Showing posts sorted by relevance for query Musa Muh'd. Sort by date Show all posts
Showing posts sorted by relevance for query Musa Muh'd. Sort by date Show all posts

Monday, 6 May 2019

KARANTA JERIN SUNAYEN MALAMAI DA ALARAMMOMIN DA JIBWIS TA KASA TA TURA TAFSIRIN RAMADAN NA 1439AH 1440H/2019 A JAHOHIN NAJERIYA DA KASASHEN DUNIYA

KARANTA JERIN SUNAYEN MALAMAI DA ALARAMMOMIN DA JIBWIS TA KASA TA TURA TAFSIRIN RAMADAN NA 1439AH 1440H/2019 A JAHOHIN NAJERIYA DA KASASHEN DUNIYA

JAMA’ATU IZALATIL BID’AH WA IKAMATIS SUNNAH SUNAYEN MALAMAI DA ALARAMMOMIN DA JIBWIS TA KASA TA TURA TAFSIRIN RAMADAN NA 1439AH 1440H/2019 A JAHOHIN NAJERIYA DA KASASHEN DUNIYA.




JIBWIS NIGERIA




1. Sheikh Abdullahi Bala Lau Da Alaramma Nasiru Salihu Gwandu - Jimeta, Adamawa

2. Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo Da Alaramma Mustapha Jalingo - Jalingo, Taraba

3. Sheikh Usman Isa Taliyawa Da Alaramma Abubakar Muhd Gombe - Gombe, Gombe

4. Sheikh Abbas Jega Da Alaramma Abubakar Adam - B/Kebbi, Kebbi

5. Sheikh Ibrahim Sabi’u Jibia Da Alaramma Aminu Salisu Jibia - Masjid Hamza Jibia, Katsina

6. Sheikh Yakubu Musa Hassan / Saifuddeen Yakubu Musa Da Alaramma Usman Birnin Kebbi - Katsina, Katsina

7. Sheikh Dr Isma’il Kumo Basirka Da Alaramma Usman Barikin Ladi - Jos, Plateau

8. Shk Dr. Abdullahi Saleh Pakistan Da Alaramma Abbas Iliyasu - Kano, Kano

9. Sheikh Muh’d Kabir Haruna Gombe Da Alaramma Ahmad Sulaiman - T/Wada / Malali, Kaduna

10. Sheik Dr Ali Mustapha Da Alaramma Mato Gumau - Gashua, Yobe

11. Sheikh Abubakar Giro Argungu Da Alaramma Saifullahi Musa Makera - Masjid Haruna Danja Zaria, Kaduna

12. Sheikh Aliyu Abdullahi Telex Da Alaramma Muhsin Ishaq - Aleiru, Kebbi

13. Sheikh Surajo Muhammad Gusau - Gusau, Zamfara

14. Sheikh Mas’ud Ibrahim Offa - Rimi College, Kaduna

15. Dr Muhammad Sani Umar R/lemo Da Alaramma Abubakar Muhammad Rariya - Masjid Gwallaga, Bauchi

16. Sheikh Sani Yakubu Da Alaramma Ridwan Kaduna - Zaria, Kaduna

17. Sheikh Abubakar Abdussalam Baban Gwale Da Alaramma Tukur Jakada - Alkhulafaur Rashidun, Alpa Nla, Agege, Lagos

18. Sheikh Ahmad Muhammad Boyi Da Alaramma Muhammad Aliyu Babangida - Masjid Finance Jalingo, Taraba

19. Dr Ibrahim Abdullahi Sani R/Lemo Da Alaramma Yusuf Suru - Area 11 Masjid, Abuja

20. Mall. Aliyu Ladan Da Alaramma Nasiru Dan Malam - Life Camp, Abuja

21. Mal AbdulRazak Yahaya Haifan Da Alaramma Kabir Hussaini Daura - Gwagwalada, Abuja

22. Mal. Abdullahi Umar Zaria Da Alaramma Salihu Gumi - Garki Village, Abuja

23. Mal. Auwal Mai Gaskiya Da Alaramma Aliyu Ibrahim Paki - Fed. Min. of Works, Abuja

24. Mal. Abdullahi Karshi Da Alaramma Abdulkrim Akwanga - Villa, Abuja

25. Mal. Sahibul Kuwa - Dakkwa, Abuja

26. Mal Abdulrahman Alzamfari Da Alaramma Saifullahi Kira - Berger Masjid, Abuja

27. Dr Ahmad Atiku Auwal - Gwarimpa Masjid, Abuja

28. Mal. Tajuddeen Imam Da Alaramma Murtala Muhammad - Prince & Princes, Abuja

29. Mal Adda’urrahman Alhassan Saeed - Gumel, Jigawa

30. Dr. Bashir Imam - Masjid Amb. Yola, Adamawa

31. Dr. Sadau Salihu - Yola, Adamawa

32. Dr. Abdulqadir Saleh Kazaure Da  Alaramma Idris Gashuwa - Jimeta, Adamawa

33. Dr Abubakar Bama - Masjid Nyanya, Abuja

34. Dr AbdulRahman Sani Yakubu Da Alaramma Sulaiman Abdullahi Azare -Juwa Emirate Council, Abuja

35. Mal Usman AbdulHamid - Numan, Adamawa

36. Mal. Alkali Sulaiman Yusuf Da Alaramma Dauda Muh’d Zukku - Masallachin Adamu Jumb, Bauchi

37.. Mal. Aliyu Saeed Gamawa Da Alaramma Saeed Adamu - Peoples Bank Masjid Gamawa, Bauchi

