Showing posts sorted by relevance for query Bashir M. Sulaiman. Sort by date Show all posts
Showing posts sorted by relevance for query Bashir M. Sulaiman. Sort by date Show all posts

Friday, 6 October 2017

Tsantsar Kalaman Soyayya

Tsantsar Kalaman Soyayya

A= A gaskiya ina sonki.

B= Babban burina in aure ki

C= Cutar sonki ba ta da magani.

D= Daddaɗan lafazin ki ke sakani farin ciki.

E= Ebo zuman sonki shayar dani mai sona.

F= Fitacciyar farar fuskarki ke haskaka
zuciyata.

G= Gaggawa nake domin na sallama zuciyata
agareki.

H= Hanzartarki ita ke durmuyani cikin kogin
sonki.

I= In gantaccen hanka linki shi yake karamun
sonki autar mata.

J= Jinjina agareki sarauniyar matan Arewa.

K= Ko kinsan Allah yayi miki ni ima da
zazzakar muyar tamkar farar Algaita.

L= Lamuni nake nema agareki danna....lalata
rayuwar makiyanki.

M= Masoyin ki shiya cacan ta ya mallaki
mulkin rayuwarki.

N= Nasan bakida shakka ko tantama akan
sonda nake miki.

O= Ohh rayuwarmu daya kuma jininmu daya.

P= Photon ki abun sha'awa ne agareni.

Q= Qarin sha'awa ta ace na mallake ki.

R= Rayuwata zatayi rauni idan narasaki.

S= Sassan jikina sai raunana sukeyi saboda
rashin ganinki.

T= Taka warki lafiya ma'abuciyar hankali d
tunani.

U= Uwar gida mai ran qarfe.

V= Vurina in aureki.

W= Wayyo yau nafada kogin sonki

X= Xan kasance cikin matsala idan narasaki.

Y= Ya cikakken zoben azurfar Zinaren
zuciyata.

Z= Zan so ki tashi ki yi nafiloli domin ki
Rokan mana Allah ya ƙara barinmu tare cikin kauna

Source: Bashir M. Sulaiman

Sunday, 1 October 2017

KARANTA WASU DAGA CIKIN HALAYEN 'YAN JAMI'A

KARANTA WASU DAGA CIKIN HALAYEN 'YAN JAMI'A

Wanka ba kokari sai yan LAW DEPT
son ayi turanci ba a iyaba sai yan HISTORY DEPT.

Rashin iya magana sai yan BIOCHEM DEPT
Mako sai yan ECONOMIC DEPT.

Rashin kunya sai yan BIOLOGY DEPT.

Iya turanci sai yan PUBLIC ADMN.

Kazanta sai yan CHEMISTRY DEPT.

Kaga mutum ya bushe ya rame sai yan MATH DEPT.

Iya wanka sai yan MEDICINE DEPT.

Tsoron attendance da assignment sai yan
INDUSTRIAL CHEMISTRY.

Surutu a thearter sai 'yan PHYSICS DEPT.

Gemun rashin kunya sai 'yan ISLAMIC DEPT.

Aje lecture a dawo ka tambayi mutum abinda aka
koyamasa yakasa baka amsa sai yan COMPUTERS SCIENCE.

Kaga an dawo lecture ana tafiya ana tada kura
kamar shanu sai yan EDUCATION.

Kullum ana gaban notice board sai yan
HUMANITIES.

Son ayi gaddama sai yan ARABIC DEPT.

Gararamba sai yan SOCIOLOGY.

Yawan bacci a hostel sai yan BLIS DEPT.

fadin gaskiya sai yan GEOGRAPHY.

Raki akan wahalar course sai 'yan HAUSA.

Ko nayi karya Friends??????

Mun Wallafa din Ne kawai Saboda Nishadi

Source: Bashir M. Sulaiman

Sunday, 8 March 2020

Wai Muna Ina aka Raba Wannan Arzikin Ne?

Wai Muna Ina aka Raba Wannan Arzikin Ne?

Wani mutum ya tsaya yana kallon gidaje ƙerarru kyawawa na ƙarshe.

Karka Take Ni'imar da Allah Yayi Maka ka Hangi na Wasu...

MarubuciBashir M. Sulaiman

Sai ya ce da abokinsa, wai muna ina aka raba wannan arzikin ne?​

​Sai abokinsa ya kama hannunsa, ya ce zo ka rakani, sai suka shiga asibiti ga marasa lafiya da masu hatsari.

Sannan abokin ya ce, wai muna ina aka raba waɗannan cututtuka?​

Karka Take Ni'imar da Allah Yayi Maka ka Hangi na Wasu.

​Don haka godewa Allah Ta'ala a duk halin da ka sami kanka, don ka fi wasu.

ALLAH YASA MU DACE AMIN.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Friday, 27 December 2019

KARANTA SUNNONI GUDA 11 A RANAR JUMA'A DA AKA MANTA DA SU

KARANTA SUNNONI GUDA 11 A RANAR JUMA'A DA AKA MANTA DA SU

1. Yin wankan juma'a da sanya turare mai dadin kamshi a ranar juma'a.

Wanda yayi wanka juma'a a ranar juma'a sannan ya sanya Turare ya shafa mai sannan ya taho masallacin juma'a, kuma bai ketara tsakanin mutane biyu sannan ya yi shiru lokacin da liman yake Huduba, an gafarta masa zunubansa tsakanin juma'a zuwa wata juma'ar.

Yayin Ruku'u

Marubuci: Bashir M. Sulaiman

ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ 883

2. Yin shiru lokacin Huɗuba da kuma kama daga ƙetara mutane idan kazo masallacin juma'a.

Kuma bai ƙetara tsakanin mutane biyu sannan ya yi shiru lokacin da liman yake Huɗuba, an gafarta masa zunubansa tsakanin juma'a zuwa wata juma'ar.

ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ 888

3. Fita zuwa masallacin juma'a da wuri kamar daga karfe 11:00 ko 10:30am.

Malamai suna cewa "Sammakon ranar Juma'a yana farawa daga fitowa rana zuwa sa'a ta biyar lokacin zaman liman akan Minbari."

Manzon Allah (S.A.W)

Wanda yazo a sa'ar farko yana da ladar wanda ya yi sadaka da rami,a sa'a ta biyu kamar mai sadaka da saniya,sa'a ta uku kamar sadakar rago, sa'a ta huɗu kamar sadaka da kaza, sa'a ta biyar kamar mai sadaka da kwai, idan liman ya hau mimbari sai a daina ruwatawa.


ﻣﺴﻠﻢ ‏1403

4. Yin barci rana bayan sallar juma'a.

Sahal bin Saad ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ yana cewa" Mu sahabban Manzon Allah (S.A.W) mun kasance muna kwanciya barcin rana a ranar juma'a bayan mun dawo daga sallar juma'a."

ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ‏( 5807 )

Yayin Huɗuba

Wannan ya nuna kenan suna yin sallar juma'ar ne da wuri kuma suna fita masallacin juma'a ne da wuri.

5. Mai Huɗuba zai yi nuni da ɗan yatsarsa manuniya a lokacin da yake addu'a acikin Huɗuba.

Manzon Allah (S.A.W) baya karawa akan yin nuni da ɗan yatsarsa a lokacin da yake yin addu'a a cikin Huɗuba.

 ﻣﺴﻠﻢ ‏( 874 ‏) ﻭﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ‏( 515 ‏) ﺍﺣﻤﺪ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺴﻨﺪ ‏( 17219/17221 / 17224/18299 )

Kwalliya ta Musamman Domin Ranar Juma'a

6. Baya cikin SUNNAH ɗaga hannu a lokacin yin addu'a a cikin Huɗuba ga liman ko mamu.

ﺍﻟﻌﻼﻣﺔ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ

Yana cewa "Ɗaga hannu dan yin addu'a lokacin da liman yake Huɗuba baya cikin SUNNAH".

