Showing posts sorted by relevance for query ADAMU NAGUDU. Sort by date Show all posts
Showing posts sorted by relevance for query ADAMU NAGUDU. Sort by date Show all posts

Saturday, 25 April 2020

Sauke Sabuwar Wakar Adamu Nagudu Ft Ikram Kano - Covid-19

Sauke Sabuwar Wakar Adamu Nagudu Ft Ikram Kano - Covid-19

Kamar Yadda Shafin
MuryarHausa24.com.ng ya shahara wajen kawo muku sababbin Waƙoƙin Soyayya har ma dana Siyasa Yau ma gamu tafe da waƙar Faɗakarwa.


Adamu Nagudu Ft Ikram Kano - Covid-19

Fitaccen mawaƙi Adamu Nagudu na masana'antar Kannywood da fasihin mawaƙi Ikram Kano sun fitar da zazzafar waƙar Covid-19 wacce tafi kowacce zafi.

Taken waƙar "COVID-19 KA TSARE MU YA ALLAH RABBA, AL'UMMAR BORNO BIRNI DA ƘAUYUKA YARO BABBA MU DAU WANNAN SAKO RIGA-KAFI MAKARIN ANNOBA".

Wannan wakar cike take da saƙonnin faɗakarwa game da cutar Sarƙewar Numfashi (Covid-19). Sadaukarwa ce ga al'ummar jihar Borno a arewacin ƙasar Nijeriya (Nigeria) dama Duniya baki ɗaya.

Wato tsayawa bayyana abinda wannan waƙar ta ƙunsa kamar ɓata lokaci ne, abin sai wanda ya saurara.

Kardai mu cika ku da surutu ku hanzarta sauke wannan waƙar yanzu domin sauraro.

SAUKE WAKAR ANAN

Kada ku sake a baku Labari.

Domin samun sababbin waƙoƙin siyasa, waƙoƙin Soyayya, waƙoƙin bege, waƙoƙin gargajiya da sauran su akan lokaci ku ci gaba da kasancewa da mu a www.MuryarHausa24.com.ng farin cikin ku shine farin cikin mu.

MURYAR HAUSA24 Muna fatan za ayi kallo gami da sauraro lafiya cikin Nishaɗi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Saturday, 12 May 2018

Takaitaccen Tarihin Maryam Babban Yaro: Abubuwan da Yakamata Ku Sani dangane da Rayuwar Jaruma Maryam Babban Yaro

Takaitaccen Tarihin Maryam Babban Yaro: Abubuwan da Yakamata Ku Sani dangane da Rayuwar Jaruma Maryam Babban Yaro

Maryam Gidado tana daya daga cikin manyan jarumai mata a masana’antar fina-finan Hausa. Aminiya ta tattauna da ita kan harkar, inda jarumar ta tabo batutuwan da suka shafi harkar fim da kuma rayuwarta.

Ga yadda hirar ta kasance:

A gabatarwa, wace ce Maryam Gidado?

Kamar yadda aka sani, sunana Maryam Jibril Gidado, wacce aka fi sani da ‘Maryam Babban Yaro.’
Na samu wannan suna ne tun daga lokacin da muka yi fim da Adam A. Zango mai suna ‘Babban Yaro.’ An haife ni a watan Disamba a 1988 a garin Jos. Na fara makaranta a Hassan Memorial, sai aka mayar da ni firamare ta LGA Gangare, sannan na yi makarantar Arabiyya ta Sakandire a Bauchi Road, duka a Jos.
Sannan na je na yi Diploma a bangaren kwamfuta a wata makaranta daban. Daga nan na koma Bauchi na nemi in yi HND, amma ban samu ba sai na yi diploma a bangaren kididdiga. Sai kuma na ci gaba har na yi HND a nan, sai na dawo Jos na yi digirina a Jami’ar Jos.

Ko Maryam ta taba yin aure?

To yanzu idan na ce ma ban taba yin aure ba sai a yi mini dariya a matsayina na Bafulatana, kasancewar kowa dai ya san ka’idar Fulanin daji yi wa ’ya’yansu aure da wuri. Bayan na gama jarrabawar WAEC da NECO aka yi mini aure.
Ina shekara sha hudu na haifi ’yata ta farko, bayan shekara daya da auren ke nan. Don haka shekara goma sha hudu na ba ’yata ta fari. Yanzu ka ga ta shiga shekara sha daya ke nan.