38. Dr. Ibrahim Adam Umar Disina- Masjid Rahama, Bauchi

39. Mal. Abba Abdullahi Gwale Da Alaramma Idris Saminaka - Lapai, Niger

40. Mall Abdul aziz Dan lami Da Alaramma
Nafiu A A saeed - Tilden Fulani, Bauchi

41. Mal. Abubakar Mala Da Alaramma Bala Bako - Alkaleri, Bauchi

42. Dr. Zubairu Madaki Da Alaramma Kabir Abdullahi - Masjid Umar bn Al khattab, Kofar Wambai, Bauchi

43. Shk Ahmad Tijjani Yusuf Guruntun Da Alaramma Muhammad Zahruddeen - Masj S19 Dutsen Tenshe Bauchi, Bauchi

44. Mal. Abubakar Mukhtar Yola - Masallachin Nepa Jimeta, Adamawa

45. Sheikh Abubakar Usman Pakistan Da Alaramma Farouq Jada Tambuwal - Makurdi, Benue

46. Mal. Nura Khalil - Apo, Legislative Quarters, Abuja

47. Mal Yaqub Isah Da Alaramma Adam Mahmud - Kwayakusar, Borno

48. Mal.Abba Musa Da Alaramma Aminu Ibrahim Potiskum - Maiduguri, Borno

49. Shk Muhd Abubakar Kachalla Da Alaramma Ahmad Jiha Ismail - Maiduguri, Borno

50. Mal Zainu Usman Baban Tine - NNPC Kaduna, Kaduna

51. Dr. Umar Dokaji Da Alaramma Auwal Ung Maikawo - Sapele, Delta

52. Mal. Nazifi Hashim Zaria Da Alaramma Hassan Musa Funtua - Cattle Market Benin City, Edo

53. Mal. Shafi’I Salihu Kazaure Da Alaramma Sani Ibrahim Mainiyya - Ung. Sabo Ile-Ife, Osun

54. Mal. Mustapha Yusuf Hadejia Da Alaramma Muhd Auwal Jalingo - P/Harcourt, Rivers

55. Mal. Adam Muhammad Adam Da Alaramma Abubakar Jibril Bula - Gombe, Gombe

56. Dr Abdallah Umar Gadon Kaya Da Alaramma Baba Lawal - Kan Bariki,( Water Board) Kumo, Gombe

57. Mal. Usman Bello Santuraki Kumo Da Alaramma Nafiu Ismail - Kazaure, Jigawa

58. Mal. Sulaiman Abubakar Birnin Kudu - Yalwan Damai, Jigawa


59. Mall Isa Abdullahi Da Alaramma Hamza Isa Abdullahi - Hadeja, Jigawa

60. Mal. Alkasim Hotoro Da Alaramma Yunus Isma’il - Potistum, Yobe

61. Dr Abdurrahman Idris zakariyya Da Alaramma Auwal Iliyasu - Saminaka, Kaduna

62. Mal. Musa Asadus Sunnah - Sokoto, Sokoto

63. Mal. Murtala Nasir Almisry Da Alaramma Aliyu Dahir - ASD Motors, Kaduna

64. Mall Abdulrahman Maiduguri Da Alaramma Shamsuddeen Haruna - Rigachikun, Kaduna

65. Mal Abubakar Usman Bolari - Oshogbo, Osun

66. Mal. Hamza Alhassan Sa’eed Da Alaramma Abubakar Rano - Sani Zangon Daura Estate, Kado, Abuja

67. Mal Nura Kofar Mata Da Alaramma Abubakar Umar Balarabe - Ojo-Express T/Sunnah Ibadan, Oyo

68. Mal. Ibrahim Abdullahi Bauchi Da Alaramma Kabiru Yawuri - Ado-Ekiti, Ekiti

69. Dr Idris Alhassan Abubakar Da Alaramma Shamsu Ahmad Mairuwa - Gboko, Benue

70. Sheikh Abdul Hadi Aliyu Daura Da Alaramma Yunusa Abubakar - Dan Fodio Masjid, Kaduna

71. Mal. Usman Zagga Da Alaramm Safiyan Abdullahi - Rijau, Niger

72. Mall Shuaibu Salihu Zaria Da Alaramma Abdullahi shu”aibu sal - Al-Islah Foundatn Zaria, Kaduna

73. Mal. Muhammad Sani Alhamidy - Bebeji, Kano

74. Mal. Abdul mudallib Ahmad Muhammad Da Alaramma Salihu Muhd Usman - Masjid Triump, Kano

75. Mall Abdul mudallib Gusau Da Alaramma Umar Ramadan - State Univ.Wudil, Kano

76. Mall Saifullahi Adam Shuaib Da Alaramma Tasiu Sabiu - Huguma Takai Kano, Kano

77. Mal Muhd Adam Algargawy - Kura, Kano

78. Mall Ibrahim Idris Zakariyya - Tudun Wadan Dankade, Kano

79. Mall Surajo Mahmoud Kankia - Govt Printing Katsina, Katsina

80. Mal. Aminu Liman Mustapha - Zaria Rd Masjid FT, Katsina

81. Mal. Mukhtar Usman Jibia - Govt. House, Katsina

82. Mal. Aminu Yammawa - Masjid. G.R.A, Katsina

83. Mal. Yahaya Salihu Isah Da Alaramma Auwal Umar - Masjid Kerau, Katsina

84. Mal. Musa Mansur Da Alaramma Salihu Ahmad - Masjid Karama Daura, Katsina

85. Mal. Hassan Yusuf Da Alaramma Haruna Salisu - Masjid Senator (Madawaki)Daura, Katsina

86. Dr Jamilu Zarewa Da Alaramma Ashiru Rawayau, Masj Bilal Ibn Rabah N/Low-Cost, Katsina

87. Mall Safiyyu Alqasim Saulawa Da Alaramma Mukhtar Salisu Jibiya - Bakori, Katsina

88. Mal. Jamilu Albani Da Alaramma Abuzaid - Lafia, Nasarawa

89. Mal. Umar Jiga Da Alaramma Shukranu Yelwan Shandam - Sokoto, Sokoto

90. Mal. Muhammad Rabi’u Isah Fatawa Da Alaramma Adam Muhammad Fana - Bena, Kebbi

91. Mal. Ahmad Ahmad Kura - Dutsin-ma, Katsina

92. Mal. Imam Aliyu Bunza Da Alaramma Amiru Ibrahim Argungun - Argungun, Kebbi

93. Mal.Umar Sadiq Jega Da Alaramma Iliyasu Birnin Gwari - Suleja, Niger

94. Sheikh Mukhtar Zinder - Illela, Sokoto

95. Mal. Imam Dahiru Lokoja Da Alaramma Ishaq - Lokoja, Kogi

96. Mal. Imam Yahaya Iddah Da Alaramma Auwal Muhammad - Iddah, Kogi

97. Mal. Yusuf Umar Da Alaramma Rabi’u Ibrahim - Obajana, Kogi

98. Mal. Salihu Muhammad Da Alaramma Ahmad Muhammad - Kaiama, Kwara

99. Mal. Attahiru Kaiama Da Alaramma Ibrahim Kaima - Ilorin, Kwara

100. Dr Abdulmajid Umar - Rimi Collage, Kaduna

101. Mal. Hussini Isa Abubakar Da Alaramma Nafi’u Bena - Yawuri, Kebbi

102. Dr Muhammad Sani Suleiman Ft Da Alarramma Abubakar Kaura - Gombe, Kumo, Gombe

103. Mall. Bukhari Yakubu Da Alaramma Muhammad fari - Agege Lagos, Lagos

104. Mall Adamu Salihu Gusau - Tambuwal, Sokoto

105. Sheikh Imam Sulaiman - Masjid 1004, Lagos

106. Mal. AbdulRahim Sabi’u Rafindadi Da Alaramma Sani Danwarai - Kontagora, Niger

107. Mall Adam Ibrahim Al-madani Da Alaramma Abbas Dahir Abubakar - Karu Masjid JIBWIS, Nassarawa

108. Mal Rufa’i Nasir Da Alaramma Ibrahim Abubakar - Keffi, Nasarawa

109. Dr Umar Gumi Da Alaramma Sulaiman Hussaini Doma - Doma, Nasarawa

110. Mal. Muh’d Sani Ahmad Almuhadis Da Alaramma Abubakar Bawa - Wawa, Niger

111. Mal. Lawal Shu’aibu Abubakar Da Alaramma Abdulrashid Jega - Minna, Niger

112. Mal. Mujittaba Yakubu Musa Da Alaramma Jamilu Isah Dallaje - Kafanchan, Kaduna

113. Mall Isah Shehu Ruga Da Alaramma Abubakar Ung Madi - Ganye, Adamawa

114. Mall.Muhammad Auwal Rijau Da Alaramma Abubakar A. Abubakar Kagara - Mariga, Niger

115. Mal. Abba Musa Da Alaramma Aminu Ibrahim - Maiduguri, Borno

116. Mall Musa Mujaddadi - Lafai, Nigrer

117. Mal.Bukhari Ibn Ishaq Albayani Da Alm Anas Abdullah Yalwan Shandam - Shiroro, Niger

118. Mal Isah Ibrahim Bawa Mai Shinkafa Da Alrm Ismail Abdullahi Mangu - Yalwan Shendam, Plateau

119. Mall Muhammad Aminu Muhammad Saminaka Da Alaramma Yusuf Dabai Mai  60 - Bukur, Plateau

120. Mal. Muhammad Barkindo Jungudo Da Alaramma Abdullahi Badejo - Jalingo Masjid Ummah, Taraba

121. Mall Nuruddeen Tukur Numan Da Alaramma Bashir Gombe - Jami’u Hajara Plaza Funtua, Katsina

122. Mal. Yunus Saeed Abdul-Hamid Da Refinery Depot, Rivers

123. Mal. Abdulbasir Ung MaiKawo Da Alarmma Sani Mulumfashi - Koko, Kebbi

124. Mal.Aliyu Aliyu Muhammad Jos Da Alaramma Bala Abubakar Tambuwal - Hadeja, Jigawa

125. Mal. Umar Mai Damma Da Alaramma Auwal Adam Sokoto - Masjid Sheik Abubakar Gumi Sokoto, Sokoto

126. Mal. Abubakar Ladan Mai Idigami Da Alaramma Muhammad Auwal - Masjid Lokoja Road Sokoto, Sokoto

127. Mall Sani Abubakar Tambuwal - Sultan Ibrahim Dasuki Mosque, Sokoto

128. Sheikh Dr. Mansur Ibrahim Sokoto Da Alaramma Abubakar Ghani - MasjidAbu Huraira, Sokoto

129. Dr Muhammad Rabi”u Collage Da Alaramma Sidi Ali - Ningi, Bauchi

130. Mal. Gambo Kyari Maiduguri Da Alaramma Mustapha Hamza Jarmai - Wukari, Taraba

131. Mal Khalid Usman Khalid Da Alaramma Salisu Ung. Kanawa - Gummi, Zamfara

132. Mal Hassan Bako - Shagamu, Ogun
133. Imam khidir Bello Manufa Da Alaramma Hudu Usman Aleiru - Bukkuyum, Zamfara

134. Mal. Attahiru Muhammad Tilde - Jaji Maji, Yobe

135. Mal Abdulaziz Ibrahim Bauchi Da Alaramma Sulaiman shafi’I FTA - Matazu, Katsina

136. Mal Aliyu S. Mafara Da Alaramma Usman Tagule - Kamba, Kebbi

137. Mal.Ibrahim Damaturu Da Alaramma Sani Nguru - Damaturu, Yobe

138. Dr Umar Musa Kano Da Alaramma Bello Argungu - Anka, Zamfara

139. Mal. Usman Arabi - Malumfashi, Katsina

140. Mal. Aminu Numan Da Alaramma Amir Abdullahi Dorawa - Mangu, Plateau

141. Mal. Abubakar Salihu Dengi - Ibadan, Oyo

142. Mal. Anas Assalafy - Ketaren Waya, Benue

143. Mal. Abubakar Musa Azi - Ebonyi, Ebonyi

144. Mal. Shuaibu Adam Makoli - Dangi, Plateau

145. Mal. Aminu Khalil U/Barau - Masjid Ahlil Sunnah Ikorodu, Lagos

146. Mal Surajo Umar Maga Da Alaramma Alkasim Musa - Masjid Hausa Qtrs Ugella, Delta

147. Mal Musa Usman Alkanawi Da Alaramma Mu’awiyya Adbdulrahman - Masjid Ujole, Ekpoma Town, Edo

148. Mal Abubakar Usman Da Alaramma Anas Abubakar - Masjid Lagos Str Benin City, Edo

149. Sheik Muhammad Fatihu Da Alaramma Ibrahim Adam Futua - Apo Legislative Qtrs Zone A, FCT

150. Sheik Ibrahim Lawal (USAMA) Alaramma Zaharadden Surajo - Apo Legislative Qtrs Zone B, FCT

151. Mal. Muhammad Abubakar Da Alaramma Fadlu Muhammad - Apo Legislative Qtrs Zone D, FCT

152. Mal Yahaya Gidadawa Da Alaramma Mustapha Hamza Jarmai - Onitsha, Anambra

153. Mal Murtala Bello Da’a Da Alaramma Ibrahim khamis Saminaka - Benin city, Edo

154. Mal Hussaini Yusuf Mabera Da Alaramma Mustapha Argungu - Warri, Delta

155. Mall. Muhammad Auwal Isah Jere Da Alaramma Murtada M. Namadi - Bakin Gareji,Jere, Kaduna

156. Dr Abubakar Usman Ribah Da Alaramma Muhammad Bunza - Bargu, Niger

157. Mall Rabi’u Aminu Bebeji - Geidam,  Yobe


GHANA

1. Mal. Muhammad Umar Abdulhanna Da Alaramma Abdulrahman Abubakar - Masjid Ib Abbas Ghana

2. Mal. Ahmad Ibrahim - Masjid Khulafa’urrashi
dun

3. Mal. Muh’d Bello Muh’d Saminu - Masjid Bilal

4. Mal. Sanusi Yusuf Muh’d - Masjid Furqan

5. Mal. Abdul Razak Kumasi Da Alaramma
Abdullahi Ibrahim - Masjid Daraarul Hadith

6. Mal. Abdul Malik Idris - Masjid Attaqwa

7. Mal. Muhammad Kaamil Da Alaramma Abubakar Idris - Masjid Ta’afo

8. Mal. Muhammad Addo - Masjid Zuraak

9. Mal. Muhammad Suwaid - Annaduwa

10. Mal. Manir Saeed - Bilal Accara

11. Mal. Sulaiman Adam Aljamzuri - Masjid Jami’ul Rahma

12. Mal. Muhammad Taufeeq Abdulrahman Kulusey - Masjidul Nurul Ameen


TOGO


1. Mal. Muawiyya Umar Mukhtar Ali Da
Alaramma Mukhtar Ali - Masjid Abu Ubaida

2. Mal. Salihu Saaya - Masjid Furqan

3. Mal. Abubakar Ali - Masjid Attaqwa

4. Imam Ahalil Sunnah (Abdulwahab Abdallah) Da Alaramma Dan Mairogo - Babban Masallacin Zango

COT’D VOURE


1. Mal. Jibirilu Musa Da Alaramma Usman Muh’d - Masjid Khausar Farbi Abidjan

2. Mal. Alhassan Musa Da Alaramma Abubakar - Apobo Abidja

3. Mal. Muh’d Abdulkarim Da Alaramma Abubakar Musa - Masjid Alh. Yusha’u Usaini Abidjan

4. Mal. Abdulsalam Shu’aibu Da Alaramma
Ukasha Alasan - Masjid Hausa Bugu Korgu

5. Mal. Khalil Abubakar Da Alaramma Abubakar Madu - Masjid Hausa Sempedro

6. Mal. Idris Haruna Da Alaramma Buhari Sale - Fresh Zeal Abidja

7. Mal. Muhammad Hariz Da Alaramma Abdullahi Yusuf Yakubu

8. Mal. Hamza Abdullahi Da Alaramma Abdullahi Abdulrahman - Yamasukuro

9. Mal. Hamza Idris - Yamasukuro

NIGER REP.