ﻓﺘﺎﻭﻱ ﺃﺭﻛﺎﻥ ﺍﻹﺳﻼﻡ ‏( ﺹ 393 )

7. Fuskantar liman da kallonsa lokacin da yake Huɗuba.

ﺍﻟﻌﻼﻣﺔ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ

Yana cewa "Fuskantar liman da kallon sa lokacin da yake Huɗuba yana cikin SUNNAR da aka manta da ita".

ﺍﻟﺴﻠﺴﻠﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ 5/110

8. Canza wajan zama ko canza yayin zama ga wanda yake gyangyadi a ranar juma'a.

Manzon Allah (S.A.W) yana cewa "Idan ɗayan ku yana gyangyaɗi a ranar juma'a to ya chanza wajan zaman sa".

ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ ‏( 1119 ‏) ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ‏( 526 ‏) ﺍﺑﻦ ﺧﺰﻳﻤﺔ‏( 1819 )

Hikima akan haka shine motsin da zaka yi na canza zama ko gurin zama zai yanke maka gyangyadi dan ka saurari Huɗuba da addu'ar liman lokacin Huɗuba.

Yayin Sujada

9. Yin sallar nafila bayan juma'a.

Sunnane ga wanda ya halarci sallar juma'a yayi nafila raka'a biyu bayan ya koma gida ko raka'a huɗu a masallaci.

ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ‏( 937 ‏) ﻣﺴﻠﻢ ‏( 882 )

ﺍﻟﻌﻼﻣﺔ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ

Yana cewa: Malamin mu ibn Taimiya yana cewa"Wanda zai yi nafila bayan sallar juma'a idan masallacin zai yi sai yayi raka'a huɗu, idan kuma sai ya koma gida ne sai yayi raka'a biyu kaɗai, wannan shi ne abin da ya tabbata a SUNNAH.

ﺍﻟﺰﺍﺩ ‏( 1/440 )

10. Yawaita salati ga Manzon Allah SAW a daren Juma'a da yinin juma'a.

ﻣﺴﻠﻢ ‏( 881 )

11. Yawaita addu'a bayan sallar la'asar ta ranar Juma'a zuwa faɗuwar rana dan dacewa da lokacin amsa addu'a ranar Juma'a.

ﺍﻟﺰﺍﺩ ‏( 1/440 )

Karanta Suratul Kahf Ranar Juma'a

A DUK RANAR JUMA'A 

Kada muyi ƙasa a gwuiwa wajen yawaita yin Salati ga Manzon Allah (S.A.W)) da Iyalan gidan sa, domin yin Salati ga Manzon Allah(S.A.W.W) da Iyalan gidansa (as) yana nufin:

1. Amsa umarni ne na Allah maɗaukakin Sarki.

2. Samar da haske ne ga kabarin mai yinsa bayan ya mutu.

3. Zikiri ne mafi girma da ɗaukaka.

4. Sinadari ne na rusa zunubai da share lefuka.

5. Ɗaukaka ce ga mai yawaita yin sa.

6. Samun kusanci ne zuwa ga Allah.

7. Bayyanar da Soyayya ne ga Manzon Allah da Iyalan gidansa (A.S).

8. Yinsa a farkon kowanne aikin lada, sirri ne na karɓuwar wannan aikin.

9. Tsarki ne ga ruhi da gangar jikin mai yinsa.

10. Ibada ce karɓabbiya wacce ba a maidowa da wanda yayi.

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA KADAN DAGA CIKIN FALALAR RANAR JUMA'A

KARANTA MANYAN FARILLAN SALLAH GUDA 14

KARANTA MANYAN LADUBBA AKAN MUSULMI GUDA 10 A RANAR JUMA'A

Yiwa Annabi da Iyalan gidansa Salati, sirrin haske ne a Duniya da lahira, dawwama a cikin hakan kuwa yana nufi dawwama ne a cikin lada da samun yardar Allah (S.W.T)

"اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّد وَآل مُحَمَّد".

Allah ne mafi sani.

Allah ka bamu ikon koyi da Manzon Allah (S.A.W) a cikin dukkan ibadar mu da rayuwar Mu baki ɗaya Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode





Tuesday, 26 September 2017

ZUWA GAMATAR DA ZAN AURA

ZUWA GAMATAR DA ZAN AURA

=>1-Ban Yarda ki rinqa
zuwa gidanku ba, sai
sallah shima dan kar
ache na hanaki
zumunchi
.
=>2-Ban yarda ki riqe
waya (handset) a
gidana ba
.
=>3-Ban yarda
qawayenki su
rinqa zuwa gidana ba
domin nine mapi
Cancantah dana debe
miki kewah
.
=>4-Ban yarda ki rinqa
yawo da sunan biki koh
suna ba .
.
=>5-Ban yarda da
wasan qanin miji ba,
domin nine napi
cancanta da inyi wasa
dake
.
=>6-Da akwae kayan
kallo a gidana,
amma ban yarda ki kalla
ba, ke koh da kuwa
Sunnah TV ne domin
nine mapi cancantah
daki kalli puskata
.
=>7-In banda
mahaipina da naki ban
yarda wani ya shigar
min gidana ba tare
da ixinina ba domin ban
gina gidan da wani ba
sai dan ke .
.
=>8-Idan Nayi baqi a
cikin gidana zaki
kulle kanki a cikin daki,
bazaki fitoh ba har sai
sun tapi
.
=>9-Ban yardah ki rinqa
xuwa islamiyyah koh
boko ba, domin zan
cigaba da neman ilmin
addini dana zamani
domin in rinqa koyar
dake a gidana
.
=>10-Idan baki da
Lapiyah ban yarda kije
asibiti wani qaton
banzan ya taba min ke
ba, nima likitah ne
saboda ni zan dubaki a
cikin gidana
.
=>11-Ban yarda ki rinqa
sauraron radio ba
domin nine mapi
cancantah daki saurari
muryatah
.
.
=>Ni kuma na miki
alqawarin Baxan Miki
kisjhiyah ba, kuma koh
kin mutu bazan sake
aure ba .
.
.
=>Hhh , shin koh akwae
wacce zata iya Aurena? saura inji Wata tace
A'a???
.
.
.
Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka  dadinkowa24.blogspot.com mungode
.
Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Al'ummar Nigeria  daga N50 zuwa abinda yasamu duk zaku iya turo da Lambobin katin  ta Email din mu akan officialdadinkowa24@gmail.com  ko Neman Account Number din mu na Bank ga mutanen dabasa cikin Nigeria, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉ officialdadinkowa24@gmail.com 
.
Suna addreshin misali..
.
Subject: Fatan Alheri
Suna: Yusuf Tk
Kasa: Nigeria
Gari: Kano
Garin da akeda Zama: Kaduna
Sako: Yaushe Ne zaku cigaba da Labarin Kundin Tsatsuba Littafi na 2 na Madakin Gini? Mungode
.
Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri
.
ALLAH yabar Zumunci Amin
.
.
Source By Bashir M. Sulaiman

Thursday, 5 March 2020

Kaso Mutum Kuma Kayi Hankali da Mutum a Duk Inda Ka Kasance

Kaso Mutum Kuma Kayi Hankali da Mutum a Duk Inda Ka Kasance

Mutum ne zai yi maka fatan alkhairi, amma idan alkhairin yazo shi zai fara nuna hassada a gareka.

Saboda Ɗan Adam babu mai iya masa sai ALLAH...

Marubuci: Bashir M. Sulaiman

Mutum ne za kayi masa alkhairi sama da sau ɗari, ranar da kai kuskure guda ɗaya dukkan shi ya rushe.

Mutum ne yake rububin ka idan yaga dama ta same ka, amma da zaran damar ta kuɓuce baka sake ganin shi.

Mutum ne za kayi masa alkhairi, daga ƙarshe ya zo yayi maka sharri.

Mutum ne yana hangen wata matsala na iya samunka, amma bazai sanar maka ba, sai bayan ta faru.

Mutum ne zaka riƙeshi amana, amma shi yaci amanar ka.

Mutum ne idan yaga samun duniya a gare ka, zai zo ya raba ka da mutanenka na asali, waɗanda suka san mutuncin ka, amma da ta gushe shi kuma sai ya gudu ya barka.

