Sunday 5 January 2020

Karanta Kayataccen Labarin Wani Makaho Mai Kaifin Basira

Tura Wannan Zuwa
A Bobi akwai wani makaho wanda a ke kira Bakin Makaho. Dalilin da ya sa mutane ke kiransa haka, domin wayon da Allah ya zuba masa ne. Kullum in ya yiwo bara ba ya batad da kudin a wofi, sai ya sami wani wuri, ya yi ta tarawa har dai kudi suka yi yawa.

Labarin Wani Makaho

Marubuci: Bukar Mada

+2348021218337

Daga littafin Magana Jari Ce 2 wallafar
Alhaji Abubakar Imam

Ranar Jumma'a, da ya dawo sai ya kwaso kudinsa duka ya kidaya, sai ya ga har sun kai fam uku. Da ya ga sun yi yawa haka sai ya ji tsoron kada ya bar su a bukkarsa, wani ya zo ya sace. Saboda haka ya yi ta neman inda zai kai su, ya ga in ya ba wani ajiyarsa kuwa lalle za a zalunce shi.

Yana cikin tunanin yadda zai yi da su, sai ya tuna ba inda ya fi ya ajiye su sai a masallaci, don ya sani lalle ba barawon da zai yi tsammani akwai wani abu a masallaci ban da buzaye da gorunan alwalla.

Ya ga in ya tafi da azahar lalle ya sami wadansu suna salla, saboda haka ya bari sai da rana ta yi tsaka, sa'an nan ya dauki kudinsa ya sa aljihu, ya tasam ma masallaci.

Da ya isa bai zame ba sai gindin mumbari, ya tsaya tsit ko ya ji motsin wani ciki, bai ji ba. Sai ya ce a ransa, "Lalle ba kowa. Da ma me zai kawo mutum masallaci da rana tsaka haka?" Ya shafa, ya kwakwale ramin gindin mumbarin nan, ya zuba kudinsa, ya tafi, yana fadi a ransa, "In na dawo mumbarin nan shi ne shaidata, ba a dai motsashi."

Ashe duk abin da makahon ya aikata wani madinki na nan yana wuridi, yana kallonsa. Wucewar makahon ke da wuya, sai madinkin ya katse wuridi, ya ce, "Bukatata ta biya. Allah ya karbi rokona." Ya tashi ya tone ramin, ya kwashe kudi, ya yi tafiyarsa.

Kashegari wani attajiri ya fid da zakka, Bakin Makaho ya sami kamar sule biyar sadaka. Sai ya nufi masallaci da karamin dansa na ja masa gora, ya bar shi waje, shi kuwa ya shige, ya lalubi mumbari ya tona gindinsa ba kudi ba dalilinsu. Ya saurara ko ya ji motsin wani, bai ji ba. Sai ya rike baki ya yi salati, ya ce, "Ba kome, in dai kudin nan halalina ne, ai ba su bata."

Ya fito ya tarad da dansa, ya ce masa, "Kai, da mu ke zuwa nan ba ka lura da wani na dubammu yana dariya ba?"

Yaro ya ce, "Ba wanda na gani yana maka dariya, sai Sanda, madinkin nan da ba ya ba mu sadaka im mun je bara kasuwa. Nan wajen kofar gidan Sarki muka wuto shi. Da na waiwaya har gwalo ma na ga yana yi maka. Ina tsammani abokin wasanka ne, shi ya sa ban ce maka kome ba, don ka hana ni tsalma baki cikin sha'anin manya"

Makaho ya ce wa yaro, "To, kai ni wajensa."

Yaro ya'ce, "To." Ya ja goran ubansa har rumfar Sanda Madinki a kasuwa, suka tarar ya dawo daga yawo.

Ko da ganinsu sai Sanda ya ce, "Bakin Makaho, me ya kawo ka nan ne yau, ba kuma ma ran Jumma'a ba? Ku dai makafin nan kun dami mutane da bara."

Makaho ya yi dariya ya ce, "Kai Sanda, in da don kai kadai mu ke zuwa kasuwan nan, lalle da mun mutu da yunwa. To, yau ba bara na zo ba da karayarka, magana ce gare ni da kai, fito ka ji."