1. Mal. Imam Abdullah Umar - Masjid Imam Malik Niamey

2. Mal. Hussaini Hassan - Masjid Usman Ibn Affan Niamey

3. Mal. Abdul rahman Hussaini - Masjid Imamul Bukhari Niamey

4. Mal. Kasim Ali - Masjid Umar bn Khattab Niame

5. Mal. Iliyasu Abdullahi Da Alaramma Adam Muh’d Ibrahim - Masjid Karkada Zinder

6. Mal. Nazir Manzo Magarya Da Alaramma Abubakar Alhassan - Magarya

7. Mal. Abubakar Ibrahim - Magarya

8. Mal. Murtala Ibrahim - Maradi

9. Mal. Murtala Ibrahim - Tassawa

10. Mal. Adamu Salihu - Dosso

11. Mal. Abba Ghana - Tahoa

12. Mal. Nuhu Muhammad - Tahoa

13. Mal. Khamis Ahmad Da Alaramma Abubakar Usman - Galmi

14. Mal. Muhammad Khulud Ahmad - Maine, Soroa

15. Mal. Adam Ibrahim - Dosso

16. Mal. Abdulrahman - Teleberi

17. Mal. Dauda Nuhu - Teleberi

18. Mal. Yakubu - Teleberi

19. Mal. Yunus Chilakaro - Diffa

20. Mal. Abba Ghana - TahoaMal.

21. Ishaq Adam (Barrister) Da Alaramma Abdulhay. - Umar bn Alkhadab Gaya

22. Sheik Shuaibu Muhammadu Da Alaramma Sulaiman Abubakar - Masjud Al’ansar Niamey

23. Mal. Aliyu Muhammad Sani Adarawa Da Alaramma Ibrahim Yahuza Bauchi - Niamey

24. Mal.Muhammadu Haruna Gaya Da Alaramma Nuhu Adamu - Masjid Imam Malik

25. Mal.Muhammad Usman Da Alaramma Khalil Iarhim - Masjid Muhajirin

26. Mal.Sanusi Abubakar Da Alaramma Muhammad Abubkar - Masjid Round Point Ba Are

27. Mal. Salifou Abdullahi Maradi Da Alaramma Kamissou - Masjid Marad

28. Mal. Buhari Muhammad Da Alaramma Idrissa Issofou - Masjid Tahoa

29. Mal. Salissou Garba Da Alaramma Massa-oudour Hussaini - Masjid Diffa

30. Mal. Laminou Da Alaramma Aliou Moussa - Masjid Zinder

31 Mal. Khalid Hassan Da Alaramma Abdullbaki - Masjid Niamey

32. Mal. Ousseini Abdoulaye Da Alaramma Laouali - Masjid Arlit

33. Mal. Bachirou Yahaye Da Alaramma Ibrahim - Masjid Tillaberi

BURKINA FASO


1. Mal. Yakubu Tanko - Kantchari

2. Mal. Hamma Zakariya - Namuno

3. Mal. Dr. Kindo Muhammad - Ougadougou

4. Mal. Muhammad Bashir Da Alaramma Yahaya Adam - Falagountou

5. Mal. Aufon Muhammad - Falagountou

6. Mal. Muhammad Usman - Masjid Furqan


BENIN REP.



1. Mal. Muhammad Kabir - Zango Cottonou

2. Mal. Suleiman Abubakar Da Alaramma Abu Sambo - Malabil

3. Mal. Abdulganiyu Raji Da Alaramma Shuaibu Latifi - Malabil

4. Mal. Jibril Abubakar Da Alaramma Ibrahim Abdullahi - Cotonor

5. Mal. Umar Garba Da Alaramma Zubair Mairiga - Cotonor

6. Mal. Idris Ishaq Da Alaramma Mujahid Dahir - Zuggu

7. Mal. Usman Abdulwahab Da Alaramma Hudu Abdullatif - Zuggu

8. Mal. Marwan Umar Da Alaramma Abdul Mateen - Kandee

9. Mal. Haruna Alhassan Da Alaramma Nasir Ishaq - Kandee

10. Mal. Dr. Dauda Da Alaramma Isa Adam - Kandee

11. Sheikh Abdullahi Banji Da Alaramma Jibril Ahmad - Malabil

12. Mal. Khalid Zakariya Da Alaramma Dauda Abubakar - Boyiko

13. Mal. Mukhtar - Farako

CAMEROUN


1. Sheikh Saidu Makoli - Bamenda

2. Sheikh Dr. Abu Umar Bala - Bamenda

3. Sheikh Suleman - Douala

4. Sheikh Bello - Younde

5. Sheikh Hadi - Younde

6. Sheikh Godabe - Doula

7. Sheikh Usman - Younde

8. Sheikh Sule Adam Labo - Masjid
ITTIHAD, Doula

9. Sheikh Abu Umar - Masjid Nur, Baminda

10. Sheikh Usman Biyagoro - Masjid Mgyengai, Younde

11. Sheikh Bello - Masjid Alhaji Garbati, Younde

12. Imam Mahmud Aliyu - Baban Masallacin Sarki, Gamdare

13. Sheikh Abdullahi - Masjid Alhaji Adam Bertuwa

14. Sheikh Zakariya Dotti - Masjid Salam, Doula

15. Sheikh Yakubu - Masjid Rahma Walhidaya, Doual

16. Sheikh Nasara Ismail Bagori - Masjid Taqwa

SENEGAL


1. Mal. Abdulkarim Yahaya - Dakar
GUINEA CONAKRY

1. Dr. Mourris Abubakar - Conakry
CENTRAL AFRICA

1. Dr. Badiga Moussa - Bangui

SAUDI ARABIA

1. Shiekh Rajab - Masjidu Ameera Makkah
United State Of America (USA)

1. Mal. Kassim Muhammad Bella - Masjid Mumineen 8875 Benning, Dr Houston Texas 77031, USA

2. Mal. Firdaws Ladan - Masjid Ibn Taymiyyah 8000 martin luther king Jr Hwj,Glen, Arden,MD, USA
Europe(UK)

1. Mal.Muhammad Mubarak Abdulai (M Bature) - Mrkazul Tauheed NO.1 rectory Road,St 1,Stoke on Trent, Staffordshire, UK


2. Mal.Muhammad Saifuddeen Abubakar - Masjidul Salaam Comunidad Islamica De Benidorn Juzgados, Benidorm, Alicante, Spain

3. Mal.Mu’azu Shu’aib Bamba - Masjidul Sunnah Uppsala, Bandstolvagen,37,75648

4. Mal.yousuf Umar Jallo - Masjidul Rahma (Hamburg) Beim Gesundbrunnen 1 ,20537,hamburg, Germany

5. Mal.Muhammad Brussels - Masjid Abubakar Sddiq Rue de la Colonne, 32,Bruxells 1080. Belgium

Allah ya taimaka, ya bada ikon aiki da abun da za'a gabatar. Amin.



Sanarwa: Sakataren kungiya na kasa
Sheikh Dr. Kabiru Gombe.


Via: Ibrahim Baba Suleiman
Director General, Jibwis
Social Media.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode






Source: Jibwis Nigeria

Tuesday, 11 June 2024

Kyakyatawa Dole: Mata Da Miji A Mota

Kyakyatawa Dole: Mata Da Miji A Mota

Wani saurayi ne ya je zance gurin masoyiyarsa, sai budurwarsa ta buƙaci ya ba ta labari, sai ya ce "To amma labarin kashi na 1, da na 2 da na 3 da na 4 ne".


Mata da Miji a mota
Hoto: People Images


Marubuci: Musa Muh'd


Sai ta ce ya ba ta, saurayin ya fara bayar da labarin kamar haka;


Kashi 1: Wani miji ne da matarsa, suna cikin tafiya a mota, can sai suka zo  mararrabar hanya, sai ya cewa matar hanyar hagu za mu bi? Matar ta ce a'a maigida mu bi hanyar da ta bi dama, aikuwa sai ya kwashe ta da mari ya ce "Ni na ke tuƙa motar ko kuwa ke? Hanyar hagu za mu bi, sai budurwar ta yi dariya ta ce "Amma wannan miji akwai mugu."


Saurayi ya ce "Saura kashi na 2: suka bi hanya suna tafiya suka iso gurin masu sai da kifi, Maigida ya saya musu, matar ta ce Maigida mai za a yi da shi? ya ce dafawa za ki yi, aikuwa matar ta zabge shi da mari, ta ce kai ne kake girkin ko ni ce? To Soyawa zan yi.


Budurwar ta ƙyalƙyale da dariya, ta ce amma ta burge ni ka ga sun yi duro, saurayi ya ce  saura kashi na 4, sai budurwar ta ce a'a kashi na 3 dai, saurayi ya kwashe ta da mari, ya ce ni ne nake bada labarin ko ke ce?


Shin idan ke ce budurwar me za ki yi masa?