To yaya aka yi kika samu kanki a harkar fim?

Ni dai gaskiya da ina kallon fim ne kawai, amma ina tunanin shirme ne kawai, domin idan na ga ’yan fim har zaginsu nake yi don ban taba tunanin zan yi fim ba.
Daga baya sai na ga yadda abin yake fadakarwa. Na ga wasu ma sun Musulunta ta hanyar fim. Sai na ga abin wa’azi ne.

To, a baya kin fada mana yadda aka yi miki aure har kika haihu. Sai dai ba ki fada mana ko kun rabu da mijin ko mutuwa ya yi ko kuma da aurenki kike yin fim ba?

To, a gaskiya ba zan iya fada ba. Saboda a duniya babu abin da ya kai sirri dadi. Idan ka rufa wa wani asiri Allah Zai rufa naka. Kuma tsakanin mata da miji sai Allah. Don haka wannan mutane su yi hakuri.

Shin wannan dan naki na biyu babansu daya da ’yarki ta farko?

Ba daya ba ne. Bayan mun rabu da mijina na yi wani sabon aure. Lokacin da na auri mahaifin dana ma har na fara harkar fim. Ina da cikinsa ya gudu ya bar ni har na haife shi yanzu shekarun dana na biyu bakwai ke nan.

Abin nufi a nan shi ne, kun rabu da shi ne ko rasuwa ya yi?

To, in dai wannan ne ba rasuwa ya yi ba, yana nan da ransa, sannan ina da cikin dana na biyu wata daya ya tafi ya bar ni, har zuwa yanzu mahaifinsa bai zo wajen da yake ba. Sai dai ya turo a dauki hotonsa, kuma zai iya kira ta waya su yi magana, amma dai yana nan a Kaduna kawai dai tafiyar da ya yi ya bar ni don wani dalili ne na daban.

To daga nan sai me ya biyo baya?

Kai dai a bar maganar haka, don sirri yana da dadi.

Ki fada mana yadda aka yi kika samu kanki a harkar fim da kuma shekarar da kika fara?

A gaskiya na manta shekarar da na shigo, amma dai na fara ne da albam din Mahmud Nagudu mai wakar ‘Garin So Nisa’ amma fim din da aka fara yi mini shi ne wani fim mai suna ‘Ragowar Yaki,’ lokacin da muke yi a Jos da ni da Ali Nuhu.

Shi ne fim dina na farko da na fara yi a duniya, kuma da ma tun da na fara fim ban fara da mai tallafa wa jaruma ba, da jaruma na fara. Kodayake da farko mutane sun dauka albam nake yi ba fim ba, saboda shi ne na fara. Sai daga baya na zo na shiga fim din su Alma, inda na yi ‘Ragaya’ da ‘bingyal da ‘Mukaddari’ da sauransu.

Ko za ki iya bayyana yawan fina-finan da kika yi?

Gaskiya ba zan iya fadar adadinsu ba. Don ka ga a wata zan iya yin fim biyu ko uku, to yaya zan iya sanin fim din da na yi a tsawon lokacin da na yi a harkar fim? Sai dai zan iya fadar wasu kadan daga cikinsu, musamman wadanda ba su dade ba kamar ‘Babban Yaro’ da ‘Wata Hudu’ da ‘Munafikin Mata’ da ‘Al’ajabi’ da ‘Zawarawa’ da ‘Fulani’ da ‘Sultan’ da ‘Basaja.’ Ina ji da su a cikin fina-finaina.
Akwai lokacin da kika yi wani tashe sai kuma aka daina ganin ki a harkar fim.

Hakan ya sa ake cewa ko kin yi aure ne, ko kuma harkar kika bari…?