Ya ALLAH ka haɗa mu da mutane masu ƙaunar mu na gaskiya, kuma tsakani da ALLAH Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.


MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.


Monday, 16 March 2020

Shin Ko Kasan Irin Tafiyar da Sau Daya Ake Yi Kuma Ba Wanda Yakeson Yinta?

Shin Ko Kasan Irin Tafiyar da Sau Daya Ake Yi Kuma Ba Wanda Yakeson Yinta?

Idan ka yi shirin tafiya Kasuwa
ko Office daga gidanka, Iyalanka za suce da kai a dawo lafiya.

Tafiya Ce Mai Nisan Zango

MarubuciBashir M. Sulaiman

Amma wata rana akwai tafiyar da za ta riskeka babu shiri a tare da kai, sannan a cikin Iyalanka babu mai cewa da kai a dawo lafiya, sai dai fa su yi maka Addu'ar samun masauki mai kyau a gurin Ubangijin nan naka mai karamci.

Saboda haka, ya Ɗan Uwa! ka yi
tanadin wannan tafiya mai nisan zango, wacce babu dawowa a cikinta.

Allah kasa muyi kyakkyawan ƙarshe
albarkar manzon Allah (S.A.W) Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Monday, 6 May 2019

KARANTA JERIN SUNAYEN MALAMAI DA ALARAMMOMIN DA JIBWIS TA KASA TA TURA TAFSIRIN RAMADAN NA 1439AH 1440H/2019 A JAHOHIN NAJERIYA DA KASASHEN DUNIYA

KARANTA JERIN SUNAYEN MALAMAI DA ALARAMMOMIN DA JIBWIS TA KASA TA TURA TAFSIRIN RAMADAN NA 1439AH 1440H/2019 A JAHOHIN NAJERIYA DA KASASHEN DUNIYA

JAMA’ATU IZALATIL BID’AH WA IKAMATIS SUNNAH SUNAYEN MALAMAI DA ALARAMMOMIN DA JIBWIS TA KASA TA TURA TAFSIRIN RAMADAN NA 1439AH 1440H/2019 A JAHOHIN NAJERIYA DA KASASHEN DUNIYA.




JIBWIS NIGERIA




1. Sheikh Abdullahi Bala Lau Da Alaramma Nasiru Salihu Gwandu - Jimeta, Adamawa

2. Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo Da Alaramma Mustapha Jalingo - Jalingo, Taraba

3. Sheikh Usman Isa Taliyawa Da Alaramma Abubakar Muhd Gombe - Gombe, Gombe

4. Sheikh Abbas Jega Da Alaramma Abubakar Adam - B/Kebbi, Kebbi

5. Sheikh Ibrahim Sabi’u Jibia Da Alaramma Aminu Salisu Jibia - Masjid Hamza Jibia, Katsina

6. Sheikh Yakubu Musa Hassan / Saifuddeen Yakubu Musa Da Alaramma Usman Birnin Kebbi - Katsina, Katsina

7. Sheikh Dr Isma’il Kumo Basirka Da Alaramma Usman Barikin Ladi - Jos, Plateau

8. Shk Dr. Abdullahi Saleh Pakistan Da Alaramma Abbas Iliyasu - Kano, Kano

9. Sheikh Muh’d Kabir Haruna Gombe Da Alaramma Ahmad Sulaiman - T/Wada / Malali, Kaduna

10. Sheik Dr Ali Mustapha Da Alaramma Mato Gumau - Gashua, Yobe

11. Sheikh Abubakar Giro Argungu Da Alaramma Saifullahi Musa Makera - Masjid Haruna Danja Zaria, Kaduna

12. Sheikh Aliyu Abdullahi Telex Da Alaramma Muhsin Ishaq - Aleiru, Kebbi

13. Sheikh Surajo Muhammad Gusau - Gusau, Zamfara

14. Sheikh Mas’ud Ibrahim Offa - Rimi College, Kaduna

15. Dr Muhammad Sani Umar R/lemo Da Alaramma Abubakar Muhammad Rariya - Masjid Gwallaga, Bauchi

16. Sheikh Sani Yakubu Da Alaramma Ridwan Kaduna - Zaria, Kaduna

17. Sheikh Abubakar Abdussalam Baban Gwale Da Alaramma Tukur Jakada - Alkhulafaur Rashidun, Alpa Nla, Agege, Lagos

18. Sheikh Ahmad Muhammad Boyi Da Alaramma Muhammad Aliyu Babangida - Masjid Finance Jalingo, Taraba

19. Dr Ibrahim Abdullahi Sani R/Lemo Da Alaramma Yusuf Suru - Area 11 Masjid, Abuja

20. Mall. Aliyu Ladan Da Alaramma Nasiru Dan Malam - Life Camp, Abuja

21. Mal AbdulRazak Yahaya Haifan Da Alaramma Kabir Hussaini Daura - Gwagwalada, Abuja

22. Mal. Abdullahi Umar Zaria Da Alaramma Salihu Gumi - Garki Village, Abuja

23. Mal. Auwal Mai Gaskiya Da Alaramma Aliyu Ibrahim Paki - Fed. Min. of Works, Abuja

24. Mal. Abdullahi Karshi Da Alaramma Abdulkrim Akwanga - Villa, Abuja

25. Mal. Sahibul Kuwa - Dakkwa, Abuja

26. Mal Abdulrahman Alzamfari Da Alaramma Saifullahi Kira - Berger Masjid, Abuja

27. Dr Ahmad Atiku Auwal - Gwarimpa Masjid, Abuja

28. Mal. Tajuddeen Imam Da Alaramma Murtala Muhammad - Prince & Princes, Abuja

29. Mal Adda’urrahman Alhassan Saeed - Gumel, Jigawa

30. Dr. Bashir Imam - Masjid Amb. Yola, Adamawa

31. Dr. Sadau Salihu - Yola, Adamawa

32. Dr. Abdulqadir Saleh Kazaure Da  Alaramma Idris Gashuwa - Jimeta, Adamawa

33. Dr Abubakar Bama - Masjid Nyanya, Abuja

34. Dr AbdulRahman Sani Yakubu Da Alaramma Sulaiman Abdullahi Azare -Juwa Emirate Council, Abuja

35. Mal Usman AbdulHamid - Numan, Adamawa

36. Mal. Alkali Sulaiman Yusuf Da Alaramma Dauda Muh’d Zukku - Masallachin Adamu Jumb, Bauchi

37.. Mal. Aliyu Saeed Gamawa Da Alaramma Saeed Adamu - Peoples Bank Masjid Gamawa, Bauchi

