Wednesday 19 February 2020

Shin ko Ya Halatta na Sayi Kare Saboda Gadi a Gidana?

Tura Wannan Zuwa
Tambaya

Assalamu alaikum. Dr. Mene ne hukuncin ajiye kare a gida saboda gadi? Allah muke roƙo ya kara wa Dr lafiya da basira Amin.

         SHIN KO YA HALATTA NA SAYI KARE                    SABODA GADI A GIDANA

Marubuci: Dr. Jamilu Zarewa

Amsa

Wa'alaikum assalam, Ya tabbata a hadisin Bukhari da Muslim cewa: "Mala'iku ba sa shiga gidan da yake akwai hoto ko KARE a ciki.

A wani hadisin mai lamba ta: 2974 da Muslim ya rawaito Annabi (S.A.W) yana cewa: "Duk Wanda ya riƙe KARE, in ba Karen noma ba ko farauta ko kiwo, to Allah zai tauye masa  manyan lada guda biyu a kowacce rana.

Da yawa daga cikin malamai sun yi kiyasin KAREN GADI akan waɗancan nau'ukan guda uku da suka gabata, don haka ya halatta musulmi ya riƙi Kare saboda gadi in har akwai buƙatar hakan.

Ba ya halatta a siyar da kare kowanne iri ne, saboda Annabi ﷺ ya hana cin kuɗin Kare a hadisin da Muslim ya rawaito kuma ya kira Shi da dauda.

Duk da cewa an halatta waɗancan nau'ukan guda huɗu saboda buƙata sai dai bai halatta a siyar da su ba, saboda ƙa'ida sananniya a wajan malaman Fiqhu wacce take cewa:

ما جوز للحاجة لا يجوز أخذ العوض عليه

MAKALOLI MASU ALAKA:

SHIN DAN ALLAH MALAM ME NE NE HUKUNCIN YIN SAKI UKU A CIKIN FUSHI?

MALAM NA TSINCI NAIRA ₦500 KOZAN IYA AMFANI DA ITA BATARE DA CIGIYA BA?

DAN ALLAH MALAM ME NE NE BAMBANCIN MUTANE DA MALA'IKU?

Idan mutun yana buƙatar ɗaya daga cikin waɗancan nau'uka na karnuka guda huɗu da suke halatta, kuma bai samu wanda zai ba shi kyauta ba, ya halatta ya siya, Amma zunubin sayarwar yana kan wanda ya sayar tun da shi ne bai bayar ba, kamar yadda Ibnu Hazm ya faɗa a littafinsa na Muhallah 4/793, Ƙa'ida tabbatacciya a wajan malamai tana cewa:

ما حرم سدا للذريعة يباح للحاجة أو المصلحة الراجحة

Allah ne mafi sani.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin daɗin ku.

MURYAR HAUSA24 Kamfani ne mai zaman kansa domin bunƙasa harshen Hausa a duk sassan Duniya.

Burin Shafin MURYAR HAUSA24 zama babban shafi a Duniya da zai samu amincewar al'umma don Ilimantarwa.

MURYAR HAUSA24  Shafi ne da yake ƙunshe da abubuwan da suke da alaƙa da harshen Hausa da Al'ummar Hausa, sannan shafi ne da yake tafiya da Zamani da kuma tsarin Gargajiya na Iyaye da Kakanni, don Ilimantarwa da Kuma Faɗakarwa.

MURYAR HAUSA24  Shafi ne a Yanar Gizo da yake gabatar da shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla, cikin sa'o'i ashirin da huɗu Dare da Rana (24 Hours) ba tareda kakkautawa ba.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a faɗin Duniya.


MURYAR HAUSA24 Mun ƙudiri aniyar bunƙasa harshen Hausa  a sassan Duniya batare da nuna ƙabilanci ba, ta hanyar rubuce-rubuce da kuma sauraro (Audio) gami da kallan hoto mai motsi (Video).

Zaku iya aiko mana da Labari, Faɗakarwa, Tunatarwa, Ilimantarwa, Nishaɗantarwa, Wa'azartarwa da sauran su ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan adireshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user