To gaskiya ba aure na yi ba, kuma ba barin harkar na yi ba, ina yi kadan-kadan ne, sai dai mutane ba za su gane ba, saboda ba sa gani na sosai, amma dai kafin na fara sai da na fada wa mahaifina, sai ya ce shi ma ga dokar da zai kafa mini, ya ce makaranta yake so in yi, kuma ya matsa sai da na yi, to da na ga na samu wannan sunan na daukaka, sai na koma makaranta. Hakan ya sa ake ganin kamar na bari ne, amma dai ina yin fim lokaci zuwa lokaci. Amma dai yanzu na gama na dawo.

A baya an fi ganin ki tare da Adam A. Zango, amma yanzu ba a ganin ku tare, me ya jawo hakan?

To ai da ma ba a kamfanin Adamu nake ba, kuma kamfanin Adamu fina-finan da suka yi mini ba su da yawa. Sai dai su ne suka yi mini fim din da ya fara daga ni. Don bayan albam din Mahmud Nagudu babu wani fim da ya daga ni sai na su Adamu. A gane furodusa ne yake hada ’yan wasa. Don haka idan suka ga dama su hada ni da Ali, in suka ga dama su hada ni da Adamu, ko Sani Danja da sauransu.

Yanzu a matsayinki na babbar jaruma, burinki ya cika a harkar fim?

Gaskiya burina ya cika sai godiya ga Allah. Yanzu burina daya ne kawai Allah Ya ba ni miji nagari.

Ku ’yan fim kullum ku ne fadar miji nagari kuke nema, amma ana yi muku kallon masu ruwan ido, ko me za ki ce kan hakan?

To, ai mu ba ruwan ido muke yi ba, muna tunanin maza suna ganin mu a fim ne, suna son su aure mu don wata manufa da suke da ita. Shi ya sa muke tsoron auren, ba wai muna tunanin wane mai kudi ba ne, ko marar kudi ba. Don idan ka auri mai kudi ma zai zaci don kudinsa ka aure shi. Gara ka auri talaka idan kudin ya zo kuna tare da shi. To yanzu abin ne sai ya zama muna tsoron mazan, su ma suna tsoron mu.

Ba kya ganin ana cewa idan kun yi auren ma ba kwa zama?

To ai wannan maganar da na yi ita ce ta ba da amsar wannan tambayarka. Nan za a gane Allah ne Ya san dalilin rabuwa tsakanin mata da miji, babu mamaki wancan dalilin zai sa a zo a yi auren wani bai yi tunanin wannan ba sai haka ta kasance.

Bayan harkar fim, ko akwai wata harka ta kasuwanci da kike yi?

E, ina yin kasuwanci. Don yanzu ina da wajen gyaran gashi a gidanmu. Sannan a makarantarmu ina yin aiki na wucin gadi, kuma ina saro kayan mata ina sayarwa.

Akwai wani lokaci da kika shirya na barin harkar fim?

Gaskiya ban shirya ba, sai lokacin da Allah Ya kawo mini miji to lokacin zan bar harkar fim.

Me kike alfahari da shi a game da harkar fim?

To abin da nake alfahari da shi na san ko ban yi komai ba akwai wadanda suka karu da ni a kan wani fim da na yi na gyara tarbiyya, sannan na san mutane masu yawa. Hakan abin alfahari ne, wanda ba kowa Allah Yake yi wa haka ba.
Sannan na samu abubuwa wadanda suke hakkokina ne nake ci ba na wasu ba. Sannan da fim na je Makka, na yi gida, na mallaki kadarori, na yi karatu, don haka dole na yi alfahari da harkar fim.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki 

Mungode

Source: Aminiya

Saturday, 8 August 2020

Sauke Sabuwar Wakar Ado Gwanja Ft Hussaini Danko - Kara Yunkuri Baba

Sauke Sabuwar Wakar Ado Gwanja Ft Hussaini Danko - Kara Yunkuri Baba

Kamar Yadda Shafin MuryarHausa24.com.ng ya shahara wajen kawo muku sababbin Waƙoƙin Soyayya har ma dana Siyasa Yau ma gamu tafe da waƙar Siyasa.


Kara Yunkuri Baba

Gamayyar mawaƙan fina-finan Hausa ne su fito su rera wannan waƙar domin ƙara tunatar da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari halin da ƙasar Nijeriya take ciki a halin yanzu, kana kuma a ƙara tunatar da al'ummar Nijeriya musamman yankin arewacin ƙasar irin gudunmawar da shugaban ƙasa da gwamnonin arewa su bayar a fannin tsaro da kuma haɓaka tattalin arzikin ƙasar Nijeriya.