38. Dr. Ibrahim Adam Umar Disina- Masjid Rahama, Bauchi

39. Mal. Abba Abdullahi Gwale Da Alaramma Idris Saminaka - Lapai, Niger

40. Mall Abdul aziz Dan lami Da Alaramma
Nafiu A A saeed - Tilden Fulani, Bauchi

41. Mal. Abubakar Mala Da Alaramma Bala Bako - Alkaleri, Bauchi

42. Dr. Zubairu Madaki Da Alaramma Kabir Abdullahi - Masjid Umar bn Al khattab, Kofar Wambai, Bauchi

43. Shk Ahmad Tijjani Yusuf Guruntun Da Alaramma Muhammad Zahruddeen - Masj S19 Dutsen Tenshe Bauchi, Bauchi

44. Mal. Abubakar Mukhtar Yola - Masallachin Nepa Jimeta, Adamawa

45. Sheikh Abubakar Usman Pakistan Da Alaramma Farouq Jada Tambuwal - Makurdi, Benue

46. Mal. Nura Khalil - Apo, Legislative Quarters, Abuja

47. Mal Yaqub Isah Da Alaramma Adam Mahmud - Kwayakusar, Borno

48. Mal.Abba Musa Da Alaramma Aminu Ibrahim Potiskum - Maiduguri, Borno

49. Shk Muhd Abubakar Kachalla Da Alaramma Ahmad Jiha Ismail - Maiduguri, Borno

50. Mal Zainu Usman Baban Tine - NNPC Kaduna, Kaduna

51. Dr. Umar Dokaji Da Alaramma Auwal Ung Maikawo - Sapele, Delta

52. Mal. Nazifi Hashim Zaria Da Alaramma Hassan Musa Funtua - Cattle Market Benin City, Edo

53. Mal. Shafi’I Salihu Kazaure Da Alaramma Sani Ibrahim Mainiyya - Ung. Sabo Ile-Ife, Osun

54. Mal. Mustapha Yusuf Hadejia Da Alaramma Muhd Auwal Jalingo - P/Harcourt, Rivers

55. Mal. Adam Muhammad Adam Da Alaramma Abubakar Jibril Bula - Gombe, Gombe

56. Dr Abdallah Umar Gadon Kaya Da Alaramma Baba Lawal - Kan Bariki,( Water Board) Kumo, Gombe

57. Mal. Usman Bello Santuraki Kumo Da Alaramma Nafiu Ismail - Kazaure, Jigawa

58. Mal. Sulaiman Abubakar Birnin Kudu - Yalwan Damai, Jigawa


59. Mall Isa Abdullahi Da Alaramma Hamza Isa Abdullahi - Hadeja, Jigawa

60. Mal. Alkasim Hotoro Da Alaramma Yunus Isma’il - Potistum, Yobe

61. Dr Abdurrahman Idris zakariyya Da Alaramma Auwal Iliyasu - Saminaka, Kaduna

62. Mal. Musa Asadus Sunnah - Sokoto, Sokoto

63. Mal. Murtala Nasir Almisry Da Alaramma Aliyu Dahir - ASD Motors, Kaduna

64. Mall Abdulrahman Maiduguri Da Alaramma Shamsuddeen Haruna - Rigachikun, Kaduna

65. Mal Abubakar Usman Bolari - Oshogbo, Osun

66. Mal. Hamza Alhassan Sa’eed Da Alaramma Abubakar Rano - Sani Zangon Daura Estate, Kado, Abuja

67. Mal Nura Kofar Mata Da Alaramma Abubakar Umar Balarabe - Ojo-Express T/Sunnah Ibadan, Oyo

68. Mal. Ibrahim Abdullahi Bauchi Da Alaramma Kabiru Yawuri - Ado-Ekiti, Ekiti

69. Dr Idris Alhassan Abubakar Da Alaramma Shamsu Ahmad Mairuwa - Gboko, Benue

70. Sheikh Abdul Hadi Aliyu Daura Da Alaramma Yunusa Abubakar - Dan Fodio Masjid, Kaduna

71. Mal. Usman Zagga Da Alaramm Safiyan Abdullahi - Rijau, Niger

72. Mall Shuaibu Salihu Zaria Da Alaramma Abdullahi shu”aibu sal - Al-Islah Foundatn Zaria, Kaduna

73. Mal. Muhammad Sani Alhamidy - Bebeji, Kano

74. Mal. Abdul mudallib Ahmad Muhammad Da Alaramma Salihu Muhd Usman - Masjid Triump, Kano

75. Mall Abdul mudallib Gusau Da Alaramma Umar Ramadan - State Univ.Wudil, Kano

76. Mall Saifullahi Adam Shuaib Da Alaramma Tasiu Sabiu - Huguma Takai Kano, Kano

77. Mal Muhd Adam Algargawy - Kura, Kano

78. Mall Ibrahim Idris Zakariyya - Tudun Wadan Dankade, Kano

79. Mall Surajo Mahmoud Kankia - Govt Printing Katsina, Katsina

80. Mal. Aminu Liman Mustapha - Zaria Rd Masjid FT, Katsina

81. Mal. Mukhtar Usman Jibia - Govt. House, Katsina

82. Mal. Aminu Yammawa - Masjid. G.R.A, Katsina

83. Mal. Yahaya Salihu Isah Da Alaramma Auwal Umar - Masjid Kerau, Katsina

84. Mal. Musa Mansur Da Alaramma Salihu Ahmad - Masjid Karama Daura, Katsina

85. Mal. Hassan Yusuf Da Alaramma Haruna Salisu - Masjid Senator (Madawaki)Daura, Katsina

86. Dr Jamilu Zarewa Da Alaramma Ashiru Rawayau, Masj Bilal Ibn Rabah N/Low-Cost, Katsina

87. Mall Safiyyu Alqasim Saulawa Da Alaramma Mukhtar Salisu Jibiya - Bakori, Katsina

88. Mal. Jamilu Albani Da Alaramma Abuzaid - Lafia, Nasarawa

89. Mal. Umar Jiga Da Alaramma Shukranu Yelwan Shandam - Sokoto, Sokoto

90. Mal. Muhammad Rabi’u Isah Fatawa Da Alaramma Adam Muhammad Fana - Bena, Kebbi

91. Mal. Ahmad Ahmad Kura - Dutsin-ma, Katsina

92. Mal. Imam Aliyu Bunza Da Alaramma Amiru Ibrahim Argungun - Argungun, Kebbi

93. Mal.Umar Sadiq Jega Da Alaramma Iliyasu Birnin Gwari - Suleja, Niger

94. Sheikh Mukhtar Zinder - Illela, Sokoto

95. Mal. Imam Dahiru Lokoja Da Alaramma Ishaq - Lokoja, Kogi

96. Mal. Imam Yahaya Iddah Da Alaramma Auwal Muhammad - Iddah, Kogi

97. Mal. Yusuf Umar Da Alaramma Rabi’u Ibrahim - Obajana, Kogi

98. Mal. Salihu Muhammad Da Alaramma Ahmad Muhammad - Kaiama, Kwara

99. Mal. Attahiru Kaiama Da Alaramma Ibrahim Kaima - Ilorin, Kwara

100. Dr Abdulmajid Umar - Rimi Collage, Kaduna

101. Mal. Hussini Isa Abubakar Da Alaramma Nafi’u Bena - Yawuri, Kebbi

102. Dr Muhammad Sani Suleiman Ft Da Alarramma Abubakar Kaura - Gombe, Kumo, Gombe

103. Mall. Bukhari Yakubu Da Alaramma Muhammad fari - Agege Lagos, Lagos

104. Mall Adamu Salihu Gusau - Tambuwal, Sokoto

105. Sheikh Imam Sulaiman - Masjid 1004, Lagos

106. Mal. AbdulRahim Sabi’u Rafindadi Da Alaramma Sani Danwarai - Kontagora, Niger

107. Mall Adam Ibrahim Al-madani Da Alaramma Abbas Dahir Abubakar - Karu Masjid JIBWIS, Nassarawa

108. Mal Rufa’i Nasir Da Alaramma Ibrahim Abubakar - Keffi, Nasarawa

109. Dr Umar Gumi Da Alaramma Sulaiman Hussaini Doma - Doma, Nasarawa

