Kanon.

A 'yan watannin da suka gabata, wasu mawaka har da 'yan fina-finan Hausa sun sami matsala da Kano State Censorship Board, hukumar da ke tace bidiyo da fina-finai ta jihar Kano.

LABARAI MASU ALAKA:

KARANTA KAMA DARACTAN FILM A KANO ZALUNCI KO ADALCI?

DAGA YAU DOLE NE SAI MASU TARBIYA NE ZASU YI FINA-FINAN HAUSA - SHEHU HASSAN KANO

BABBAN BURINA A DUNIYA IN AURI JARUMA HASSANA MUHAMMAD - FURODUSA ABUBAKAR MAISHADDA

Cikin wadanda aka kama a baya akwai Sadiq Zazzabi da Sanusi Oscar, wadanda a halin da ake ciki su ma suna fuskantar shari'a kan wasu tuhume-tuhume da hukumar tace fina-finan ta shigar da kara a kai.

Insha Allah nan bada dadewa ba wakilin shafin Muryar Hausa24  zai kawo muku cikakken tarihin Nazir M. Ahmad (Sarkin Waka) .

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








Source: BBC HAUSA
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user