Taken waƙar "KAYI ƘOƘARI BABA A ƘARA YUNKURI, AKAN GYARAN ƘASA MUSAMMAN SHA'ANIN TSARO ƘYALE 'YANSAN A ƁATA BAZASU TAYAKA BA".

Idan baku manta ba, tun a shekarar dubu biyu da sha biyar (2015), mawaƙan fina-finan Hausa suke tare da Baba Buhari, idan muyi waiwaye a shekarun baya sun yi waƙoƙi da dama cikin waɗanda suka fi shahara sune: Lema Ta Yage, Sakamakon Chanji, Aikin Gama Ya Gama da sauran su.

Kalli Bidiyon Kai Tsaye...

Kaɗan daga cikin mawaƙan da suka bayar da muryoyinsu domin isar da wannan saƙon ga dubban al'ummar Hausawa dake cikin ƙasar Nijeriya dama Duniya baki ɗaya:

Adamu Nagudu
Auta Waziri
Audu Boda
Baban Chinedu
El-Mu'az Birniwa
Dan Musa Gombe
Ibrahim Ibrahim
Isyaku Forest
Jamilu Jadda Garko
Sani Sabo Kwarko

Waƙar ta hau kan  tsari bisa tsarin mawaƙan waɗanda su baje kolin basira da hikimar su a cikin waƙar.

Wannan dai sabuwar waƙa ce da Mawaƙan Sakamakon Chanji su rera cikin wannan sabuwar shekarar da muke ciki (2020), waƙar dai tazo da wani sabon salo mai tafiyar da zukatan Masoya Baba Buhari cikin farin ciki da walwala.

Wato tsayawa bayyana abinda wannan sabuwar waƙar ta ƙunsa kamar ɓata lokaci ne, abin sai wanda ya saurara.

Kardai mu cika ku da surutu ku hanzarta sauke wannan waƙar yanzu domin sauraro.

SAUKE WAKAR ANAN

KADA KU SAKE A BAKU LABARI

Domin samun sababbin wakokin siyasa, wakokin Soyayya, wakokin bege, wakokin gargajiya da sauran su akan lokaci ku ci gaba da kasancewa da mu a www.MuryarHausa24.com.ng farin cikin ku shine farin cikin mu.

MURYAR HAUSA24 Muna fatan za ayi sauraro lafiya cikin Nishaɗi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Saturday, 26 September 2020

Sauke Sabuwar Wakar Hamisu Breaker Ft Umar M Sharif - Arewa Mu Farka

Sauke Sabuwar Wakar Hamisu Breaker Ft Umar M Sharif - Arewa Mu Farka

Kamar Yadda Shafin MuryarHausa24.com.ng ya shahara wajen kawo muku sababbin Waƙoƙin Soyayya har ma dana Siyasa Yau ma gamu tafe da waƙar Siyasa.


Arewa Mu Farka

Gamayyar mawaƙan fina-finan Hausa ne su fito su rera wannan waƙar domin ƙara tunatar da al'umma halin da ƙasar Nijeriya take ciki a halin yanzu, kana kuma a ƙara tunatar da al'ummar Nijeriya musamman yankin arewacin hanyoyin da za abi domin daƙile yaɗuwar fyaɗe da sauran ayyukan ta'addanci wanda su addabi yankunan ƙasar baki ɗaya musamman arewacin Najeriya.

Taken waƙar "INA ZAMU JE! INA ZAMU KWANA! MU TASHI MU FARKA 'YAN AREWA".

Kalli Bidiyon Kai Tsaye...

Kaɗan daga cikin mawaƙan da suka bayar da muryoyinsu domin isar da wannan saƙon ga dubban al'ummar Hausawa dake cikin ƙasar Nijeriya dama Duniya baki ɗaya:

Ali Jita
Adam A. Zango
Adamu Nagudu
Ado Gwanja
El-Mu'az Birniwa
Fati Niger
Fresh Emir
Dan Musa Gombe
Hamisu Breaker
Hussaini Danko
Ibrahim Ibrahim
Nazifi Asnanic
Naziru M. Ahmad
Sadik Zazzabi
Umar M. Sharif

Waƙar ta hau kan  tsari bisa tsarin mawaƙan waɗanda su baje kolin basira da hikimar su a cikin waƙar.

