Tuesday 17 December 2019

Karanta Babban Sako Zuwa ga 'Yan Luwadi da Wadanda Suke yin Sha'awar Harkar Luwadi - Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Tura Wannan Zuwa
Liwaɗi shine namiji yana neman ɗan uwansa namiji, kamar yadda ake neman mace.

Taɓewa tun a nan Duniya Idan ba'a tuba ba...

Marubuci: Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Sheɗan ya fitowa da mutane wannan halaka,  da buƙatu da yawa,  domin tsafi, domin neman kudi,  domin neman daukaka, domin neman mulki, domin neman kwarjini da makamantansu, kuma duk karyace, babu wani abu da ake samu sai kaskanci da koma baya a duniya da lahira.

Babbar musifa babban bala'i, tashin hankali,tir, abin kaico, abin kunya abin takaici, namiji yana neman ɗan uwansa namiji, abinda ba a samu a cikin  dabbobi, amma a sami wasu matasa, wai har sun kafa kungiya ta masu neman maza, wannan kawai ya isa musifa da bala'i
da halaka.

A sami wannan laifi yana yaɗuwa a cikin matasa, mu duba yadda Allah Ta'ala ya yiwa wannan kasa, ta Annabi Ludu (A.S) , da suke liwaɗi aka ruguza su, sama ta koma ƙasa, ƙasa ta koma sama, amma ace wannan abin ya zama, a cikin al'ummar Annabi Muhammad (S.A.W) , Allah ya shiryar da masu yi da waɗanda ake yiwa.

Luwaɗi yana jawowa mai yinsa bala'i 31 kamar haka:

1. Karancin muwafaka

2. Gurɓatar ra'ayi

3. Gurɓatar zuciya

4. Toshewar basira

5. Jefa ƙiyayya da ƙyamar mai yi a zuciyar bayin Allah

6. Yana haifar da ɗimuwa

7. Rashin amsa addu'a

8. Shafe albarka

9. Taɓewa

10. Jarabta da ƙasƙanci

11. Rinjayen maƙiya

12. Kuncin ƙirji

13. Bacin zuriya

14. Mugayen abokai

15. Zama cikin tsoro da firgici

16. Kuncin rayuwa

17. Raunin jiki

18. Mugun mafarki

19. Cututtuka marasa magani

20. Kin jin dadin sauraren Alkur'ani mai girma

21. Gafala ga ambaton Allah

22. Mummunar cikawa

22. Gushewar ni'imah

23. Taɓuwar hankali

24. Zubewar mutunci

25. Ɗabi'ar daud

26. Gushewar kunya

27. Gushewar kishi

28. Kaskanci

29. Rinjayar sheɗan

30. Mala'iku zasu gujeshi

31. Hukuncin kisa ya hau kansa idan an kama shi da shedu ko kuma yayi iitirafi a gaban kotu.

Magani da Yardar Allah:

1. Tuba da Nadama

2. Hakuri daga sabon Allah

3. Canja abokai

4. Addu'a

5. Yawan Ambaton Allah

6. Yawan karatun Alkur'ani mai girma

7. Karanta tarihin magabata

8. Tunanin Wuta da Aljannah

9. Tsoran Mummmunar cikawa

10. Yin aure da wadatuwa da iyali ta inda Allah ya halatta.

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA MANYAN SIFFOFIN 'YAN LUWADI DA RAYUWAR SU CIKIN SIRRI KASHI NA FARKO (1)

ME CE CE KUNYA KUMA TA YA YA AKE GANE MUTUM YANA DA KUNYA ??

KARANTA CUTUTTUKA GUDA 30 DA LUWADI YAKE HAIFARWA GA MAI YINSA

Allah ya shiryi waɗanda suka faɗa wannan bala'i ya tsare waɗanda basu faɗa ba Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode





TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user