Monday, 23 April 2018

Karanta Kaji: Kuskure 10 da akai acikin Film din KALAN DANGI tare da Sharhin Fim din

Karanta Kaji: Kuskure 10 da akai acikin Film din KALAN DANGI tare da Sharhin Fim din


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Tare Da: Saddika Habib Abba
No. 09097438402
Email habibsaddika@gmail.com
Suna: Kalen dangi
Tsara labari: Fauziyya D Sulaiman
Furodusa: Abubakar Bashir Mai Shadda
Director: Ali Gumzak
Kamfani: Tsamiya Inbestment

Jarumai: Ali nuhu, Aminu Sharif Momo, Sadik S Sadik, Sani
Idris Moda, Baballe Hayatu, Aisha Aliyu Tsamiya, Jamila
Nagudu, Hafsat Idris, Maryam Booth, Hajara Usman, Hadiza
Muh’d, Rabi’u Rikadawa, Ibrahim Mandawari.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

A farkon fim din an nuna gidan wani attajirin mai kudi
Alh.Mu’azzam Canji (Ibrahim Mandawari) shine shugaban
‘yan caji yana zaune a gidansa tare da matarsa (Hajara
Usman) da kuma ‘ya’yansa Guda biyu mata Fadila (Jamila
Nagudu) da kuma kanwarta Kubra (Maryam Booth) an nuna
cewar ita Fadila ‘yar karyace ‘yar nuna son a sani ce sannan
kuma ta tsani talaka tana kyamatarsa in har ya rabeta, ita
burinta ta auri me kudi, sai ita kanwarta ta Kubra ita babu
ruwanta da nuna ita mai kudi ce sannan tana da saukin kai
kuma tana harka da talaka, sai kuma bangaren masu aikin
gidan (Rabi’u Rikadawa) shine mai gadin gidan da matarsa
Marka (Hadizan Saima) da ‘ya’yansu ‘yan mata guda uku
duk a gidan suke zaune akwai Samira (Aisha Tsamiya) da
kuma Salma (Fati Washa) da kuma (Hafsat Barauniya)
amma dukkansu ‘ya’yan makaryata ne burinsu suyi wa
samari karya sannan su auri mai Kudi guda daya ce rak ta
kirki ( Hafsat Barauniya) itace bata goyon bayan abinda suke
yi sakamakon hakan ya haifarmata da tsana a wurin
mahaifiyarta Marka saboda ita  ma mahaifiyar mai idon cin
naira ce burinta ‘ya’yanta su auri mai kudi  a gurin
mahaifinsu Mai gadi  kadai ta ke samun sassauci domin shi
sam baya bin bayan abinda suke yi matar tasa ta fi karfinsa
ne kawai, Salma da Samira har kwalliya suke su tafi jami’a
da wurare na shakatawa su hada baki da direban gidan
Mado (Musa Mai Sana’a) ya daukesu yana zazzagawa dasu
acikin mota domin masu kudi su gansu suce suna san su
idan sun dawo zu kawo kudi su bawa Mado don dama kafin
su fita sai sun yi ciniki.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Sai bangaren Adamu (Ali Nuhu) wanda yake aikin direba a
gidan Alh.Sabo (Baballe Hayatu) shima babu abinda yake yi
sai karyar arziki idan ya dauki mota sai yaje yana yiwa ‘yan
mata karyar cewa motarsa ce domin yayansa shine
shugaban ‘yan kasuwa a haka har suka hadu da Samira suka
fara soyayya domin kowannensu yana zaton me kudi ne. sai
kuma bangaren Habu (Aminu Sharif)wanda yake zaune cikin
talauci da kakarsa kullum mafarkinsa ya zamto mai kudi ya
dinga hawa manyan motoci sannan burinsa iri daya tare da
wani Abokinsa Tukur (Sadik Sani Sadik) wanda yake shi
almajiri ne ma amma babu abinda suka saka a gaba sai son
su zama masu kudi domin su dinga yiwa ‘yan mata karya
ana cikin haka sai wataran Habu yazo gida ya tarar ankawo
wa kakarsa kayan abinci na zakka ya tambayeta waya kawo
tace masa Alh. Sunusi ne nan fa Habu ya fara tsalle da
murnar ashe dama a danginsu akwai mai kudi bata taba
fadamasa ba tace masa ba d’an uwanta bane sun yi zaman
makota ka ne tare da kakarsa shi kuma a lokacin yana yaro
Habu ya fara tsalle da murnar ai dan uwansu ne duk da haka
ba da bata lokaci ba ya nemi kwatancen gidan Alh. Sunusi
ya je ya yi masa bayani da farko bai gane shi ba sai da ya yi
masa bayanin ai shi jikan mai kosai ne wadda ya kawo wa
zakka dakyar Alh. Sunusi ya gane sannan ya daukeshi aiki
har yake bashi motarsa yana hawa anan  Habu ya  sake
samun lasisin yiwa abokai da ‘yanmata karya abotarsu da
Tukur ta sa ke kulluwa a haka har Habu ya hadu da Salma
suka fara soyyaya ita a zaton ta mai kudi ne shi kuma a
zatonsa ‘yar Alh. Mu’azzam canji ce domin haka tace masa
haka suka cigaba da yiwa juna karya.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

A bangaren gidan Alh. Sabo kuwa matarsa bata haihuwa har
ya yi yunkurin kara aure ya hadu da Fadila ta nuna cewar ita
bata harka da talaka domin duk ita a zaton ta talaka ne bata
san babban me arziki bane shi yasa taci zarafinsa har ya
hakura da neman aurenta wannan abinda ta yi masa shine
ya yi masa ciwo ya sanya suka hada baki da abokinsa Alh.
Sunusi domin a nemo yaro dan karya a biya shi yaje ya
yaudari Fadila da cewar shi mai kudi ne idan yaso bayan
auren sai ya bayyana mata kansa domin ta gane kuskurenta,
Alh. Sunusi ya sanya Habu ya nemo musu yaro Habu kuwa
ya nemo abokinsa Tukur su Alh. Sabo suka yaba da Tukur
sannan suka ba shi manyan motoci da kaya masu kyau
domin ya je ya sato zuciyar Fadila haka kuwa aka yi domin
Fadila tana ganinsa da wannan manyan motocin ta rude ta
amshi soyayyarsa suka kulla, ana cikin haka sai Alh. Sabo ya
kuma haduwa da kanwar Fadila Kubra itama ya nuna yana
sonta cikin girmamawa ta amshi soyyarsa.
Alh. Mu’azzam Canji kuwa ana haka  sai  ya umarci duk ‘yan
matan gidansa su fito da mijin aure kowacce ta fadawa na
ta saurayin kowannensu kuwa ya fito shi Adamu ya yi hayar
waliyyai da kayan aure Tukur da Habu kuwa Alh. Sabo ya yi
musu komai aka zo aka daura aure sai bayan an daura a
gurin fatin bikin kuma duk asiri ya tonu shi Tukur da kansa
ma ya ta shi ya bayyana ko shi wanene su kuma ragowar
wasu mata ne da Mado direba suka zo suka tona asiri a
gurin fatin hankalin kowannesu ya tashi har da masu cewar
sun fa sa.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Abubuwan Birgewa:

1- An yi amfani da kayan aiki masu kyau a labarin.

2- shirin ya tabo wata matsala da take faruwa a wannan
zamanin kuma an nuna wa masu irin wannan dabi’ar illar ta.

3- Jaruman kowannensu ya yi matukar kokari wurin isar da
sakon.


Hotuna daga Shafin Muryarhausa24.com

Kurakurai:

1- Akwai wurin da aka ga abun daukar sauti ya
fito a jikin Habu.

2- ‘ya mace ‘yar kwalliya ce amma kwalliyar da aka din ga
nu no wa a fuskokin duk jaruman mata a kodayaushe da
kowanne irin lokaci ta yi yawa don bazai yu ace kullum
mutum da kwalliya ba irin wannan babu wani ranar hutu an
nuna kamar ana nuna wa masu kallo su ga kwalliyar ne.

3-Bazai taba yi wu wa a gaske ace suna yin wannan
karyace karyacen kuma duk sun nemi aure a gida daya ba
amma asirinsu bai taba to nuwa ba, shin a auren babu
bincike da akayi? kawai auren aka yi?

4- Shin dama Mado direba mawaki ne ? ko kuma M.C ne? a
fim din direba kawai aka nuna yana yi amma sai ga shi an
ganshi a wurin biki yana M.C kuma yana waka.

5- Sutturar matan masu kudi manyan lesina ne da atamfofi
manya amma yanda ake kuranta kudin Alh. Mu’azzam gidan
da aka nuna yana ciki da sutturar da ‘ya’yansa da matarsa
suke sakawa ya yi Kadan a yanda ake bayyanar da arzkinsa.

6- Akwai wurin da Alh. Sabo ya ke fadawa Alh.Sunusi ya
hadu da Fadila a jami’a ta wulakanta shi a gaban mutane ta
saka ana kallonsa amma masu kallo sun san wurin da aka
nuna sun hadu ba jami’a bane kuma wurin babu kowa sai su
kadai amma har ya ce jama’a suna kallonsa.

7-Ka’ida idan za’ayi aure kowa yasan kafin akai ga daurin
aure ake zuwa ganin wurinda amarya za ta dauna amma sai
ga shi an nuna sai bayan daurin aure aka nuna an zo gidan
Habu ganin dakin Salma

8- Akwai wurin da Marka ta ke fadawa mijinta kayan
abincinsu ya kare har Hajiya take fadin ta dibi na su kowa ya
san masu aikin da suke zaune a gidan iyayen gidansu ba sa
siyan abinci a gidan ake fitar musu ballantana su Marka da
suke gidan tsahon shekara Ashirin da wani abu.

9- Habu da Tukur kowa ya san basu yi karatun boko ba
saboda babu hasali ma shi Tukur kolo ne amma sai ga shi
idan sun je wurin ‘yan matansu suna yi musu turanci mai
kyau bana dan koyo ba.

10- A irin arzikin Alh.Mu’azzam bai kamata ace direba daya
ba ne kuma motar da ake fita da ita daya ba ce  da har idan
aka sami matsala ‘yarsa za ta fita ta hau adaidaita sahu
kamar yanda Kubra ta yi lokacin da Mado ya ce Mota ta
sami matsala.

Karkarewa: Labarin ya kayatar kuma ya bai wa mutane
dariya, amma kuma karyace-karyacen da a ka nuna babu
yadda za a yi a gaske su faru kuma har a yi auren asiri bai
tonu ba. Wallahu a’alamu!

Source by Leadership A Yau and  Muryarhausa24.com

Monday, 26 August 2019

Karanta Abubuwan Mamakin da Suka Faru a Ranar Hausa Ta Duniya

Karanta Abubuwan Mamakin da Suka Faru a Ranar Hausa Ta Duniya

A duk ranar 26 ga watan Agusta, rana ce da akaware saboda Hausa a Duniya. 