Mawaƙan sun yi kira sosai ga shugabanni, kana sun taɓa fanni daban-daban wanda 'yan arewa suke ciki a gwamnatin ƙasar amma babu abinda muƙaman nasu suke tsinanawa al'ummar ƙasar musamman matasa waɗanda sune mafiya yawan al'ummar ƙasar Nijeriya.

Wato tsayawa bayyana abinda wannan sabuwar waƙar ta ƙunsa kamar ɓata lokaci ne, abin sai wanda ya saurara.

Kardai mu cika ku da surutu ku hanzarta sauke wannan waƙar yanzu domin sauraro.

SAUKE WAKAR ANAN

KADA KU SAKE A BAKU LABARI

Domin samun sababbin wakokin siyasa, wakokin Soyayya, wakokin bege, wakokin gargajiya da sauran su akan lokaci ku ci gaba da kasancewa da mu a www.MuryarHausa24.com.ng farin cikin ku shine farin cikin mu.

MURYAR HAUSA24 Muna fatan za ayi sauraro lafiya cikin Nishaɗi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Thursday, 28 May 2020

Sauke Sabuwar Wakar Nazifi Asnanic Ft Ali Jita - Coronavirus Gaskiya Ce

Sauke Sabuwar Wakar Nazifi Asnanic Ft Ali Jita - Coronavirus Gaskiya Ce

Kamar Yadda Shafin
MuryarHausa24.com.ng ya shahara wajen kawo muku sababbin Waƙoƙin Soyayya har ma dana Siyasa Yau ma gamu tafe da waƙar Faɗakarwa.

Coronavirus Gaskiya Ce

A yau muna tafe da waƙar faɗakarwa game da cutar Sarƙewar Numfashi (Covid-19) ta gamayyar mawaƙan masana'antar shirya fina-finan Hausa (Kannywood).

Kaɗan daga cikin mawaƙan da suka bayar da muryoyin su domin isar da wannan saƙon ga dubban mutane:

Adamu Nagudu
Ali Jita
Nazifi Asnanic

An rera wannan waƙar ne domin tunatar da al'umma cewa "Covid-19 Gaskiya Ce". Abinda ya rage mana mu bi matakan kare kai.

Wato tsayawa bayyana abinda wannan sabuwar waƙar ta ƙunsa kamar ɓata lokaci ne, abin sai wanda ya saurara.

Kardai mu cika ku da surutu ku hanzarta sauke wannan waƙar yanzu domin sauraro.

SAUKE WAKAR ANAN

MURYAR HAUSA24 Muna fatan za'ayi sauraro lafiya cikin Nishaɗi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Tushe/Asali: www.muryarhausa24.com.ng

Friday, 16 April 2021

Sauke Sabuwar Wakar Nazifi Asnanic Ft Hussaini Danko - Sabunta Katin Jam'iyya

Sauke Sabuwar Wakar Nazifi Asnanic Ft Hussaini Danko - Sabunta Katin Jam'iyya

 Kamar Yadda Shafin MuryarHausa24.com.ng ya shahara wajen kawo muku sababbin Waƙoƙin Soyayya har ma dana Siyasa Yau ma gamu tafe da waƙar Siyasa.


MU SABUNTA KATIN JAM'IYYA


Gamayyar mawaƙan fina-finan Hausa ne su fito, su rera wannan waƙar domin ƙara tunatar da al'ummar Nijeriya domin su hanzarta su sabunta katin su na jam'iyyar APC.

Taken waƙar "MU SABUNTA KATIN JAM'IYYA....".

Idan baku manta ba, tun a shekarar dubu biyu da sha biyar (2015), mawaƙan fina-finan Hausa suke tare da Baba Buhari. Idan mu yi waiwaye a shekarun baya sun yi waƙoƙi da dama cikin waɗanda suka fi shahara sune: Lema Ta Yage, Sakamakon Chanji, Aikin Gama Ya Gama da sauran su.