Sanda ya fito, suka koma wuri daya, Bakin Makaho ya ce, "Tun tuni na ke son ba ka shawara, na dakata tukun a kare rigimar zakka mu gani. Yau kudin da na ke tarawa na bara yanzu na ga sun yi dan yawa, saboda haka na ke so in ka yarda in ba ka su ka rika juyawa, kana sayen 'yan kayayyaki kana sayarwa, ka ga da ni da kai duk sai mu amfana. Yanzu dinki ba ya ciwuwa da damana, da ma ka bar shi sai kaka. Yau ma can inda na ke ajiya na tafi in kai wadansu 'yam fam guda da na samu wajen zakkar da attajirai suka fid da jiya, na tarar wurin da na ajiye kudin akwai mutane, saboda haka na bari sai rana ta take tsaka, sa'ad da kafa ta dauke na tafi in kai wadannan. Gobe kuma in na je, abin da na samu daga wadanda Sarki zai fitar, zan komo ma'ajina in dauki wadancan in gama, in kawo maka. Kai na ga kana iya rikon amana, shi ya sa na ba ka. Amma don Allah kada ka ci amanata. Ka san fa kowa ya ci amanar wani, Allah ya ci tasa."

Da Sanda Madinki ya ji haka sai ya yi murna a ransa, ya ce, "Subuhana lillahi, ai tsakanina da kai babu cin amana. Kai ne watakila ba ka sani ba, ai na ji labari da tsohona da tsohonka sa'ad da suna yara ba abin da ke raba su. To, gobe da azahar ina nan ina jiranka."

Bakin Makaho ya ce, "To, Allah ya kai mu." Sanda ya raka shi, suka yi sallama. Yaro ya ja goran ubansa, suka nufi gida.

Da wucewarsu sai Sanda ya yi wa makaho gwalo daga baya, ya ce a ransa. "Bari in je yanzu im mai da kudin nan fam uku a masallaci, don idan an jima, da rana tsaka Bakin Makaho ya kai fam gudan da ya ke fadi, ya tarad da wadannan can. Idan ya kai wadannan, watau sun cika fam hudu ke nan, da magariba sai in lababa in kwashe su duka, in zo in sayi turame in yi ta dinki. Kafin kaka kuwa ai lalle in sayi keke, in shiga cikin 'yan'uwana ina kece raini."

Nan da nan sai ya dauki kudin nan ya kidaya, ya ga ashe ma jiya har ya sai wa matansa zannuwa na sule goma daga ciki. Saboda haka ya tafi ya samo rancen sule goma ya gama, suka tashi fam uku daidai, ya kai inda ya tono su a masallaci, ya binne. Ya ce, "Ashe dai ba shakka abin da mutane ke fadi gaskiya ne, dare, daya Allah ya kan yi Bature. Dubi wannan baiwa da Ubangiji ya yi mini yau, in sami fam hudu ba saye ba sayarwa. Ya kama hanya ya tafi.

Da rana ta yi tsaka, Bakin Makaho ya komo masallaci ya tona mumbari sai ga kudinsa fam uku cur. Ya yi godiya ga Allah da ya nufa wannan dabara tasa ta fita. Ya kwashe ya koma gida.

Magariba na yi, Sanda shi ya riga Liman zuwa masallaci. Da aka yi salla aka kare, sai ya kama wuridin karya don mutane su watse su bar shi, shi kuwa ya tone kudin.

Da ya ga duk an fita, sai ya tashi ya nufi gindin mumbari, ya tona ya tona, bai ga kome ba. Sai duk ransa ya baci, ba don batan sule hamsin din nan ba, amma don sule goman nan da ya ranto ya cika. Da zai fita ya ce, "Kai, me ma zai bata mini rai ga wannan? Da ma na dauke su, zunubin da zan kwasa na wannan bawan Allah ai Ubangiji kadai ya san iyaka." Ya wuce yana tunanin abin da zai yi ya biya mutane sule goma dinsu.

Da gari ya waye ya yi ta jiran Bakin Makaho har azahar ta wuce, bai gan shi ba. Sai ya tashi ya bi shi gida, ya ce, "Na zo bisa ga maganar da muka kulla jiya ne, ka san ni ba na son in na ce i, in komo in ce a'a."

Bakin Makaho ya ce, "Ai ni ma yadda ka ke din nan haka na ke. Kudin na zamani ke da ban al'ajibi, in ka duba inda ka ajiye su, wata sa'a sai ka tarad da su sun tafi yawo. Da yanzu fa zan kai maka, sai na tarad da duk sun fita shan iska, ba ko daya,sai fa in sun dawo ka gan ni da su."

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA KAYATACCEN LABARIN ZAKI DA MUTUM

KARANTA KAYATACCEN LABARIN WATA MATA DA KWARTAYE BIYU

KARANTA KAYATACCIYAR HIKAYAR SHEHU JAHA "KARKA GASKATA SHI"

Da ya ji Bakin Makaho ya tasar wa yi masa ba'a sai ya yi fushi, ya haura takalmansa ya tafi yana cewa, "Mutanen duniya dai yanzu Turawa sun bata su da wayo, ko ina ka fito musu suna make suna kallonka."

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode





TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user