Farin Ciki da Ranar Hausa a Duniya

Saboda farin ciki da wannan rana a yau, yasa Muryar Husa24 ta kawo muku wasu daga cikin sharhin mabiyan mu akan wannan rana domin nuna farin cikin su da zagayowar wannan rana mai albarka.

Sharhin Bukar Mada

Wasu kalmomin Hausa masu ma'ana fiye da ɗaya.

1. RAMA

Rahamu ta taƙarƙare da cin ganyen RAMA kullum wai don ta yi maganin yunwar da ke sa RAMA, don ta ji an ce ramamme ba ya RAMA bugu.

2. KARA

Kallamu ya kora karsanarsa zuwa KARA domin ya sayar, a kan hanya ta ture wa Ali rumfar KARA da yakan kasa KARAn rake, da yake Ali mutum ne mai haƙuri da KARA sai ya yafe wa Kallamu.

3. KARE

Musa ya suri sandarsa da yake KARE da ita idan suna wasan karabkiya shi da Ja'e, ya nufi 'yan dangullan da yake kiwo a guje domin ya KARE su daga wani baƙin KARE da ya hango yana dafafen su yana yaƙe haƙora.

4. ZUBA

Kande takan so ta ZUBA wa Habu miya da tantakwashi, idan miyar ta kai masa karo, ya fara ZUBA mata labarin da babu waƙafi balle aya, tamkar bishiyar da ganyenta ke ZUBA lokacin hunturu, takan dube shi ta bushe da dariya.

5. TAFI

Lokacin da Inde ya TAFI gidan Sarkin Noma domin ya roƙoTAFI  uku na irin dawa sai ya jiyo matan gidan na daka suna TAFI da carabke.

6. RUGA

Audu ya RUGA da gudu yana dariyar ƙeta lokacin da ya wawushe sauran ɗanwaken da suke ci shi da Rabe ya RUGA shi duka a cikin baki, Rabe ya bi shi, suka yi ta guje-guje a cikin RUGA suka firgita zabi da kaji waɗanda suka haye saman damfami suna ta kwakwazo.

7. TUƘA

Kabiru ya TUƘA a-kori-kurarsa ya nufi siton Alhaji Audu Dankwangila domin ya ɗauko hatsin da za a TUƘA wa 'yan makaranta tuwo, a kan hanya ya wuce Garba a cikin rumfarsa yana TUƘA (tubka) igiyar da zai ɗaure ragonsa da ya ci ya ƙoshi yana ta faman TUƘA abin da ya ci.

8. KURA

Wata KURA da ta kubce babu takunkumi a cikin ƙauyen Magangari ta sa wani mutum ya yi watsi da ruwan da ya turo a KURA, garin gudu ya ture wani yaro da ke janye da KURA (mayen ƙarfe) yana kama ƙananan ƙarafunan da ke turbuɗe a cikin ƙasa.

9. CAJI

Sule ya kai batirin wayarsa wajen mai CAJI, lokacin da ya CAJI aljihunsa domin biyan kuɗin sai ya ji babu ko ƙarfanfana, nan take ya juya da sauri domin ya CAJI Ɗari da laifin lalube masa aljihu lokacin da suke kallon ƙwallo.

10. TURMI

Mani ya saɓi TURMI guda na atamfa daga cikin shagonsa, ya nufi ƙauye domin ya kai wa Inna ziyara, lokacin da ya isa sai ya tarar da ita tana daka magani a TURMI wanda Buba zai shafa a mummuƙe saboda haƙoransa, TURMI, da ya yi kogo yana masa ciwo.

DUBA WADANNAN:

Karanta Takaitaccen Tarihi akan Tushen Harshen Hausa da Al'ummar Hausawa

Ko Ka San Harufan Hausa Guda Nawa Ne?

Karanta Takaitaccen Tarihin Yaren Harshen Hausa

Ga kuma ƙarin wasu kalmomin, ko za a iya jaraba sanya kowace a cikin jimla tare da kawo dukkan ma'anoninta kamar yadda muka bayar da misali a sama? Kowa ya bar gida, gida ya bar shi. Bisimillah!

Rago

Gara

Dama

Zage

Mari

Waya

Gari

Sara

Gado

Fara

Fito

Guga

Gora

Baiwa

Kwaɗo

Rina

Sa'a

Dawa

Duma

Taki

Dare

Baƙi

Kuɗi

Wuri

Wari

Taro

 Sharhin Shu'aibu Alkali


KANANCI–SAKKWATANCI

Eh–Awo wallah

Wannan–Wanga

Kuli-Kuli–Bakuru

Gyad'a–Gujjiya

Dankali–Kudaku

Bacci–Kwana

'Kofa–Garka

Gumi–Zuhwa

Ina kwana?–Kwal lahiya?

Miyar Kuka–Miyar 'Bakko/Kad'i

Zogala–TaMakka

Miyar Taushe–Miyar Sure

Me kace?–Mi kacce?

Gafiya–Burgu

'Bera–Kusu

Kyanwa–Mussa


Kana Bahaushe kana raina Hausa da Hausawa, har ma kana ganin cin darasin Hausa a makaranta ba wani abun a zo a gani ba ne. Bayan Mama da Baba da suka sa ka makarantar har ka yi wayewar da ta rude ka kake ganin Hausa da Hausawan ba abakin komai ba, babu Yaren da suka iya suke alfahari da shi sama da Hausar, ba su kuma da dangin da suka wuce Hausawan.
Alaji, sunanka Shagiri-girbau, sako-tumaki-ballo-jakkai.


RANAR HAUSA.

Gaskiya ce babu wasa, 
    Ta shige sak'o da  sassa,
              Ko'ina ta yad'a rassa,
                Duniya in dai ka dosa,
                    Za ka sam yare na Hausa.

Alfahar da zama Bahaushe,
   Hausa nan aka samu Baushe,
            Goro ko a kirashi Daushe,
              A miyar Hausa da Taushe,
                Wanda za'a hada da tuwo a kwasa.

Bahaushe ke da Hausa,
  Yai karin magana da Hausa,
        Yayyi zaurance da Hausa,
           Ko yama zambo da Hausa,
              Sai kwararre zai san ina ya dosa.

Hausa ne ke da kalamai,
    A rubuce kamar alamai,
      Sai a furtawa su zan mai,
         Masu banbanci kula mai,
            Ne d'ai zai san me suka k'unsa.

K'waro aka cewa Fara,
   Mai marar fata kwa Fara,
       Haka wani k'waro fa Gara,
          Wanda ke wawanci fa Gara,
                    Ka ji yare namu Hausa.

Sumar kai ce fa Gashi,
   In ka mik'a kuma Gashi,
     Tsuntsuwa kuma ke ta Tashi,
                Za ka mik'e kuma Tashi,
                    Kun fahimci ina na dosa.

To akwai bishiya ta Dashi,
    Masu tara kudi kwa Dashi,
           K'wace aka cewa Fashi,
             K'in zuwa makaranta Fashi,
                        Ba'a tsere mana gasa.

Kun sani da yawa irinsa,
       Na sani ko da a gasa,
         Ba'a tsere mana wasa,
           Matukar mun san irinsa,
              Ko da Jinn sai mun wucesa.


SABODA RANAR HAUSA.

Fadi sunan wadannan abubuwan da HAUSA;

1- Kwalba
2- Kwana
3- Duniya
4- Bokiti
5- Keke
6- Rashawa
7- Mota
8- Inji
9- Injin nika
10- Aljannah

Fadi ma'anar wadannan abubuwan;

1- Gafaka
2- Korami
3- Dumfama
4- Sakali
5- Kura tandu
6- Abawa
7- Laulawa
8- Nade da mai
9- Komaiya
10- Da6e

SHARHIN JAAFAR JAAFAR

Sunayen Igbo da Yarabawa da Turawa da sauran kabilu wandanda Hausawa suka canjawa launi.

1) Tope = Takwai
2) Kingsley = Kirsili
3) Gbenga = Biyanga
4) Ifreke = Cikurege
5) Ngozi = Ingozi
6) Nwankwo = Nawanko
7) Gbagyi = Gwari
8) Luggard = Lugga
9) Bordeaux = Bod'o
10) Awolowo = Awwalaho
11) Nnamdi = Namandi
12) Balat Hughes = Balatus
13) Taylor Woodrow = Tal'udu

Fita ta Biyu

Conductor = Kwandasta
Scrutiniser = Sakwaneza
Brake = Birki
Gear Box = Giyabos
Bumper = Bamba
Radiator = Lagireto
Carburator = Kafireto
Distributor = Disfuto
Coil = Kwayil
Valve = Bawul
Bearings = Boris
Rigs = Ringi
Plug = Fulogi
Crank Shaft = Karanshaf
Grand Overhaul = Garanbawul

Fita ta Uku

Ibadan = Badun
South West Nigeria = Kurmi
Port Harcourt = Fatakwal
Onitsha = Anacha
Africa = Afirka
America = Amurka
Turkey = Turkiyya
Istanbul = Santabul
Parsia = Fasha
Russia = Rasha
Germany = Jamus
Britain =  Birtaniya
Sierra Leone = Salo
Chad = Chadi
Cotonou = Kwatano
Port Lame = Fallomi
Yemen = Yamal
Israel = Isira'ila
China = Sin
Niamey = Yamai

Fita ta Hudu

Ford = Hodi
Bedford = Bilhodi
Mercedes = Marsandi
Peugeot = Fijo
Volkswagen = Besuwaja
Volkswagen Beetle = Ladi ba du wu
Fiat = Fet
Austin = Ostan-Ostan
Bus = Kiya-kiya (borrowed from Yoruba)
Station wagon = Dafa-duka
1973 Mercedes-Benz W114/W115 = Bagobira
1982 Toyota Corolla = Bana ba harka
Hatchback/coupe = ‘Yar kumbula
Long bus = Safa
Ten-wheel = Tangul
Mercedes 911 truck = Roka
Mercedes 1413-1414 truck = Bargazal
Mercedes 1312 (and similar sizes) truck = 'Yar Fakas
Max Diesel = 'Yar Rasha (Kirar Kurma)
Man Diesel (12-Wheeler) = Kwamanda
Truck with wooden body = Shorido
Hearse = Motar gawa
Towing van = Janwe
Tractor = Tantan
Trailer = Titiri
Pick-up van = A kori kura
Bulldozer = Katafila

DUBA WADANNAN:

Karanta Takaitaccen Tarihi akan Tushen Harshen Hausa da Al'ummar Hausawa

Ko Ka San Harufan Hausa Guda Nawa Ne?

