Sunday 25 August 2019

KARANTA LABARUN DA BISHIYOYIN KUKA KE SANAR MANA KASHI NA DAYA

Tura Wannan Zuwa
Kashi na ɗaya.

Kasancewar akwai ilimi acikin kowanne abu, ya kamaci muyi duba ga bishiyoyin kuka don fahimtar iliman da suke sanar mana anan kasar Hausa.

Bishiyar Kuka

MarubuciSADIQ TUKUR GWARZO

08060869978

Domin kuwa kamar yadda masana kimiyyar duwatsu ke cewa akwai tarihi a kowanne dutse, haka ma akwai labari ga mafi yawan rukunonin bishiyoyin kuka anan kasar hausa.

To amma, wanne labari bishiyoyin suke sanar mana?

1. Ana Gane wanzuwar birnin Hausawa daga kukoki.

Hakika, kasancewar tun da jimawa, babu shahararrun gine-gine masu kafuwa cikin kasa a kasar hausa, muna iya cewa babu wani ma'auni dake tabbatar mana da wanzuwar tsohuwar rayuwa a kasar hausa sama da rukunin kukoki.

 Ko tantama babu, duk inda aka samu kukoki sun jeru reras, ko sunyi da ira, ko wani abu mai kama da haka, to akwai labarin cewa gari ya taɓa wanzuwa a wannan wuri.

2. Ana sanin Tsufan gari gami da tumbatsar sa daga kukoki.

Akan haka, munyi duba ga tarihin wasu tsoffin garuruwa anan kasar hausa masu cike da bishiyoyin kukoki, kuma ga ɗan abinda muka samo:-

  I. Sabon Birni

Daga tsoffin biranen dake kasar hausa, akwai wani Sabon Birni a kasar Getso mai cike da kukoki.

Masana tarihin garin, sun bayyana cewar wasu fulani ne suka kafa shi, waɗanda suka taso daga arewa sama da shekaru ɗari biyar da suka gabata.

Kasancewar garin fulani irin wannan mai cike da kukoki, yasa akwai zakuwar sanin dalilan fitowar waɗannan kukoki a wannan gari.

Ada, hasashen mu yafi tafiya akan cewar mu'amala da iskokai ke tilastawa hausawan dauri rayuwa da kukoki a muhallansu, amma samunsu a mtsugunin da tun asali fulani suka kafa, sai yazo da wani sabon abu.

A bisa jin dalilin fitowar kukokin, Mazauna garin sunce acan baya babu kukoki a wannan wuri kafin ya zama gari, amma kasancewar fulanin da suka zauna a wurin suna amfani da kwalba wajen kaɗa nono ('ya'yan kuka), to idan an zubar dasu a wuri, sai kaga wata bishiyar ta sake tsirowa. Har ma sai da takai ga cewa a kowanne gida, akwai kuka acikinsa. Wani gidan ma har sama da ɗaya akan samu.

Wanzuwar tsoffin kukoki da kuma yawaitarsu a wannan tsohon gari ke nuna cewar ada-can baya, garin ya cika da gidajen mutane.

Sai dai, duk da cewar fulanin garin basu taɓa gina ganuwa ba kasancewar su matafiya ba mazauna ba, idan labarin yaki yazo sukan shige birnin getso ne wanda wani bamaguje mai suna Babbaka Toro ya kafa bisa neman mafaka.

Daga al'adun mutanen garin kuwa, sharo ne yafi shahara, wanda suka ce ada can a duk shekara mutane mata da maza daga garuruwa makwabta na taruwa a kofar gari, kusa da wasu duwatsu ayi kwana biyu ana sharo, ana kiɗan kotso da gangi harma da kiɗan Balaye wadda ake mata  rawar juya-juya.

Daga wannan garin ne aka samu wani maharbi mai suna Ganjigo ya tashi har yaje ya gina garin walawa a kasar karaye, da kuma wani gari mai suna Kafin Allah Gaba a kasar zazzau.

Don haka, mazauna garin sun tafi akan cewar babban labarin da kukokin garin ke bayarwa shine jimawar al'umma a cikin sa, domin kuwa saida mutane suka soma zama sannan kukokin garin suka fito.

Har ma wani dattijo yace akwai wata kuka data fito a gidansu suna yara, sama da shekaru hamsin kenan bata girma ba har zuwa yau, don haka yace tabbas akwai shekaru ɗaruruwa ga waɗannan tsofaffin kukoki na garinsu.

   II. Zangon Dan-Nafada

Shi kuma wannan gari, wani mai suna Madugu ne aka ce ya sare shi shekaru ɗaruruwa da suka shuɗe. Rukunin kukokin da suka zagaye garin kaɗai ya isa ya bada shaidar cewa hausawa sun jima suna rayuwa a wannan gari.

Akace Wai yayin da Madugu yazo wucewa, sai ya yada zango a wannan wuri, don haka sai ake cewa da wurin zangon madugu. Daga baya sunan garin ya koma Zangon ɗan Nafada.

 A cewar wani mazaunin garin, Babbaka Toro daya sari garin getso, anan ya soma zama tare da Madugu da wasu jama'a kowanne cikin ɗan botonsa, daga bisani ya tashi yaje ya sari Getso.

Da yake shima wannan gari cike yake da kukoki, mazauna garin sun tabbatar da cewa sai da mutane suka soma zama sannan kukokin suka fito a dalilin zubar da kwallayensu da akeyi ko ina idan an shanye.

Don haka, tsufan garin na iya zamowa wasu shekaru sama da shekarun kukokin wannan gari kenan..

A bisa tsoffin hausawa da fulani da muka tambaya, kusan ɗaukacin su sun tafi akan cewa duk kukar daka gani ba'a san sanda aka shukata ba. Dukkan su sun gamsu cewar manyan kukoki masu alamar shekaru, tasowa sukayi suka gansu.

Haka nan, ana iya lura cewar a gonaki da dazuzzuka inda babu mutane dake rayuwa a wurin, ba kasafai bishiyar kuka ke fitowa ba. Amma kuma mafi yawan unguwannin hausa na tsoffin garuruwa na ɗauke da bishiyoyin kokoki. A wani sa'in ma, akan samu bishiyar kuka a kowanne gida, ko kuma a bayan kowanne gida.

Watakila, hakan na nuna cewar sai da mutane suka fara zama a wannan wuri sannan kukokin suka fito.

Idan kuwa hakan ta tabbata, to zamu iya sanin shekarun kukoki a kasar hausa ta hanyar binciken zamani, sannan da watakila zamu iya sanin jimawar lokacin da hausawa suka fara zama a wannan wuri, tayadda daga bisani zamu gane gari mafi tsufa a kasar hausa.

DUBA WADANNAN:

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN YAKIN DUNIYA NA DAYA

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN SHEIKH ABUBAKAR MAHMUD GUMI

Karanta Jerin Jadawalin Kabilun Nijeriya Guda 373 Da Jahohin Da Ake Samun su

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN YAKIN BASASAR NIGERIA

Idan kuma ta tabbata cewar yawan bishiyoyin kuka ke nuni da yawan mutanen da suka rayu a gari, da shima zai zamo mana ma'auni mafi sauki don gane tsoffin garuruwan da sukafi tumbatsa da mutane shekaru aru-aru da suka wuce..

Zamu Ci gaba Insha Allah.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user