110. Mal. Muh’d Sani Ahmad Almuhadis Da Alaramma Abubakar Bawa - Wawa, Niger

111. Mal. Lawal Shu’aibu Abubakar Da Alaramma Abdulrashid Jega - Minna, Niger

112. Mal. Mujittaba Yakubu Musa Da Alaramma Jamilu Isah Dallaje - Kafanchan, Kaduna

113. Mall Isah Shehu Ruga Da Alaramma Abubakar Ung Madi - Ganye, Adamawa

114. Mall.Muhammad Auwal Rijau Da Alaramma Abubakar A. Abubakar Kagara - Mariga, Niger

115. Mal. Abba Musa Da Alaramma Aminu Ibrahim - Maiduguri, Borno

116. Mall Musa Mujaddadi - Lafai, Nigrer

117. Mal.Bukhari Ibn Ishaq Albayani Da Alm Anas Abdullah Yalwan Shandam - Shiroro, Niger

118. Mal Isah Ibrahim Bawa Mai Shinkafa Da Alrm Ismail Abdullahi Mangu - Yalwan Shendam, Plateau

119. Mall Muhammad Aminu Muhammad Saminaka Da Alaramma Yusuf Dabai Mai  60 - Bukur, Plateau

120. Mal. Muhammad Barkindo Jungudo Da Alaramma Abdullahi Badejo - Jalingo Masjid Ummah, Taraba

121. Mall Nuruddeen Tukur Numan Da Alaramma Bashir Gombe - Jami’u Hajara Plaza Funtua, Katsina

122. Mal. Yunus Saeed Abdul-Hamid Da Refinery Depot, Rivers

123. Mal. Abdulbasir Ung MaiKawo Da Alarmma Sani Mulumfashi - Koko, Kebbi

124. Mal.Aliyu Aliyu Muhammad Jos Da Alaramma Bala Abubakar Tambuwal - Hadeja, Jigawa

125. Mal. Umar Mai Damma Da Alaramma Auwal Adam Sokoto - Masjid Sheik Abubakar Gumi Sokoto, Sokoto

126. Mal. Abubakar Ladan Mai Idigami Da Alaramma Muhammad Auwal - Masjid Lokoja Road Sokoto, Sokoto

127. Mall Sani Abubakar Tambuwal - Sultan Ibrahim Dasuki Mosque, Sokoto

128. Sheikh Dr. Mansur Ibrahim Sokoto Da Alaramma Abubakar Ghani - MasjidAbu Huraira, Sokoto

129. Dr Muhammad Rabi”u Collage Da Alaramma Sidi Ali - Ningi, Bauchi

130. Mal. Gambo Kyari Maiduguri Da Alaramma Mustapha Hamza Jarmai - Wukari, Taraba

131. Mal Khalid Usman Khalid Da Alaramma Salisu Ung. Kanawa - Gummi, Zamfara

132. Mal Hassan Bako - Shagamu, Ogun
133. Imam khidir Bello Manufa Da Alaramma Hudu Usman Aleiru - Bukkuyum, Zamfara

134. Mal. Attahiru Muhammad Tilde - Jaji Maji, Yobe

135. Mal Abdulaziz Ibrahim Bauchi Da Alaramma Sulaiman shafi’I FTA - Matazu, Katsina

136. Mal Aliyu S. Mafara Da Alaramma Usman Tagule - Kamba, Kebbi

137. Mal.Ibrahim Damaturu Da Alaramma Sani Nguru - Damaturu, Yobe

138. Dr Umar Musa Kano Da Alaramma Bello Argungu - Anka, Zamfara

139. Mal. Usman Arabi - Malumfashi, Katsina

140. Mal. Aminu Numan Da Alaramma Amir Abdullahi Dorawa - Mangu, Plateau

141. Mal. Abubakar Salihu Dengi - Ibadan, Oyo

142. Mal. Anas Assalafy - Ketaren Waya, Benue

143. Mal. Abubakar Musa Azi - Ebonyi, Ebonyi

144. Mal. Shuaibu Adam Makoli - Dangi, Plateau

145. Mal. Aminu Khalil U/Barau - Masjid Ahlil Sunnah Ikorodu, Lagos

146. Mal Surajo Umar Maga Da Alaramma Alkasim Musa - Masjid Hausa Qtrs Ugella, Delta

147. Mal Musa Usman Alkanawi Da Alaramma Mu’awiyya Adbdulrahman - Masjid Ujole, Ekpoma Town, Edo

148. Mal Abubakar Usman Da Alaramma Anas Abubakar - Masjid Lagos Str Benin City, Edo

149. Sheik Muhammad Fatihu Da Alaramma Ibrahim Adam Futua - Apo Legislative Qtrs Zone A, FCT

150. Sheik Ibrahim Lawal (USAMA) Alaramma Zaharadden Surajo - Apo Legislative Qtrs Zone B, FCT

151. Mal. Muhammad Abubakar Da Alaramma Fadlu Muhammad - Apo Legislative Qtrs Zone D, FCT

152. Mal Yahaya Gidadawa Da Alaramma Mustapha Hamza Jarmai - Onitsha, Anambra

153. Mal Murtala Bello Da’a Da Alaramma Ibrahim khamis Saminaka - Benin city, Edo

154. Mal Hussaini Yusuf Mabera Da Alaramma Mustapha Argungu - Warri, Delta

155. Mall. Muhammad Auwal Isah Jere Da Alaramma Murtada M. Namadi - Bakin Gareji,Jere, Kaduna

156. Dr Abubakar Usman Ribah Da Alaramma Muhammad Bunza - Bargu, Niger

157. Mall Rabi’u Aminu Bebeji - Geidam,  Yobe


GHANA

1. Mal. Muhammad Umar Abdulhanna Da Alaramma Abdulrahman Abubakar - Masjid Ib Abbas Ghana

2. Mal. Ahmad Ibrahim - Masjid Khulafa’urrashi
dun

3. Mal. Muh’d Bello Muh’d Saminu - Masjid Bilal

4. Mal. Sanusi Yusuf Muh’d - Masjid Furqan

5. Mal. Abdul Razak Kumasi Da Alaramma
Abdullahi Ibrahim - Masjid Daraarul Hadith

6. Mal. Abdul Malik Idris - Masjid Attaqwa

7. Mal. Muhammad Kaamil Da Alaramma Abubakar Idris - Masjid Ta’afo

8. Mal. Muhammad Addo - Masjid Zuraak

9. Mal. Muhammad Suwaid - Annaduwa

10. Mal. Manir Saeed - Bilal Accara

11. Mal. Sulaiman Adam Aljamzuri - Masjid Jami’ul Rahma

12. Mal. Muhammad Taufeeq Abdulrahman Kulusey - Masjidul Nurul Ameen


TOGO


1. Mal. Muawiyya Umar Mukhtar Ali Da
Alaramma Mukhtar Ali - Masjid Abu Ubaida

2. Mal. Salihu Saaya - Masjid Furqan

3. Mal. Abubakar Ali - Masjid Attaqwa

4. Imam Ahalil Sunnah (Abdulwahab Abdallah) Da Alaramma Dan Mairogo - Babban Masallacin Zango

COT’D VOURE


1. Mal. Jibirilu Musa Da Alaramma Usman Muh’d - Masjid Khausar Farbi Abidjan

2. Mal. Alhassan Musa Da Alaramma Abubakar - Apobo Abidja

3. Mal. Muh’d Abdulkarim Da Alaramma Abubakar Musa - Masjid Alh. Yusha’u Usaini Abidjan

4. Mal. Abdulsalam Shu’aibu Da Alaramma
Ukasha Alasan - Masjid Hausa Bugu Korgu

5. Mal. Khalil Abubakar Da Alaramma Abubakar Madu - Masjid Hausa Sempedro

6. Mal. Idris Haruna Da Alaramma Buhari Sale - Fresh Zeal Abidja

7. Mal. Muhammad Hariz Da Alaramma Abdullahi Yusuf Yakubu

8. Mal. Hamza Abdullahi Da Alaramma Abdullahi Abdulrahman - Yamasukuro

9. Mal. Hamza Idris - Yamasukuro

NIGER REP.