Karanta Takaitaccen Tarihin Yaren Harshen Hausa


Bari na sauke wasu Karin Magana guda 35 da suke da Ma'anoni daban-daban, wadanda suke dauke da darussa, duk dai a cikin Yaren mu na Hausa wanda muke alfahari dashi, tunda yau ranar sa ce.

Kowa ya dauki wanda ya sani sannan ya fassara mana shi zuwa ainihin Ma'anar shi.

1. A rina, an saci zanen mahaukaciya.

2. A yi sha'ani, ɗanbirni ya cuci na ƙauye.

3. Abun dariya, kunkuru ya yi wa bushiya ƙafa.

4. Allah wadaran naka ya lalace, raƙumin dawa ya ga na gida.

5. Allah ya kawo baƙon da zai ci da ɗan gari.

6. An ce da ido wa ka raina? Ya ce wanda na ke gani yau da kullum.

7. Ana bikin duniya, ake na kiyama.
8. Ba cas, ba as.

9. Babban goro, sai magogin ƙarfe.

10. Bakin da Allah ya tsaga, ba zai hana shi abinci ba.

11. Ban ci nanin ba, nanin ba za ta ci ni ba.

12. Ban ga ta zama ba, an saci ɗan ɓarawo.

13. Ban sa a ka ba, in ji ɓarawon tagiya.

14. Baya ganin zalau, sai ya leƙa.

15. Cikina kwarkwaro, cikina tashiya.

16. Cil-da-cil, ganin annabin tsohuwa.

17. Da kamar wuya, gurguwa da auren nesa.

18. Da mai kama, ake ƙota.

19. Da sauran rina, a kaba.

20. Da wuya ta kashe ka, gwara/gwanda daɗi ya kashe.

21. Duk wanda ya samu rana, sai ya yi shanya.

22. Duniya rawar 'yanmata na gaba ya koma baya.

23. Fankam-fankam, bata kilishi.

24. Faɗan da ya fi ƙarfinka, mai da shi wasa.

25. Ga bikin zuwa, babu zanin daurawa.

26. Ga fili, ga mai doki.

27. Gaba kura, baya siyaki.

28. Gaba ta kai ni, gobarar titi.

29. Gani ga wane, ya ishi wane tsoron Allah.

30. Garaje, ga dami.

31. Guntun goro, ya fi babban dutse.

32. Gurin da ba ƙasa, nan ake gardamar kokawa.

33. Haka ma arziƙi ne, ka yi baƙo ya kashe ka.

34. Idan ba a yi sharar masallaci ba, a yi ta kasuwa.

35. Idan gemun ɗan'uwanka ya kama da wuta, shafawa naka ruwa.

Ranar Hausa ta Duniya



Yau 26 ga wata itace ranar Hausa ta duniya.
"Ina fatan matasa kada kuyi koyi da masu zuciya kamar Kunkuniya, domin suna nan a kowace kwarkwad'a da surkuki suna nufi kowa ya zam samma kal dasu, fatan mu shine qardajiya tayi ajalin su".

Wasu matasan a yau basu jin Hausa ko na sanqiyar bacci, koda yake dama a yau Hausa dodar sai Wanda yaci, ya sha, ya qoshi kuma yayi gyatsa da Hausa ne zai yi ta, acigaba da Koyon Hausa matasa a hankali a hankali wata ran Matankadi zai shiga Buta".

Ina masu yawan rubutu a Media? toh ga sako gare ku, daga Abdulhadi Isah Ibrahim.
Tunda ance yau ranar Hausa ce, ina so nayi mana gyara musamman mu masu yawan rubutu a Media, kura-kuran da ake yawan yi a rubutun Hausa a social media, na zabo guda 4 nayi magana akai.....

1. Duk inda zaka rubuta sunan gari, ko sunan mutum, dabba ko wuri ko mukami, ba'a rubuta farkon sa da small later, misali sai kaga mutum ya rubuta (abuja, kano, nigeria) kuskure ne hakan, duk wanda ya gani zai ce har yanzu da sauran ka, kuma mutane baza su rinka damuwa da posting din ka ba in kayi.

Sannan abu na biyu, majority din masu rubutu a social media suna da 'karancin sanin yanda ake rubutu da Hausa a tsarin da kowa zai gane, ta yanda suke hade kalmomin da ba'a hada su, misali sai kaga mutum ya rubuta (kasarmu) madadin ya bayar da space (Kasar mu), ko kuma kaga mutum ya rubuta (iyayensa) madadin (iyayen sa) da space.

Saboda kalmar (iyaye) kalma ce mai cin gashin kan ta, haka kalmar (sa) ko (shi) kalma ce ta daban, dan haka ba'a hada su, kamar a Turanci ne ka rubuta (myname is Abdullahi) is wrong, dole ka rabe (My name...) kar kazo rubutu ka rubuta (garinmu) sai dai (garin mu), sai mu gyara, haka kuma kuskure ne ka rubuta (rubutunsa) dole ka sanya space (rubutun sa) saboda kalmomi ne guda biyu, kwararrun masana Hausa basa hade su.

3. Sannan a rubutun Hausa akwai kalmomin da biyu ne amma ya halatta ka hade su a rubutun ka, misali (kazo) ko kuma (mune) babu laifi, saboda wani lokacin idan ka rabe zai bada wata ma'ana ta daban, misali (kayi?) ko da Turanci "You do?" kaga a Hausa kalmar (Ka) daban ce, kalmar (yi) daban ce, amma duk da haka masana rubutun Hausa sun ce ya halatta ka hade su, amma a Turanci kuskure ne ka rubuta (youdo?).

Akwai kalmomin da biyu ne amma ana iya hada su, a Hausa da Turanci, misali (tazo) "She came", kaga kalmar (ta) kalma ce ta daban, (zo) kalma ce ta daban, amma zaka iya hade su, ko kuma a turanci (myself) kaga kalmomi biyu ne (My) da (self) amma sai aka ce ya halatta hade su ka rubuta (myself), abu na 'karshe.

4. Sannan duk wurin da numfashi yake tsayawa a magana to ana saka masa Comma idan a rubutu ne, haka kuma duk wurin da zance ya cika ana sanya comma, kuskure ne ka rubuta (Hajiya ta dawo jiya har tazo da tsaraba) akwai comma (Hajiya ta dawo jiya, har tazo da tsaraba).

Wannan wasu ne daga cikin abubuwan da ya dace duk wanda zai rubutu da Hausa ya lura dasu kuma yayi aiki dasu, nagode.

Ranar Hausa, Hausa ba dabo ba dabara.

Tsinstiya, tsageranci, tsiya, tsagewa, tsaki, tsaga, tsakiya, tsiwa, tsunkunu, tsokaci, tsurku, tsaka, tsafta, tsamiya, tsada, tsaada, tsiri, tsira, tsirara, tsaigaitawa, tsawaitawa, tsanani, tsantseni, tsamewa, tsammani, tsohuwa, tsoho, tsotsa, tsanantawa, tsatstsafi, tsaro, tsaba, tsibi, tsabarage, tsimi, tsumuwa, tsire, Tsula,tsari,Tsiya,tsumi, Tsutsa, tsula, tsanya, tsando, tsinuwa, tsiya, Tsire, tsatso, tsimaya, Tsani, tsatsuba, tsimi, tsagwaro, Tsibiri, tsunke, tsuma, tsarguwa, tsangaya, Tsada, Tsafi, tsanewa.

Wasu daga cikin sunayen Hausawa na asali.
Garba, Mati, Lado, Tanko, jatau, Nomau, Shagari, Babangida, Asabe, Mudi, kande, kuluwa, Biba, Fatu, Audu, Dan tani, Larai, Talatu, Laraba, iya, Marka, Shatu, A'ille, Iro, Ubale, Uwani, Dan Asabe, Tukur, Ilu, Habulle, Tine, Assibi, Gambo, Jummai, Talle, Datti, Tani.


Ranar Hausa ta Duniya a shekarar da ta Gaba ta a dauki hotan.


DUBA WADANNAN:

Karanta Takaitaccen Tarihi akan Tushen Harshen Hausa da Al'ummar Hausawa

Ko Ka San Harufan Hausa Guda Nawa Ne?

Karanta Takaitaccen Tarihin Yaren Harshen Hausa


YAU CE RANAR HAUSA TA DUNIYA... KAWO MANA KARIN MAGANA GUDA DAYA DA HAUSA.

In ka ji mutum yana tsoro dare ba a ‘daure shi ya kwance ba.

Albasa ba ta halin ‘kasa, da ba ta yi yaji ba.
Maraya ba ya shakkar mutuwar uwar wani.

Ba’kon munafuki ba na mutum ‘daya ba ne
An san biri yana da wuya a kan ‘daure shi a gindi.

Ma’kiyinka ba shi yabonka ko da ka kama damisa ka ba shi.

Gudu da waiwaya shi ya kawo mugun zato.
Wanda za a kashe don an karairaya shi ba kome

An ce da akuya Sarkin Fawa ya mutu, ta ce, “Oho, ya mutu da wu’kar yanka ne ?”

Barawon da ba a gani ba sunansa mamman.

Abin da wancan ya ce shi na ce, kirarin mai tsoro.

Barawon kakaki, ba shi da ikon ya busa shi.
Wai an ce da jaki falke zai shiga aljanna, ya ce “Im ba ni nan kusa ba ?

Ina zan zauna, matsegunci ya je kasuwa.

Izza na Kano, sarauta na Sakkwato, ya’ki na Zariya, karin magana na Bauchi

Kowa ya hana ka ‘dakin kwana, da safe sai ya ganka.

Gurgu yana gani a kan sari sanda a buge shi.

KOWA YA KAWO NASA GUDA DAYA... 

DOMIN JIN DADIJ RANAR HAUSAWA TA DUNIYA.

SHARHIN RABI'U BIYORA

Kishingide nake a shigifa bisa karauni, ina nazarin wannan sarari da muke rayuwa cikinsa, tsam na mike na fito na haye laulawa jikina sanye da riga Kwakwata da wando tsala, na saka kafafuna cikin takalmi fade, unguwar gangare na nufa gidan , Malam Alto wamzami don ya sassabe mun sumar dana tara, bayan nayi sallama Alto Wanzami ya fito ratyae da Zabira a kafadarsa.

