Thursday 20 February 2020

Kowanne Mutum Yana da Abokai Guda Uku a Rayuwarsa da Bayan Mutuwarsa

Tura Wannan Zuwa
1. Abokin da yake tare da kai har numfashinka tun daga ranar da ALLAH ya nufi halittarka har zuwa mutuwarka: shine Arzikinka kuma zai amfaneka har bayan mutuwarka idan kayi amfani dashi ta kyakkyawar hanya musamman Sadaƙa mai gudana.

Ka Mu'amalanci Mutane da Kyakkyawar Manufa..

Marubuciya: Faridah Bintu Salis 

2. Abokin da yake tare da kai a yayin rayuwarka da lokacin da ka mutu da bayan mutuwarka: shine ilimin da ka gabatar a lokacin rayuwarka.

3. Abokin da yake tare da kai har zuwa ƙabarinka inda aka bizne ka da kuma bayan mutuwarka idan ya kasance nagartacce: shine Ɗan ka.

Hadith ya tabbata cewa Annabi (ﷺ) Yace: “Idan bawa ya mutu dukkan ayyukansa sun yanke sai dai abubuwa guda uku:

1. Sadaƙa mai gudana.

2. Da ilimin da ya amfanar.

3. Ko kuma ɗan da ya bari salihi wanda yake masa addu'a.” [Muslim ne ya ruwaito]

Wannan hadisi yana nuna mana Sadaƙa mai gudanarwa ita ce wanda ka taimakawa addininka dashi misalai: ka haƙa rijiya bayin ALLAH suna amfana da ruwan da ke fita daga gareta, ko kuma ka gina masallatai bayin ALLAH suna shiga suna gabatar da ibada, ko kuma ka gina wata makaranta ta addini, ko kuma ka taimakawa marayu, ko kuma kayi copy na wasu littafan addini kaɗan daga ciki ne waɗannan duk sadaƙa ce mai gudana.

Wannan hadisi yana nuna mana cewa idan ka tsaya ka karantar da al'umma wani ilimi da ALLAH ya hore maka shi, shima ka taimakawa addininka.

Wannan hadisin yana tabbatar da tsayawa ka bawa ɗanka Tarbiya Nagari wanda har zai samu ikon yi maka addu'a bayan baka raye wannan shima ka taimakawa kanka da kuma addininka domin idan ya zama nagari ana sa ran zai amfani al'ummah.

MAKALOLI MASU ALAKA:

Karanta Irin Abokin da Yakamata Kayi Rayuwar Ka da Shi

Abokai Iri Uku Ne a Duk Fadin Duniya

Shin Ko Abokina Zai Iya Canza Min Halayena Bansani Ba?

Waɗannan abubuwa duk ka taimakawa addininka sannan kuma ka taimakawa kanka tunda har bayan ka bar duniya za'a ringa rubuta maka ladan, kuma ladan zai ringa riskar ka.

ALLAH Yasa mu dace Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin daɗin ku.

MURYAR HAUSA24 Kamfani ne mai zaman kansa domin bunƙasa harshen Hausa a duk sassan Duniya.

Burin Shafin MURYAR HAUSA24 zama babban shafi a Duniya da zai samu amincewar al'umma don Ilimantarwa.

MURYAR HAUSA24  Shafi ne da yake ƙunshe da abubuwan da suke da alaƙa da harshen Hausa da Al'ummar Hausa, sannan shafi ne da yake tafiya da Zamani da kuma tsarin Gargajiya na Iyaye da Kakanni, don Ilimantarwa da Kuma Faɗakarwa.

MURYAR HAUSA24  Shafi ne a Yanar Gizo da yake gabatar da shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla, cikin sa'o'i ashirin da huɗu Dare da Rana (24 Hours) ba tareda kakkautawa ba.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a faɗin Duniya.


MURYAR HAUSA24 Mun ƙudiri aniyar bunƙasa harshen Hausa  a sassan Duniya batare da nuna ƙabilanci ba, ta hanyar rubuce-rubuce da kuma sauraro (Audio) gami da kallan hoto mai motsi (Video).

Zaku iya aiko mana da Labari, Faɗakarwa, Tunatarwa, Ilimantarwa, Nishaɗantarwa, Wa'azartarwa da sauran su ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan adireshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user