Monday 16 September 2019

Karanta Takaitaccen Tarihin Sarkin Musulmi Ibrahim Dasuki

Tura Wannan Zuwa
An haife shi ne a garin Dogon Daji na jihar Sakkwato a shekarar 1923.

Sarkin Musulmi

Da ne ga Haliru dan Barau wanda ya rike sarautar Ubankasar Dogon Daji wato Sarkin Yamma Dogondaji.

Ya yi karatun addinin Musulunci da na elementare a garin na Dogondaji kafin daga bisa ni ya tafi kwallejin Middle School ta Sakkwato da kuma ta Barewa da ke Zariya inda ya kammala karatunsa na Sakandare a 1943.

Mai alfarma Alhaji Ibrahim Dasuki shi ne Sarkin Musulmi na 18 a jerin sarakunan Daular Usmaniyya.

Kafin zamowarsa sarkin musulmi a shekara ta 1988, ya rike sarautar Baraden Sakkwato matsayin da ya yi amfani da shi wajen bayar da gudunmuwa wurin kafa kungiyar Jama'atul Nasril Islam.

Shi ne dai Sarkin Musulmi na farko daga Zuri'ar Buhari dan Sheikh Usman Bin Fodiyo, kuma kawo yanzu shi kadai ya yi sarautar ta Sarkin Musulmi daga wannan gidan.

Tsakanin shekarun 1965 zuwa 1988 da aka nada shi sarauta, Alhaji Ibrahim Dasuki ya fi mayar da karfi ne ga harkokin kasuwanci.

Marigayin ya zama Sarkin Musulmi ne a watan Disambar shekara ta 1988 bayan rasuwar Sarkin Musulmi na 17 Alhaji Abubakar Sadik na III

Sanar da shi a zaman magajin Sarki Abubakar na III a maimakon dansa Alhaji Muhammadu Maccido Abubakar III ya jawo wata zanga-zanga ta tsawon kwanaki biyar a birnin na Sakkwato wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla goma.

Masu adawa da nadinsa a lokacin na ganin Muhammad Maccido mai ra'ayin mazan jiya a zaman wanda ya fi cancantar da wannan kujerar bisa shi Alhaji Ibrahim Dasuki mai ra'ayin tafiya da zamani.

Ya kwashe shekaru takwas kan mulki kafin gwamnatin soji ta Marigayi Janar Sani Abacha ta sauke shi a shekara ta 1996.

An zarge shi da kin bin umarnin gwamnati da kuma yin tafiye-tafiye zuwa kasashen waje ba tare da neman izni ba.

Bayan sako shi daga wurin da aka tsare shi a jihar Taraba na tsawon shekaru, ya tare a gidansa da ke birnin Kaduna inda ya ci gaba da tafiyar da harkokin rayuwarsa har zuwa lokacin ya kamu da cutar ajali.

Marigayin ya nuna rashin jin dadinsa karara, lokacin da jami'an tsaro suka kai sumame gidansa na Sokkwato a lokacin da suke binciken dansa Sambo Dasuki.

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN IMAM MALIK BN ANAS

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN SHEIKH ABUBAKAR MAHMUD GUMI

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN DR. ZAKIR NAIK

Shi dai Sambo, wanda tsohon mai baiwa Shugaba Goodluck Jonathan shawara ne kan harkokin tsaro, yana fuskantar shari'a kan zargin cin hanci da rashawa.

Batun da ya musanta yana mai cewa siyasa ce kawai.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








Source: BBC HAUSA

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user