Bayan ya zauna sai ya fito da kayayyakin aikin nasa, Koshiya ya fara daukowa, sai yar tsaga da Aska, Mawashi da isga sai kuma kaho, daganan ya sassabemun suma kamar yadda na bukata....

TAMBAYA GAMU HAUSAWA DA MASU AMFANI DA YAREN HAUSA....

A wannan rana da ake bukin Harshen Hausa a Duniya, ya kamata musan asalin sunayen wadannan abubuwan....

Mota
Jirgin Sama
Babur
Keke
Bokiti
Television
Radio
Fanka/fans
Titin Mota
Telephone

Zaka iya karawa da sunayen wasu abubuwan daka sani nasu na asalin Hausa....

Tattaunawa cikin shakatawa don taya juna murnar ranar Hausa ta Duniya......

Ranar Hausa ta Duniya



SHI BA BAHAUSHE BA KUMA SHI BA BATURE BA, HAKA KAWAI KA ARI ABIN DA BA NAKA BA KACE DOLE NE SAI YA ZAMA NAKA? SUMA FA MASU WANNAN YAREN (ENGLISH) SUN MAYAR DA HANKALI AKAN GINA YAREN NASU WANDA A YAU HAR YAKAI MATSAYIN DA YAKE KAI.

ME NE NE YASA KAI MA BAZAKA BAYAR DA GUDUNMAWAR KA WAJEN CI GABAN HARSHEN KA BA?

AKWAI HANYOYI DA YAWA DA ZAKA IYA BAYAR DA GUDUNMAWAR KA, IDAN KANA DA SHA'AWAR HARKAR RUBUCE-RUBUCE KAYI AMFANI DA DANDALIN SADA ZUMUNCI DA MUSAYAN RA'AYI (FACEBOOK) KO KUMA (TWITTER, WHATSAPP, YOUTUBE, INSTAGRAM DA SAURAN SU) IDAN KANA DA DAMA ZAKA IYA TAIMAKAWA WAJEN BUDE WEBSITE/BLOG DOMIN BAYAR DA TAKA GUDUNMAWAR.

SUMA FA YAREN NAN (ENGLISH) DA KAKE GANIN KOMAI AKE NEMA A NET ZAKA SAMU MATUKAR DA ENGLISH KA BINCIKA BASU NEMI TAIMAKON KOWA BA WAJEN GINA SHI A NET.

ME YASA KAI MA BAZAKA YI AMFANI DA ILIMI DA BASIRAR D ALLAH (SWT) YA BAKA WAJEN GANIN YAREN NAMU YAKAI WANI MATAKI ANAN GABA BA? 

KOWANNEN MU YANA DA IRIN BAIWAR DA ALLAH YAYI MASA TA WANI BATAYI KAMA DA TA WANI BA, HAKA ZALIKA ABIN DA WANI ZAI YI WANI KO TIRILIYAN AKA BASHI ACE YAYI BAZAI IYA BA (KAMAR MISALIN MACE MAI CIKI CE) NAMIJI BAZAI IYA HAIHUWA BA, SABODA ALLAH BAIYI MASA MAHAIFAR DA ZAI IYA HAIHUWA BA.

TO HAKA MISALIN BAIWA TAKE KOWA DA KALAR TASHI BAIWAR.

DAN UWA NA, AKWAI HANYOYI DA YAWA DA ZAKA IYA TAIMAKAWA WAJEN GANIN AN GINA YAREN HAUSA A WANNAN KAFA TA ZAMANI WANDA A HALIN YANZU KUSAN ZAMU IYA CEWA , ANFI MAYAR DA HANKALI WAJEN BINCIKE DA KARANCE-KARANCE A WANNAN KAFA (YANAR GIZO) FIYE DA YADDA AKE BINCIKE A LITTATTAFAI KO KUMA DAKIN KARATU.

INA DA BURI DA FATA NA GANIN HARSHEN HAUSA YA WANZU A DUK SASSAN DUNIYA BA YANKIN AFRICA KAWAI BA , DUNIYA GABA DAYA NAKE DA BURIN GANIN HARSHEN YA SAMU SHIGA KOWANNE LUNGU DA SAKO INSHA ALLAH.

DAFATAN ZA'AYI MIN UZIRI NA RASHIN AIKO DA SAKO DA KUMA FARIN CIKI NA ZAGAYOWAR RANAR HAUSA TA DUNIYA, HAKAN YA FARU NE SABODA WANI DALILI.

ALLAH YA SA MU DA CE AMIN.


Rayuwa!

‘Salamu alaikum ko mutan gidan na ciki?’

Sallama ce daga waje.

‘Wa’alaikumus salam,’ yaro ne dan shekara 8 ya amsa mata.

Ta shigo cikin falon, ta yi tsaye da ta ga yaro ba ko riga yana kallon ta.

‘A’aaaha, ba kowa ne a cikin gidan, sai kai?’

‘Akwai kowa mana, ko ni ba kowa ba ne halan?’ Ya fada cikin yarinta.

‘Yi hakuri, ni ba baka na ce ka fada mini ba, daga tambaya!

‘Ai, akwai magana fara ne da kike batun baka? Abar dai zancen, duk sun fita, sun bar ni tsaron gida ne.’

‘Don Allah rufe man baki da yawan surutu, ta yaya kamar ka zai tsare gida in ba hauka ba.’

‘Hauka? Ta yaya yaro kamana zai yi hauka, cewa nake yi sai manya ko  ma’aikatan gwamnati ke yin hauka?’

Cikin mamaki ta ce da shi, ‘yaya kake ce da ma’akaitan gwamnati mahaukata?’

‘Haka na ji Baba na fada. Yana cewa ai mai aikin gwamnati shi ne mahaukaci yau a Nijeriya. Domin kuwa ba yadda za a yi idan ba hauka ba, mutum ya amshi albashin dubu talatin a wata, alhali shi yana bukatar dubu sittin ya ciyar da iyalinsa, ya yi mirsisi ya ce Allah ya kyauta,’ in ji Baba.

‘Ban gane ba, me Babanka ke nufi?’

‘Bari na yi maki Gwari-Gwari. Cewa yake yi hauka ne ka amshi albashin da ka san ba zai ci da iyalinka ba, a kuma zauna lafiya!’

‘Ta yaya mutum zai zama mai hankali idan da kai ne za ka yi bayanin da kyau,’ ta fada, ta kuma nemi wuri ta rashe.

‘Ai da in zama mahaukaci, gara in zama barawo!’ Ya ce da ita.

‘Haba kai ko, ta yaya za ka ce haka, barawo ai ba mutum ba ne.’

‘Shi ko mahaukaci fa, mutum ne? Ya tambaye ta.

‘Mutum ne mana, me kake nufi?’

‘Wallahi ni dai ban amsar abin da na san bai ciyar da iyalina domin in bauta wa gwamnati.’

‘Kai kuwa dana ai ba bauta ba ce, ba ka ganin cewa abin da ya dace a biya ka ke nan?’

‘Rabin hakkina a wata shi ne biya na? To ko ke ma kin soma irin nasu haukan ne?’

‘Ashe ba ka da kunya, ni kake ce wa mahaukaciya?’ Ta fada cikin kakkausar murya.

‘Allah ya huci zuciyarki, ba haka nake nufi ba. Amma don Allah ki fada mani gaskiya ke ma ma’aikaciyar gwamnati ce ko?’

‘Ehhh, ita ce, sai me?’ Ta fada a fusace.

‘A’a, ba komi’, ya fada cikin guna-guni.

‘Don Allah ka bayyana mini man, ba zan sake yin fushi da kai ba.’

‘To shi ke nan. Na san dai kin zo wurin Mama ne ki roki sauran garin kwaki, to mu ma Baba ya jefa tiyar garin da ta rage cikin wata bakar leda, ya sa kirtani ya daure, ya dauki bakar ledar ya sa cikin wani kwanon sha, ya rufe, ya sa bisa silin din dakinsa ya boye!’

‘Saboda me?’ Ta ce da shi cikin mamaki.

‘Ai haka Baba yake yi duk tsakiyar wata, yana cewa ba a kara shan gari sai wata ya kusa karewa’.

‘Haba sai ka ce mahaukaci?’

‘Mahaukaci!’ Ya ce da ita.

‘Me ka ce?’

‘Na ce mahaukaci!’

‘Baban naka kake ce da shi mahaukaci?’

‘Yo ba ke kika ce in ce ba!’

‘To mu manta da wannan batun, ni ba garin kwaki na zo bida ba, dama ina son ku ‘yan mani ruwa ne, ba mu da ko tarfi a gidan, tun jiya da dare.’

‘Ai abin da nake gaya maki ke nan tun dazu. Ba kowa gidan, yayyena sun tafi bakin kasuwa inda famfon ya fashe, su gani ko za su kwakulo mana jarka guda, tun dazu ba su dawo ba.’

‘Ku ma naku famfon ya lalace ne?’ Ta ce da shi.

‘Ko alama, Mama cewa take a kullum, famfon namu gara babu da shi, domin kuwa rabon da ruwa ya digo daga jikin famfon tun kafin a yi yayen ‘Yar lele, yau kusan wata shida ke nan.’

‘Ita Babar taku ina ta tafi?’

‘Ta leka wajen masu nikan masara ne ta ga me ya faru. Domin tun da safe ta aiki wana Kabir kai nika har yanzu ba su dawo ba?’

‘Ko ka san abin da ya hana Kabir dawowa da nikan?’

‘Na sani mana. Na gaya wa Mama kada ma ta damu kan ta, ba zai sami nikan ba sai da magariba, ta ki saurare na, ni kuma na kyale ta.’

‘Amma kai ko, ai dole ta bi shi saboda a sami garin da za a yi muku tuwon dare.’

‘Lallai haka ne. Amma ai abin da ba ta sani ba shi ne NEPA ba za ta kawo wuta ba sai da kusan magariba, a lokacin kuma Mushirikat ta tafi coci, ba kuma za su daina wake-waken da raye – rayen ba sai wajen takwas na dare. To ina amfanin bin yaya da ta yi?’

‘Ka sani ko tana son su kai nikan wajen injin ruwa ne!’