1. Mal. Imam Abdullah Umar - Masjid Imam Malik Niamey

2. Mal. Hussaini Hassan - Masjid Usman Ibn Affan Niamey

3. Mal. Abdul rahman Hussaini - Masjid Imamul Bukhari Niamey

4. Mal. Kasim Ali - Masjid Umar bn Khattab Niame

5. Mal. Iliyasu Abdullahi Da Alaramma Adam Muh’d Ibrahim - Masjid Karkada Zinder

6. Mal. Nazir Manzo Magarya Da Alaramma Abubakar Alhassan - Magarya

7. Mal. Abubakar Ibrahim - Magarya

8. Mal. Murtala Ibrahim - Maradi

9. Mal. Murtala Ibrahim - Tassawa

10. Mal. Adamu Salihu - Dosso

11. Mal. Abba Ghana - Tahoa

12. Mal. Nuhu Muhammad - Tahoa

13. Mal. Khamis Ahmad Da Alaramma Abubakar Usman - Galmi

14. Mal. Muhammad Khulud Ahmad - Maine, Soroa

15. Mal. Adam Ibrahim - Dosso

16. Mal. Abdulrahman - Teleberi

17. Mal. Dauda Nuhu - Teleberi

18. Mal. Yakubu - Teleberi

19. Mal. Yunus Chilakaro - Diffa

20. Mal. Abba Ghana - TahoaMal.

21. Ishaq Adam (Barrister) Da Alaramma Abdulhay. - Umar bn Alkhadab Gaya

22. Sheik Shuaibu Muhammadu Da Alaramma Sulaiman Abubakar - Masjud Al’ansar Niamey

23. Mal. Aliyu Muhammad Sani Adarawa Da Alaramma Ibrahim Yahuza Bauchi - Niamey

24. Mal.Muhammadu Haruna Gaya Da Alaramma Nuhu Adamu - Masjid Imam Malik

25. Mal.Muhammad Usman Da Alaramma Khalil Iarhim - Masjid Muhajirin

26. Mal.Sanusi Abubakar Da Alaramma Muhammad Abubkar - Masjid Round Point Ba Are

27. Mal. Salifou Abdullahi Maradi Da Alaramma Kamissou - Masjid Marad

28. Mal. Buhari Muhammad Da Alaramma Idrissa Issofou - Masjid Tahoa

29. Mal. Salissou Garba Da Alaramma Massa-oudour Hussaini - Masjid Diffa

30. Mal. Laminou Da Alaramma Aliou Moussa - Masjid Zinder

31 Mal. Khalid Hassan Da Alaramma Abdullbaki - Masjid Niamey

32. Mal. Ousseini Abdoulaye Da Alaramma Laouali - Masjid Arlit

33. Mal. Bachirou Yahaye Da Alaramma Ibrahim - Masjid Tillaberi

BURKINA FASO


1. Mal. Yakubu Tanko - Kantchari

2. Mal. Hamma Zakariya - Namuno

3. Mal. Dr. Kindo Muhammad - Ougadougou

4. Mal. Muhammad Bashir Da Alaramma Yahaya Adam - Falagountou

5. Mal. Aufon Muhammad - Falagountou

6. Mal. Muhammad Usman - Masjid Furqan


BENIN REP.



1. Mal. Muhammad Kabir - Zango Cottonou

2. Mal. Suleiman Abubakar Da Alaramma Abu Sambo - Malabil

3. Mal. Abdulganiyu Raji Da Alaramma Shuaibu Latifi - Malabil

4. Mal. Jibril Abubakar Da Alaramma Ibrahim Abdullahi - Cotonor

5. Mal. Umar Garba Da Alaramma Zubair Mairiga - Cotonor

6. Mal. Idris Ishaq Da Alaramma Mujahid Dahir - Zuggu

7. Mal. Usman Abdulwahab Da Alaramma Hudu Abdullatif - Zuggu

8. Mal. Marwan Umar Da Alaramma Abdul Mateen - Kandee

9. Mal. Haruna Alhassan Da Alaramma Nasir Ishaq - Kandee

10. Mal. Dr. Dauda Da Alaramma Isa Adam - Kandee

11. Sheikh Abdullahi Banji Da Alaramma Jibril Ahmad - Malabil

12. Mal. Khalid Zakariya Da Alaramma Dauda Abubakar - Boyiko

13. Mal. Mukhtar - Farako

CAMEROUN


1. Sheikh Saidu Makoli - Bamenda

2. Sheikh Dr. Abu Umar Bala - Bamenda

3. Sheikh Suleman - Douala

4. Sheikh Bello - Younde

5. Sheikh Hadi - Younde

6. Sheikh Godabe - Doula

7. Sheikh Usman - Younde

8. Sheikh Sule Adam Labo - Masjid
ITTIHAD, Doula

9. Sheikh Abu Umar - Masjid Nur, Baminda

10. Sheikh Usman Biyagoro - Masjid Mgyengai, Younde

11. Sheikh Bello - Masjid Alhaji Garbati, Younde

12. Imam Mahmud Aliyu - Baban Masallacin Sarki, Gamdare

13. Sheikh Abdullahi - Masjid Alhaji Adam Bertuwa

14. Sheikh Zakariya Dotti - Masjid Salam, Doula

15. Sheikh Yakubu - Masjid Rahma Walhidaya, Doual

16. Sheikh Nasara Ismail Bagori - Masjid Taqwa

SENEGAL


1. Mal. Abdulkarim Yahaya - Dakar
GUINEA CONAKRY

1. Dr. Mourris Abubakar - Conakry
CENTRAL AFRICA

1. Dr. Badiga Moussa - Bangui

SAUDI ARABIA

1. Shiekh Rajab - Masjidu Ameera Makkah
United State Of America (USA)

1. Mal. Kassim Muhammad Bella - Masjid Mumineen 8875 Benning, Dr Houston Texas 77031, USA

2. Mal. Firdaws Ladan - Masjid Ibn Taymiyyah 8000 martin luther king Jr Hwj,Glen, Arden,MD, USA
Europe(UK)

1. Mal.Muhammad Mubarak Abdulai (M Bature) - Mrkazul Tauheed NO.1 rectory Road,St 1,Stoke on Trent, Staffordshire, UK


2. Mal.Muhammad Saifuddeen Abubakar - Masjidul Salaam Comunidad Islamica De Benidorn Juzgados, Benidorm, Alicante, Spain

3. Mal.Mu’azu Shu’aib Bamba - Masjidul Sunnah Uppsala, Bandstolvagen,37,75648

4. Mal.yousuf Umar Jallo - Masjidul Rahma (Hamburg) Beim Gesundbrunnen 1 ,20537,hamburg, Germany

5. Mal.Muhammad Brussels - Masjid Abubakar Sddiq Rue de la Colonne, 32,Bruxells 1080. Belgium

Allah ya taimaka, ya bada ikon aiki da abun da za'a gabatar. Amin.



Sanarwa: Sakataren kungiya na kasa
Sheikh Dr. Kabiru Gombe.


Via: Ibrahim Baba Suleiman
Director General, Jibwis
Social Media.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode






Source: Jibwis Nigeria

Monday, 27 August 2018

Karanta Kaji: Kuskure 6 da akai acikin Film din MARIYA tare da Sharhin Fim ɗin

Karanta Kaji: Kuskure 6 da akai acikin Film din MARIYA tare da Sharhin Fim ɗin

Suna: Mariya

Tsara Labari: Fauziyya D. Sulaiman da Ali Nuhu

Kamfani: Mai Shadda Inbestment

Shiryawa: Abubakar Bashir Mai Shadda

Umarni: Ali Nuhu


Jarumai: Ali Nuhu, Jamila Nagudu, Maryam Yahya, Ladidi Fagge, Garzali Miko, Umar M. Sharif, Baballe Hayatu, Hadiza Muhammad, Abdu Karkuzu. Da sauran su.

Sharhi: Hamza Gambo Umar

A farkon fim din an nuna Yawale (Garzali Miko) tare da tawagar abokan sa ‘yan daba suna tafe rike da mugayen makamai, ganin su ne yasa Abdullahi (Umar M. Sharif) Ya garzaya a guje yaje gidan su Mariya (Maryam Yahya) ya sanar da mahaifiyar ta Habiba (Ladidi Fagge) tahowar su Yawale da mugun nufi don su hallaka Mariya. Jin hakan yasa Mariya tabi ta bayan gidan ta gudu yayin da saurayin ta Abdullahi yabi bayan ta suka bazama cikin daji. A wannan lokacin ne Yawale da gayyar abokan sa ‘yan daba suka iso gidan su Mariya suna neman ta, ganin basu ganta bane yasa suka cinnawa gidan wuta sannan suka fita, a sannan ne wani saurayi ya fada musu hanyar da su Mariya suka bi, nan suka bi bayan su Mariya wadda ta sanar wa da Abdullahi tana jin ‘kishirwa, hakan yasa ya bazama cikin daji yana neman ruwa, kafin ya dawo su Yawale sun kusa isowa wajen da Mariya ta buya, amma sai wani maciji ya biyo su hakan yasa suka gudu. Ganin sun gudu ne sai Mariya ta cigaba da gudu, amma sai tayi kicibus da abokan Yawale ‘yan daba, har sun yi yunkurin cutar da ita amma sai tayi nasarar watsa musu ‘kasa a idanun su, hakan yasa suka daina gani, ita kuma Mariya ta gudu shima Abdullahi yabi bayan ta rike da robar ruwan da ya debo mata. Bayan Abdullahi ya kawowa Mariya ruwa tasha sai ta fadi ‘kasa ta suma a sanadiyyar jigatar da tayi da kuma raunin da taji a goshin ta. Kafin faruwar hakan a baya Mariya suna soyayya da Abdullahi duk da Yawale ma yana son ta, domin akwai lokacin da ya taba tsayar da ita yana mata magana amma sai tayi masa rashin kunya wanda hakan yasa Abokin Yawale ya mareta amma sai Yawale ya rama mata duk da tayi fushi ta bar musu wajen.