Kaɗan daga cikin mawaƙan da suka bayar da muryoyinsu domin isar da wannan saƙon ga dubban al'ummar Hausawa dake cikin ƙasar Nijeriya dama Duniya baki ɗaya:

Adamu Nagudu
Abubakar Sani (Ɗan Hausa)
Ahmad Shanawa
Alfazazi
Ado Gwanja
Abdul Smart
Auta Waziri
Dan Musa Gombe
El-Mu'az Birniwa
Hussaini Danko
Ibrahim Ibrahim
Ikram Kano
Musa Isah Gwanja
Nazifi Asnanic

Da sauransu

Waƙar ta hau kan  tsari bisa tsarin mawaƙan waɗanda suka baje kolin basira da hikimar su a cikin waƙar.

Wannan dai sabuwar waƙa ce da Mawaƙan Sakamakon Chanji su rera cikin wannan sabuwar shekarar da muke ciki (2021), waƙar dai tazo da wani sabon salo mai tafiyar da zukatan jam'iyyar APC cikin farin ciki da walwala.

Wato tsayawa bayyana abin da wannan sabuwar waƙar ta ƙunsa kamar ɓata lokaci ne, abin dai sai wanda ya saurara.

Kardai mu cika ku da surutu ku hanzarta sauke wannan waƙar yanzu domin sauraro.

SAUKE WAKAR ANAN

KADA KU SAKE A BAKU LABARI

Domin samun sababbin wakokin siyasa, wakokin Soyayya, wakokin bege, wakokin gargajiya da sauran su akan lokaci ku ci gaba da kasancewa da mu a www.MuryarHausa24.com.ng farin cikin ku shine farin cikin mu.

MURYAR HAUSA24 Muna fatan za ayi sauraro lafiya cikin Nishaɗi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Monday, 23 April 2018

Karanta Kaji: Kuskure 10 da akai acikin Film din KALAN DANGI tare da Sharhin Fim din

Karanta Kaji: Kuskure 10 da akai acikin Film din KALAN DANGI tare da Sharhin Fim din


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Tare Da: Saddika Habib Abba
No. 09097438402
Email habibsaddika@gmail.com
Suna: Kalen dangi
Tsara labari: Fauziyya D Sulaiman
Furodusa: Abubakar Bashir Mai Shadda
Director: Ali Gumzak
Kamfani: Tsamiya Inbestment

Jarumai: Ali nuhu, Aminu Sharif Momo, Sadik S Sadik, Sani
Idris Moda, Baballe Hayatu, Aisha Aliyu Tsamiya, Jamila
Nagudu, Hafsat Idris, Maryam Booth, Hajara Usman, Hadiza
Muh’d, Rabi’u Rikadawa, Ibrahim Mandawari.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