‘Uhum, ai injin ruwa daya ne kurum a unguwar. Kuma tun jiya na ji Iya Tawakaltu tana ce da Tawa, ta gaya wa mahaifinsu in ya dawo daga gareji ta tafi dauko injin din da ta kai gyara can kara, ba kuma za ta dawo ba sai gobe da safe.’

‘Kai ko wai yaya aka yi ka yi wayo haka?’

‘Ba wayo ba ne, rayuwa ce!’

‘Ban gane ba, wata makaranta ce kake zuwa ta rayuwa?’

Ya yi murmushi, ‘ai ko makarantar ma ban shiga ba!’

‘Me ya hana?’

‘Baba ya hana!’

‘Don Allah ka daina yi wa iyayenka karya, me zai hana su sa ka makaranta kai kuwa?’

‘Da wane kudin za su sa ni? Imam, babban wana na jami’a. Maijidda, mai bi masa na kwaleji. Isa da ke biye da ita, na firamare.

A kowane zangon karatu Baba na bukatar sama da Naira dubu 90 ya biya musu kudin makaranta. Saboda haka ya ce ni in dan huta kafin wani lokaci. Shekara biyu ke nan ina hutawa.’

‘Haba yaro ya za a yi a kasa biya maka kudin makaranta saboda ‘yan uwanka na karatu?’

‘Hala dai ba ki yi makaranta ba ne?’

‘Me ya sa ka ce haka?’

‘Idan aka tara dubu 30 sau uku, nawa ke nan?’

‘Dubu 90!’ Ta ce da shi.

‘A kowane zangon karatu wata nawa ne, in ce uku?’ Bai jira ta amsa ba, ya ci gaba, ‘kin manta cewa albashin Baba dubu 30 ne kowane wata?’

‘To shi Baban naka bai iya yin komi ya samu kudin da zai cikasa ya sa ka makaranta?’

‘Yana iyawa!’

‘To me ya hana shi?’

‘Ban sani ba!’

‘Haba, yaro mai wayo kamar ka zai ce bai sani?

Don Allah gaya man hanyar da zai bi ya taimake ku.’

‘Hanya daya ce,’ ya fada da ajiyar zuciya.
‘Wace ce?’

‘Ya yi sata.’

Ta yi zambur ta mike tsaye. ‘Sata, haba dana, sata fa ka ce!’

Yana mamaki, ya ce da ita, ‘to laifi ne yin satar?’

‘Laifi ne mana!’

‘In laifi ne shi ne na yi ta gani a talbijin an nuno buhunan Gana-Mus-Go a majalisar Dattijai da ta Wakilai ana cewa daga ofishin Shugaban kasa ne, wai an aiko musu da cin hanci?’

Ta yi shiru.

‘Me ya same ki, na ji kin yi shiru?’

Ba ta amsa ba!

‘Kukan me kike, cinnaka ne ya cije ki, na ga kina zubar da hawaye?’

Ta sa hannu ta share hawaye da habar zanenta, ta ce ‘ba komi, kana ba ni tausayi ne kurum.’

‘In don ni ne kada ma ki damu kan ki, ba abin da zai same ni, domin Babana ya ce mu yara ba abin da zai same mu daga mahaukaciyar gwamnatin kasar nan.’

‘Wai wa ke koya maka irin wadannan miyagun kalamai haka?’

‘Babana!’

‘Shi ke koya maka zagi da bakaken maganganu irin wadannan?’

‘Ehh mana. Na ce maki ni ba na ko zuwa makaranta balle ki ce can na koyo. Rayuwa ce kurum! Idan ma kika ji yadda Baba ke bayani, ai ni ba komi nake cewa ba. Jiya na ji yana cewa ai shi bai ki duniyar ta watse ba. Yana cewa in ma an ga dama a yi tashin kiyama, yau ko gobe. Haka kuma na ji yana ta fadar bai taba ganin shegun shugabanni irin namu ba. Yana karawa da cewa bai taba ganin mugaye, macuta, mamugunta, azzalumai ba irin masu kudinmu. Da na ce da shi Baba ta yaya kake neman a yi tashin kiyama a halin yanzu, me ya yi zafi….’

Nan take ta katse masa hanzari ta ce da shi, ‘kai amma ana cikin matsalaloli a kasar nan.’

‘A’a, ba a cikin matsaloli, mu tamu matsala daya ce kurum!’ Ya ce da ita!

‘Wace ce?’

‘Yunwa!’

‘Shi ke nan?’

‘To kila talauci!’

‘Talauci?’ Ta tambaye shi.

‘Rashin boza mana, ko ba ki san wannan ba? Fatara. Rashin naira!

Ni ban san wannan ba!’

‘Karya kike yi wallahi?’

‘Kai dan abin uwar nan…. ni kake karyatawa!’

‘Ni ban karyata ki ba. Ba kuma ni na fada ba, Baba ne ya ce duk wanda ya ce bai san talauci a kasar nan ba, to mahaukaci ne ko kuma makaryaci?’

‘Me ya sa Babanka ke bayyana maka wadannan abubuwa marasa dadin ji da kuma ban takaici?’

‘Cewa yake saboda idan na girma ba zan hadu da matsaloli a rayuwa ba.’

‘Me zai faru gare ka in ka girma? Me yake hange?’

‘Matsaloli!’

‘To ai yana nan raye zai iya taimakon ka ko!

‘Ya ce kafin ya mutu zan san hanyoyin magance matsalolin rayuwa.’

‘Me zai sa ya mutu?’

‘Matsalolin rayuwa mana!’ Fashi da makami. Sace-sacen mutane. Karuwanci da zina da madigo. Kashe mutane da yankar kai da kuma hadama da babakere. Kai ga su nan bilahaddin…. 

Ta yi ajiyar zuciya, sa’annan ya ji tana cewa,‘ Allah ya isa, Allah ya tsine. Allah wadarai. Allah ka fatattaka wadannan musu bata mana rayuwa da ta yara irin wannan. Allah ka sa su shiga cikin kunci da muke ciki, ko ma nasu ya fi haka. Allah, idan masu gyaruwa ne ka gyara su, idan ko ba masu gyaruwa ba ne, Allah ka kashe su, ka kashe su na ce!’

‘Me ya sa kike irin wadannan miyagun maganganu ke ma, ko kina zuwa makarantarmu ne?’ Ya ce da ita.

‘Wace?’

‘Ta rayuwa!’

Ba ta amsa masa ba.

‘Shegu!’ Ta fada cikin kakkausar murya.
Ya fashe dariya, ‘ke ma kin soma magana irin ta Baba.’

‘Allah ya isa! Ai ni wallahi da zan ga inda aka ajiye kahon nan, wallahi da na dauko shi na hura shi yanzu-yanzu, kowa ya huta. Takadarun azzalumai kawai!’

Ta mike za ta wuce, ta ce da shi, ‘ka gaya wa Mamanka cewa na leko, idan kuma ta rage tuwon jiya ta aiko ka da shi, domin yaran gidana tun safe rabon su da su jefa wani abu a uwar hanjinsu.

‘To za ta ji.’ Ta fice. Shi kuma ya yi zaune zugudum, yana magana a hankali, ‘ ka ji maras hankali ko. To ta aiko maki da sauran tuwo, mu kuma mu ci me?’


MALAM BAHAUSHE A JIYA DA YAU!!!

Bahaushen jiya.

Yana da  Riqo da addininsa
Yana da tsarin shugabancin sa mai kyau na sarakunan gargajiya.

Yana da matukar riqo da Harshensa da Al'adunsa na usuli.

Bahaushen jiya baiyarda da zaman banza ba da mutuwar zuciya ba shiyasa zaka magidanci yana Noma ko kasuwanci, a gidansa kuma zaka samu akwai garke na awaki ana kiwo, matansa kuma zakaga akwai aikin dasuke agida na dogaro dakansu irinsu niqa, chasa d.s
Bahaushen jiya keda matuka wajen taimakon junansa misali idan andawo daga wajen sana'a za afito da abinci daga gida ahadu guri daya aci, idan wani yaga dan wani yayi laifi to zai hukunta shi kuma axo har gida ai masa godiya.

Ranar Hausa ta Duniya

Bahushen yau.

I'm sorry to say to the extend bahaushen yanxu ya gurbace tako ina compare to asalin bahushen jiya. Hujja ta ita ce,
Bahaushen yau ya zubarda yawancin al'adaunsa kyawawa yana ganinsu a matsayin qauyenci.

Bahaushen yau bai dauki addininsa da muhimmanci ba a aikace sai a baki kawai.
Hassada, kyashi, mugunta, son kai da zunzurutun jahilci ya samu babban muhali a zukatan hausawan yau sai wadanda Allah ya tsare kawai.

Mafita ga bahaushen yau.

1. Ni bahaushe in yarda banda Yaren dayafi Hausa.

2. Yin watsi da bakin al'adu na aro da dabbaka namu na usul.

3. Bibiyar tarihin magabata da koyi da yanda sukai rayuwansu.

4. Yin cikakken ilimin Addini dakuma aiwatar da karatun a aikace.

Yau take Ranar Hausa ta duniya.


RANAR HAUSA,

Aci ba'a siyar ba kaza tafi doki

Ranar hausa

Duk daya ne akace da makafi sunyi dare

Ranar Hausa

Duk tsawonka kujerar gwamna tafi ka tsayi

Ranar hausa

Abinda kamar wuya wai raba talaka da buhari

Ranar hausa

cin moriyar jaki nisan kwana,

Ranar Hausa

Yau da gobe kesa a mari suruka

Ranar Hausa

kuturu da kudinsa alkaki saina kasan kwano

Ranar Hausa

A bari ya huce shike kawo rabon wani 

Ranar Hausa

me rabon ganin badi ko ana dakawa a turmi sai ya gani

Ranar Hausa

Abin rabo ne kuturu ya kama tarwada

Ranar hausa

Alhamdulillah!!! a cikin waɗannan sharhin da MURYAR HAUSA24 ta kawo muku daga wasu mabiyan mu , sharhin wane ne ya fi birge Ka/Ki kuma yafi daukar hankalin Ka/Ki?

Zaku iya yin sharhi a ƙasan wannan maƙala ko kuma ku turo mana da sharhin ku a akwatin aika saƙo na imel a muryarhausa24@gmail.com za mu yi farin ciki da samun saƙon Ka/Ki Mungode!

Muryar Hausa24 muna yiwa dukkan al'ummar Hausa Barka da Wannan rana dafatan za'asha shagulgulan bikin wannan rana lafiya Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode