Thursday 31 October 2019

BAI KAMATA AYI SHIRU AKAN WANNAN ZALUNCIN BA FA

Tura Wannan Zuwa
Ko kunsan cewa a halin yanzu Likitoci sun tabbatar da cewa daya daga cikin yaran nan guda 9 da aka Kubutar a Kano anyi mata Fyad'e yafi a qirga lokacin da take hannun tsinannun inyamuran da suka Sace ta daga gaban iyayenta? Likitocin sun qara da cewa a halin yanzu Yarinyar tana Asibiti kuma anyi mata lahani a gabanta(Farjinta) banda zargin da ake na cewa Wataqila ma ta kamu da wata cuta.


'Yan Arewa Bamu da Hankali

Marubuci: Mubarak Musa Al-mubarak

Ko kunsan cewa Yunusu Yallow a halin da ake ciki Gwamnatin Jihar Bayelsa tana shirin yanke masa hukuncin zalunci a bisa laifin da bai aikata ba.? Yanzu haka Gwamnan Bayelsan da kansa ya tanadi Lauyoyi masu Muqamin SAN da kuma qananun Lauyoyi wadanda sune zasu taimakawa GWAMNATIN wajan aiwatar da wancan zaluncin akan Yunusa..

Baya ga Haka ana zargin Gwamnan ya bawa Dukkanin Sarakuna da Al'ummar jihar tasa ta Bayelsa Umarnin cewa suyi gum da bakin su kuma kar su sake su shiga maganar ko da wasu qungiyoyi daga nan Arewa zasu je domin neman goyon bayansu akan wannan Shari'a.

Sannan kuma wani zargin ya qara nuna cewa Gwamnatin Bayelsa din ta dauke ita waccen yarinya Mai suna ESE ORURU wadda ake zargin Yunusa din akan ta, tare da Mahaifiyarta an killace su a cikin gidan Gwamnatin Jihar da nufin hana dukkanin wasu qungiyoyi ko Lauyoyi da zasu tashi daga nan Arewa domin suje su tattauna dasu a kokarin su na tabbatar da an yiwa Yunusa Yellow Adalci.

Abun da ya fito fili dai a yanzu Shine; Gwamnatin Jihar Ta Bayelsa da hadin Bakin Al'ummar jihar sun tashi Haiqan domin bawa  ESE ORURU kariya da kokarin Wulaqanta Yunusa kawai dan sabo da Shi Dan Arewa ne kuma Musulmi. Duk da a zahirin gaskiya bashi da laifi.

Amma Mu anan Arewa da aka Tabbatar da zaluncin da Mutanen nan suka aikatawa Yaran mu da yawan su yakai kusan 73 mun kasa hada wata qwaqqwarar Tawaga wacce zata hada gwiwa da Gwamnatocin mu da Sarakunan hadi da Malamai da Lauyoyi tare da Sauran Kungiyoyin mu dake rajin kishin al'ummar Arewa, mu fuskanci wannan zaluncin da aka aikata mana.

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA SANARWA GAME DA BATUN YUNUSA YELLOW

Karanta Ma'anar Kalmar VAT a Mahangar Masana? Akan Su Waye Karin Harajin da Gwamnati Take yi Zai Shafa?

Karanta Illolin da Kabilar IGBO ta yiwa Sauran Kabilun Nigeria Wanda Hakan Zai Iya Haifar da Matsala anan Gaba

Abun Kaico abun Allah wadai sai nake ganin wasu daga cikin al'ummar mu na Arewa na Sukar wadanda suke magana akan Sace Yaran nan da sauya musu Addini... Wai mun cika surutu da neman Kambama abun da bai kai ya kawo ba.

Yanzu Dan Girman Allah wannan wane irin Rashin Kishi ne....?!

Allah Ya kyauta...

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user