A farkon fim din an nuna gidan wani attajirin mai kudi
Alh.Mu’azzam Canji (Ibrahim Mandawari) shine shugaban
‘yan caji yana zaune a gidansa tare da matarsa (Hajara
Usman) da kuma ‘ya’yansa Guda biyu mata Fadila (Jamila
Nagudu) da kuma kanwarta Kubra (Maryam Booth) an nuna
cewar ita Fadila ‘yar karyace ‘yar nuna son a sani ce sannan
kuma ta tsani talaka tana kyamatarsa in har ya rabeta, ita
burinta ta auri me kudi, sai ita kanwarta ta Kubra ita babu
ruwanta da nuna ita mai kudi ce sannan tana da saukin kai
kuma tana harka da talaka, sai kuma bangaren masu aikin
gidan (Rabi’u Rikadawa) shine mai gadin gidan da matarsa
Marka (Hadizan Saima) da ‘ya’yansu ‘yan mata guda uku
duk a gidan suke zaune akwai Samira (Aisha Tsamiya) da
kuma Salma (Fati Washa) da kuma (Hafsat Barauniya)
amma dukkansu ‘ya’yan makaryata ne burinsu suyi wa
samari karya sannan su auri mai Kudi guda daya ce rak ta
kirki ( Hafsat Barauniya) itace bata goyon bayan abinda suke
yi sakamakon hakan ya haifarmata da tsana a wurin
mahaifiyarta Marka saboda ita  ma mahaifiyar mai idon cin
naira ce burinta ‘ya’yanta su auri mai kudi  a gurin
mahaifinsu Mai gadi  kadai ta ke samun sassauci domin shi
sam baya bin bayan abinda suke yi matar tasa ta fi karfinsa
ne kawai, Salma da Samira har kwalliya suke su tafi jami’a
da wurare na shakatawa su hada baki da direban gidan
Mado (Musa Mai Sana’a) ya daukesu yana zazzagawa dasu
acikin mota domin masu kudi su gansu suce suna san su
idan sun dawo zu kawo kudi su bawa Mado don dama kafin
su fita sai sun yi ciniki.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Sai bangaren Adamu (Ali Nuhu) wanda yake aikin direba a
gidan Alh.Sabo (Baballe Hayatu) shima babu abinda yake yi
sai karyar arziki idan ya dauki mota sai yaje yana yiwa ‘yan
mata karyar cewa motarsa ce domin yayansa shine
shugaban ‘yan kasuwa a haka har suka hadu da Samira suka
fara soyayya domin kowannensu yana zaton me kudi ne. sai
kuma bangaren Habu (Aminu Sharif)wanda yake zaune cikin
talauci da kakarsa kullum mafarkinsa ya zamto mai kudi ya
dinga hawa manyan motoci sannan burinsa iri daya tare da
wani Abokinsa Tukur (Sadik Sani Sadik) wanda yake shi
almajiri ne ma amma babu abinda suka saka a gaba sai son
su zama masu kudi domin su dinga yiwa ‘yan mata karya
ana cikin haka sai wataran Habu yazo gida ya tarar ankawo
wa kakarsa kayan abinci na zakka ya tambayeta waya kawo
tace masa Alh. Sunusi ne nan fa Habu ya fara tsalle da
murnar ashe dama a danginsu akwai mai kudi bata taba
fadamasa ba tace masa ba d’an uwanta bane sun yi zaman
makota ka ne tare da kakarsa shi kuma a lokacin yana yaro
Habu ya fara tsalle da murnar ai dan uwansu ne duk da haka
ba da bata lokaci ba ya nemi kwatancen gidan Alh. Sunusi
ya je ya yi masa bayani da farko bai gane shi ba sai da ya yi
masa bayanin ai shi jikan mai kosai ne wadda ya kawo wa
zakka dakyar Alh. Sunusi ya gane sannan ya daukeshi aiki
har yake bashi motarsa yana hawa anan  Habu ya  sake
samun lasisin yiwa abokai da ‘yanmata karya abotarsu da
Tukur ta sa ke kulluwa a haka har Habu ya hadu da Salma
suka fara soyyaya ita a zaton ta mai kudi ne shi kuma a
zatonsa ‘yar Alh. Mu’azzam canji ce domin haka tace masa
haka suka cigaba da yiwa juna karya.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

A bangaren gidan Alh. Sabo kuwa matarsa bata haihuwa har
ya yi yunkurin kara aure ya hadu da Fadila ta nuna cewar ita
bata harka da talaka domin duk ita a zaton ta talaka ne bata
san babban me arziki bane shi yasa taci zarafinsa har ya
hakura da neman aurenta wannan abinda ta yi masa shine
ya yi masa ciwo ya sanya suka hada baki da abokinsa Alh.
Sunusi domin a nemo yaro dan karya a biya shi yaje ya
yaudari Fadila da cewar shi mai kudi ne idan yaso bayan
auren sai ya bayyana mata kansa domin ta gane kuskurenta,
Alh. Sunusi ya sanya Habu ya nemo musu yaro Habu kuwa
ya nemo abokinsa Tukur su Alh. Sabo suka yaba da Tukur
sannan suka ba shi manyan motoci da kaya masu kyau
domin ya je ya sato zuciyar Fadila haka kuwa aka yi domin
Fadila tana ganinsa da wannan manyan motocin ta rude ta
amshi soyayyarsa suka kulla, ana cikin haka sai Alh. Sabo ya
kuma haduwa da kanwar Fadila Kubra itama ya nuna yana
sonta cikin girmamawa ta amshi soyyarsa.
Alh. Mu’azzam Canji kuwa ana haka  sai  ya umarci duk ‘yan
matan gidansa su fito da mijin aure kowacce ta fadawa na
ta saurayin kowannensu kuwa ya fito shi Adamu ya yi hayar
waliyyai da kayan aure Tukur da Habu kuwa Alh. Sabo ya yi
musu komai aka zo aka daura aure sai bayan an daura a
gurin fatin bikin kuma duk asiri ya tonu shi Tukur da kansa
ma ya ta shi ya bayyana ko shi wanene su kuma ragowar
wasu mata ne da Mado direba suka zo suka tona asiri a
gurin fatin hankalin kowannesu ya tashi har da masu cewar
sun fa sa.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Abubuwan Birgewa:

1- An yi amfani da kayan aiki masu kyau a labarin.

2- shirin ya tabo wata matsala da take faruwa a wannan
zamanin kuma an nuna wa masu irin wannan dabi’ar illar ta.

3- Jaruman kowannensu ya yi matukar kokari wurin isar da
sakon.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Kurakurai:

1- Akwai wurin da aka ga abun daukar sauti ya
fito a jikin Habu.

2- ‘ya mace ‘yar kwalliya ce amma kwalliyar da aka din ga
nu no wa a fuskokin duk jaruman mata a kodayaushe da
kowanne irin lokaci ta yi yawa don bazai yu ace kullum
mutum da kwalliya ba irin wannan babu wani ranar hutu an
nuna kamar ana nuna wa masu kallo su ga kwalliyar ne.

3-Bazai taba yi wu wa a gaske ace suna yin wannan
karyace karyacen kuma duk sun nemi aure a gida daya ba
amma asirinsu bai taba to nuwa ba, shin a auren babu
bincike da akayi? kawai auren aka yi?

4- Shin dama Mado direba mawaki ne ? ko kuma M.C ne? a
fim din direba kawai aka nuna yana yi amma sai ga shi an
ganshi a wurin biki yana M.C kuma yana waka.

5- Sutturar matan masu kudi manyan lesina ne da atamfofi
manya amma yanda ake kuranta kudin Alh. Mu’azzam gidan
da aka nuna yana ciki da sutturar da ‘ya’yansa da matarsa
suke sakawa ya yi Kadan a yanda ake bayyanar da arzkinsa.

6- Akwai wurin da Alh. Sabo ya ke fadawa Alh.Sunusi ya
hadu da Fadila a jami’a ta wulakanta shi a gaban mutane ta
saka ana kallonsa amma masu kallo sun san wurin da aka
nuna sun hadu ba jami’a bane kuma wurin babu kowa sai su
kadai amma har ya ce jama’a suna kallonsa.

7-Ka’ida idan za’ayi aure kowa yasan kafin akai ga daurin
aure ake zuwa ganin wurinda amarya za ta dauna amma sai
ga shi an nuna sai bayan daurin aure aka nuna an zo gidan
Habu ganin dakin Salma

8- Akwai wurin da Marka ta ke fadawa mijinta kayan
abincinsu ya kare har Hajiya take fadin ta dibi na su kowa ya
san masu aikin da suke zaune a gidan iyayen gidansu ba sa
siyan abinci a gidan ake fitar musu ballantana su Marka da
suke gidan tsahon shekara Ashirin da wani abu.

9- Habu da Tukur kowa ya san basu yi karatun boko ba
saboda babu hasali ma shi Tukur kolo ne amma sai ga shi
idan sun je wurin ‘yan matansu suna yi musu turanci mai
kyau bana dan koyo ba.

10- A irin arzikin Alh.Mu’azzam bai kamata ace direba daya
ba ne kuma motar da ake fita da ita daya ba ce  da har idan
aka sami matsala ‘yarsa za ta fita ta hau adaidaita sahu
kamar yanda Kubra ta yi lokacin da Mado ya ce Mota ta
sami matsala.

Karkarewa: Labarin ya kayatar kuma ya bai wa mutane
dariya, amma kuma karyace-karyacen da a ka nuna babu
yadda za a yi a gaske su faru kuma har a yi auren asiri bai
tonu ba. Wallahu a’alamu!

Source by Leadership A Yau and  Muryarhausa24.com