Friday 27 December 2019

KARANTA SUNNONI GUDA 11 A RANAR JUMA'A DA AKA MANTA DA SU

Tura Wannan Zuwa
1. Yin wankan juma'a da sanya turare mai dadin kamshi a ranar juma'a.

Wanda yayi wanka juma'a a ranar juma'a sannan ya sanya Turare ya shafa mai sannan ya taho masallacin juma'a, kuma bai ketara tsakanin mutane biyu sannan ya yi shiru lokacin da liman yake Huduba, an gafarta masa zunubansa tsakanin juma'a zuwa wata juma'ar.

Yayin Ruku'u

Marubuci: Bashir M. Sulaiman

ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ 883

2. Yin shiru lokacin Huɗuba da kuma kama daga ƙetara mutane idan kazo masallacin juma'a.

Kuma bai ƙetara tsakanin mutane biyu sannan ya yi shiru lokacin da liman yake Huɗuba, an gafarta masa zunubansa tsakanin juma'a zuwa wata juma'ar.

ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ 888

3. Fita zuwa masallacin juma'a da wuri kamar daga karfe 11:00 ko 10:30am.

Malamai suna cewa "Sammakon ranar Juma'a yana farawa daga fitowa rana zuwa sa'a ta biyar lokacin zaman liman akan Minbari."

Manzon Allah (S.A.W)

Wanda yazo a sa'ar farko yana da ladar wanda ya yi sadaka da rami,a sa'a ta biyu kamar mai sadaka da saniya,sa'a ta uku kamar sadakar rago, sa'a ta huɗu kamar sadaka da kaza, sa'a ta biyar kamar mai sadaka da kwai, idan liman ya hau mimbari sai a daina ruwatawa.


ﻣﺴﻠﻢ ‏1403

4. Yin barci rana bayan sallar juma'a.

Sahal bin Saad ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ yana cewa" Mu sahabban Manzon Allah (S.A.W) mun kasance muna kwanciya barcin rana a ranar juma'a bayan mun dawo daga sallar juma'a."

ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ‏( 5807 )

Yayin Huɗuba

Wannan ya nuna kenan suna yin sallar juma'ar ne da wuri kuma suna fita masallacin juma'a ne da wuri.

5. Mai Huɗuba zai yi nuni da ɗan yatsarsa manuniya a lokacin da yake addu'a acikin Huɗuba.

Manzon Allah (S.A.W) baya karawa akan yin nuni da ɗan yatsarsa a lokacin da yake yin addu'a a cikin Huɗuba.

 ﻣﺴﻠﻢ ‏( 874 ‏) ﻭﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ‏( 515 ‏) ﺍﺣﻤﺪ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺴﻨﺪ ‏( 17219/17221 / 17224/18299 )

Kwalliya ta Musamman Domin Ranar Juma'a

6. Baya cikin SUNNAH ɗaga hannu a lokacin yin addu'a a cikin Huɗuba ga liman ko mamu.

ﺍﻟﻌﻼﻣﺔ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ

Yana cewa "Ɗaga hannu dan yin addu'a lokacin da liman yake Huɗuba baya cikin SUNNAH".

ﻓﺘﺎﻭﻱ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻹﺳﻼﻡ ‏( ﺹ 393 )

7. Fuskantar liman da kallonsa lokacin da yake Huɗuba.

ﺍﻟﻌﻼﻣﺔ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ

Yana cewa "Fuskantar liman da kallon sa lokacin da yake Huɗuba yana cikin SUNNAR da aka manta da ita".

ﺍﻟﺴﻠﺴﻠﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ 5/110

8. Canza wajan zama ko canza yayin zama ga wanda yake gyangyadi a ranar juma'a.

Manzon Allah (S.A.W) yana cewa "Idan ɗayan ku yana gyangyaɗi a ranar juma'a to ya chanza wajan zaman sa".

ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ ‏( 1119 ‏) ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ‏( 526 ‏) ﺍﺑﻦ ﺧﺰﻳﻤﺔ‏( 1819 )

Hikima akan haka shine motsin da zaka yi na canza zama ko gurin zama zai yanke maka gyangyadi dan ka saurari Huɗuba da addu'ar liman lokacin Huɗuba.

Yayin Sujada

9. Yin sallar nafila bayan juma'a.

Sunnane ga wanda ya halarci sallar juma'a yayi nafila raka'a biyu bayan ya koma gida ko raka'a huɗu a masallaci.

ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ‏( 937 ‏) ﻣﺴﻠﻢ ‏( 882 )

ﺍﻟﻌﻼﻣﺔ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ

Yana cewa: Malamin mu ibn Taimiya yana cewa"Wanda zai yi nafila bayan sallar juma'a idan masallacin zai yi sai yayi raka'a huɗu, idan kuma sai ya koma gida ne sai yayi raka'a biyu kaɗai, wannan shi ne abin da ya tabbata a SUNNAH.

ﺍﻟﺰﺍﺩ ‏( 1/440 )

10. Yawaita salati ga Manzon Allah SAW a daren Juma'a da yinin juma'a.

ﻣﺴﻠﻢ ‏( 881 )

11. Yawaita addu'a bayan sallar la'asar ta ranar Juma'a zuwa faɗuwar rana dan dacewa da lokacin amsa addu'a ranar Juma'a.

ﺍﻟﺰﺍﺩ ‏( 1/440 )

Karanta Suratul Kahf Ranar Juma'a

A DUK RANAR JUMA'A 

Kada muyi ƙasa a gwuiwa wajen yawaita yin Salati ga Manzon Allah (S.A.W)) da Iyalan gidan sa, domin yin Salati ga Manzon Allah(S.A.W.W) da Iyalan gidansa (as) yana nufin:

1. Amsa umarni ne na Allah maɗaukakin Sarki.

2. Samar da haske ne ga kabarin mai yinsa bayan ya mutu.

3. Zikiri ne mafi girma da ɗaukaka.

4. Sinadari ne na rusa zunubai da share lefuka.

5. Ɗaukaka ce ga mai yawaita yin sa.

6. Samun kusanci ne zuwa ga Allah.

7. Bayyanar da Soyayya ne ga Manzon Allah da Iyalan gidansa (A.S).

8. Yinsa a farkon kowanne aikin lada, sirri ne na karɓuwar wannan aikin.

9. Tsarki ne ga ruhi da gangar jikin mai yinsa.

10. Ibada ce karɓabbiya wacce ba a maidowa da wanda yayi.

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA KADAN DAGA CIKIN FALALAR RANAR JUMA'A

KARANTA MANYAN FARILLAN SALLAH GUDA 14

KARANTA MANYAN LADUBBA AKAN MUSULMI GUDA 10 A RANAR JUMA'A

Yiwa Annabi da Iyalan gidansa Salati, sirrin haske ne a Duniya da lahira, dawwama a cikin hakan kuwa yana nufi dawwama ne a cikin lada da samun yardar Allah (S.W.T)

"اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّد وَآل مُحَمَّد".

Allah ne mafi sani.

Allah ka bamu ikon koyi da Manzon Allah (S.A.W) a cikin dukkan ibadar mu da rayuwar Mu baki ɗaya Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode





TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user