A gefe daya kuma mahaifin Yawale ma yana son Mariya wanda ya kasance Sarkin Fawa a garin (Abdu Kano) Sarkin Fawa mutum ne mai auri saki domin bai yarda a haihu a gidan sa ba, uwargidan sa Talatu (Hadiza Muhammad) itace kadai wadda baya sakin ta domin ita ke kula da gidan sa. Wata rana Sarkin Fawa suna tafe da Tanimu (Musa Mai Sana’a) sai yaga Mariya yaji yana son ta, nan fa Tanimu ya ‘karfafa masa guiwa kuma yaje wajen Habiba mahaifiyar Mariya (Ladidi Fagge) ya sanar mata da cewar Sarkin Fawa yana son auren Mariya amma sai Habiba ta nuna sam bata amince da hakan ba. Haka sai Tanimu ya sake dawowa ya kawowa Habiba kudi don ta amince a aurawa Mariya Sarkin Fawa amma sam ta’ki karbar kudin sa. Hakan yasa Sarkin Fawa da Tanimu suka nufi wajen ‘kanin mahaifin Mariya wato Kawu Bala (Alasan Kwalle) wanda ya kasance me son abin duniya. Jin bukatar su Sarkin Fawa da kuma kudin da suka basa sai ya amince zai bashi auren Mariya amma bayan yaje wajen Habiba da maganar sai ta’ki amincewa. Cikin lokaci kadan Kawu Bala ya karbi kudin auren Mariya da sadaki a wajen Sarkin Fawa sannan yaje ya bawa Habiba wasu daga cikin kudin, amma sam ta’ki karba, saidai hakan bai sauyawa Kawu Bala ‘kudirin sa na aurar da Mariya ba.

Lokacin da Mariya ta samu labarin abinda ke shirin faruwa na auren dolen da za’a yi mata sai ta garzaya taje ta fadawa saurayin ta Abdullahi, nan fa duk hankalin su ya tashi suka rasa mafita har zuwa lokacin da aka daura auren Mariya da Sarkin Fawa.
Bayan auren ne Mariya ta kulle kanta a cikin daki ta’ki amince wa da Sarkin Fawa, duk da irin dabarar da yayi don ta amince dashi amma hakan ya faskara. Shi kuwa Yawale ganin Mariya ta auri mahaifin sa sai ya tsaneta ko kallon arziki ya daina shiga tsakanin su. Wata rana Mariya tana zaune a cikin dakin ta tana sauraron rediyo sai taji ana bada labarin wata mata wadda ta zubawa mijinta guba a cikin abinci yaci ya mutu a sakamakon matar bata son sa. Jin hakan ne yasa Mariya ta fito ta aiki Auwalu dan Sarkin Fawa ta bashi kudi ya siyo mata shinkafar bera ta nuna masa beraye ne suka dameta zata zuba musu magani. A bangaren Abdullahi kuwa ya shiga damuwa saboda rashin samun damar auren Mariya iyayen sa sun rarrashe sa amma sai ya roke su akan su bashi dama ya tafi birni wajen kawun sa. Wata rana Talatu uwar gidan Sarkin Fawa ta bawa Mariya girkin abincin gidan da nufin lokacin karbar girkin ta yayi. Bayan Mariya ta girka abinci sai ta zuba masa shinkafar bera a cikin abincin, har tayi nufin kai wa Sarkin Fawa abinci sai tayi wani tunani wanda hakan yasa ta sauya ra’ayi ta fasa zuba masa guba a cikin abinci, har ta juya zata mayar da abincin sai Talatu ta nufo wajen ta ta nuna lallai sai Mariya ta kai wa Sarkin Fawa abincin yaci domin taga lokacin da Mariya ta zuba gubar, haka Mariya ta kai abincin ba don ranta yaso ba. Ai kuwa bayan su Sarkin Fawa da Tanimu sun ci abincin sai duk suka mutu. Daga lokacin da su Sarkin Fawa suka mutu sai aka mi’ka Mariya ga jami’an tsaro, daga nan kuma aka mika ta ga kotu aka fara shari’a. A wannan lokacin ne wata lauya (Jamila Nagudu) ta roki mijinta (Ali Nuhu) akan ya bata damar tsayawa Mariya a kotu domin ta tausaya mata. Bayan ya bata dama ne aka cigaba da shari’a, yayin da Abdullahi tun kafin hakan ta faru ya soma yawo a wajen lauyoyi irin su (Baballe Hayatu) yana neman lauyan da zai tsayawa Mariya amma sai suka fada masa wasu miliyoyin kudi da zai bayar wanda sam bashi dasu. Daga ‘karshe dai lauyar da ta tsayawa Mariya ta shiga ta fita har aka kori ‘karar su Mariya domin bata kai matakin da za’a yanke mata hukunci ba. Saidai kafin kotu ta kori ‘karar sai lauyar ta kira Talatu kuma ta soma yi mata tambayoyi irin nasu na ‘kwararrun likitoci wanda a sannan ne aka gane cewa Talatu ce ta kashe Sarkin Fawa ba Mariya ba. Nan dai aka yankewa Talatu uwargidan Sarkin Fawa hukuncin kisa, yayin da kotu ta wanke Mariya daga zargin da ake mata.

Bayan dawowar su ‘kauye ne jami’an tsaro suka kama Yawale da tawagar sa saboda yunkurin da suka yi na kashe Mariya. Yayin da Mariya ta cigaba da soyayya da Abdullahi.

Abubuwan Birgewa

1- Marubutan fim din sun yi ‘ko’kari wajen gina labarin, kuma fim din ya tafi kai tsaye domin har ya dire labarin bai karye ba.

2- Anyi ‘kokari wajen samar da kayan aiki masu kyau, kamar su camera da abin daukar sauti, haka kuma an samar da wuraren da suka dace da labarin.

3- Daraktan fim din yayi ‘ko’kari wajen gina fim din ta hanyar da ta dace, haka kuma jaruman sun yi ‘ko’kari musamman Mariya da Yawale.

4- Wa’ko’kin fim din sun nishadantar, haka kuma wasu daga cikin jaruman sun nishadantar da mai kallo, irin su Abdu Kano (Sarkin Fawa) da Tanimu (Musa Mai Sana’a)

Kurakurai:

1- A cikin kotu lokacin da alkali yace ya janye shari’ar Mariya (Maryam Yahya) akan cewar an yi mata afuwa kuma kotu ta wanke ta, ya dace ace an ga matsanancin farin ciki a fuskar Abdullahi (Umar M Sharif) amma fuskar sa a murtuke babu alamar murna duk da irin son da aka nuna yana yi mata.

2- Jarumin fim din Abdullahi ba shi da abinda ake cewar “action” a turance ma’ana kazar-kazar a aikace, sanyin sa yayi yawa domin akwai abubuwan da ya dace ya nuna zafin sa akan su saboda son da yake yiwa Mariya amma bai yiba.

3- An ga Kawu Bala ya fadi ‘kasa bayan sun gama rigima da mahaifiyar Mariya, shin mutuwa yayi ko suma? Sannan kuma menene sanadin hakan? Domin shine wanda bashi da gaskiya kuma shine yaci zarafin ta balantana ace sanadin abinda tayi masa ne yasa zuciyar sa ta buga, shin hakki ne ya kama shi ko me? Ya kamata a wayar da kan me kallo.

4- Wakokin fim din sun yi barkatai, domin da yawa daga cikin su basu sami muhalli ba kawai sako su aka yi.

5- A kotu an ga su Yawale suna hauragiya duk da tsari da doka irin ta kotu amma ba’a ga an tsawatar musu ba, ya dace a nuna musu cewar kotu fa ba ‘kauye bace ballantana suyi abinda suka ga dama a kyale su.

6- Kauyen da suke ciki mai suna kukan ka banza an nuna ‘kauye ne ‘kayau amma wayewar mutanen garin da lafuzan su sam babu ‘kauyanci a ciki, hakan yafi kama da wadanda suke cikin tsakiyar birni.

Karkarewa:

Fim din ya fadakar kuma ya samu kyakykyawan aiki daga wajen kwararrun ma’aikata, amma ya yi matukar kamanceceniya da wasu labaran fitattun finafinan Hausa da a ka taba yi a baya-bayan nan, wato Bilkisu Mai Gadon Zinare da kuma Rayuwa Bayan Mutuwa.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Leadership A Yau

Sunday, 27 October 2019

Karanta Kurakurai 4 da akai a cikin Film din HAFEEZ tare da Sharhin Fim din

Karanta Kurakurai 4 da akai a cikin Film din HAFEEZ tare da Sharhin Fim din

Suna: Hafiz

Tsara Labari: Fauziyya D. Sulaiman

Kamfani: Maishadda Global Production Limited

Shiryawa: Abubakar Bashir Mai Shadda

Umarni: Ali Nuhu

Jarumai: Umar M. Sharif, Ali Nuhu, Yakubu Muhammad, Hassana Muhammad, Maryam Yahya, Amal Umar, Bilkisu Shema, Aisha Humaira, Abba El-Mustafa, Asma’u Sani, Jamila Umar Nagudu, Aisha Yola. Da sauran su.

Sharhin Fim din Hafeez


Sharhi: Hamza Gambo Umar

A farkon fim din an nuna Salma (Aisha Humaira) suna hira da kanwarta Saudat (Amal Umar) a sannan ne kuma mahaifiyar su (Asma’u Sani) ta shigo dakin ta kira Salma da nufin taje wajen bakon saurayin ta Hafiz wanda yazo gidan, jin hakan ne yasa Saudat ta soma yabawa da Hafiz amma sai Salma tayi saurin dakatar da ita ta hanyar gargadin ta akan kada ta shiga sabgar sabon saurayin ta.

Sai dai kuma cikin rashin sa’a, bayan Salma ta fita zuwa wajen Hafiz tun a haduwar farko yaji bata birge shi ba saboda sabanin fahimta da suka samu wanda ya janyo sanadin day a mari Salma din kafin ya bar gidan.

Amma kuma duk da wulakancin da yayiwa Salma mahaifiyar ta bata ji haushin abin ba sai ma laifin Salma din da take gani saboda ta bata mata shiri domin ta kasha kudi masu yawa a wajen malamai don a jawo mata hankalin Hafiz zuwa kan ‘yar ta saboda kasancewar shi dan masu kudi, a dalilin haka ne ma yasa bayan kanwar Salma ta samu mahaifiyar tasu da rokon a shawo mata kan Hafiz ko ita zai saurare ta, mahaifiyar ta su bata bata lokaci ba wajen daukar Saudat din suka nufi gidan iyayen Hafiz.

Amma duk da kasancewar mahaifiyar Hafiz wato Azeema (Jamila Nagudu) ta kasance aminiya ga Mahaifiyar su Salma (Asma’u Sani) Hakan bai sa Azeema tayi kokarin tilastawa Hafiz akan yayi soyayya da Saudat ba, domin shi dan gata ne sosai a wajen iyayen nasa wadanda ba sa son ganin abinda zai bata masa rai. Shima kuma Hafiz ko bayan day a shigo gidan ya hadu da Saudat sai ya fice daga gidan saboda ganin yadda take kallon shi, amma duk da haka sai da Saudat tabi bayan shi zuwa waje inda ta nuna masa cewar tana kaunar shi, nan Hafiz ya watsar da ita ba tare daya karbi soyayyar ta ba.

Shi dai Hafiz ya taso mutum me tsananin farin jini a wajen ‘yammata, duk budurwar da ta gan shi sai taji ya birge ta kuma ta fara soyayya dashi, akwai ba don komai ba sai don kyau da iya kwalliyar sa gami da kudin da mahaifin shi ya mallaka wanda yake takama dasu. Babban abin takaicin kuma shine, Hafiz sam bai taba ganin yarinyar da ta birge shi ba akaf cikin ‘yammatan da suke zub da ajin su wajen nuna masa cewar suna son shi, gaba daya wulakanci yake yi musu bay a basu fuskar da zasu rayu tare, yayin da a kullum iyayen shi ba su da burin da ya wuce su ga yayi aure ya zauna da iyalin sa.

Hakan ne kuma yasa iyayen shi suka bashi goyon baya wajen zuwa ya ga ‘yar abokin mahaifin sa ko zasu daidaita har ya aure ta, amma cikin rashin sa’a Hafiz sai yaga itama yarinyar bat a birge shi ba, hakan yasa yayi mata kyautar kaya yayi tafiyar sa, wanda ganin haka sai ya yiwa mahaifin yarinyar ciwo (Abba Al-Mustafa) saboda yana matukar son Hafiz ya auri ‘yar shi ko don hakan ya zamo sanadin wani cikar burin sa, dalilin hakan ne yasa yaje ya sanar da mahaifin Hafiz wato (Yakubu Muhammad) cewar Hafiz ya amince da auren ‘yar sa, amma ko da mahaifin Hafiz ya tuntube sa sai ya nuna sam ba haka bane.

Ana tsaka da haka ne Hafiz ya hadu da Safna (Hassana Muhammad) wadda ta kasance ‘yar talakawa, tun daga sanda ta taimakawa da Hafiz ruwa ya zuba a motar shi sai yaji ta birge shi har ya kamu da son ta, sai dai kuma tun daga lokaci na farko day a fara zuwa hira wajen ta yaci karo da mahaifin ta Malam Sada (Ali Nuhu) sai hankalin Hafiz ya tashi, domin ya taba cin zarafin Malam Sada ya ture shi da mota har yaji masa rauni kuma ya soma kokarin dukan Malam Sada din.

Ko da Hafiz ya fahimci cewar Malam Sada ne mahaifin Safna sai hankalin shi ya tashi amma son da yake mata ne yasa ya kasa hakuri da ita yayi yunkurin turo iyayen sa, sai dai kuma Malam Sada yaki yarda da auren Hafiz da Safna saboda wulakancin da Hafiz din yayi masa. Ganin yadda Hafiz ya rikice akan son Safna ne hakan yasa iyayen sa suke takaici saboda ba ‘yar masu kudi ya nema ba, amma son da suke yiwa Hafiz ne yasa suka yi ta kokarin ganin cewar an daidaita da mahaifin Safna, ana cikin haka kuma sai aka tashi mahaifin Safna wato Malam Sada daga gidan da yake haya, hakan ne yasa ya hada kan iyalan sa gaba daya ya koma kauye, duk da kafin tafiyar shi, mahaifin Hafiz yayi masa tayin muhalli amma Malam Sada yaki amincewa domin shi mutum ne me zafin zuciya da gudun abin hannun wasu.

Ko da Hafiz ya samu labarin cewa Safna sun koma kauye sai ya gujewa iyayen sa ya tafi kauyen su Safna don neman soyayyar ta. Bayan zuwan Hafiz kauyen ne da yadda yake yin wahala sai abin ya soma bawa Malam Sada tausayi wato mahaifin Safna har daga karshe ya amince da nadamar Hafiz sannan ya bawa Hafiz din dammar turo magabatan sa don ya aura mishi Safna.

Abubuwan Birgewa:

1. Labarin ya tafi kai tsaye zuwa ga sakon da ake son isarwa sannan an nuna tsantsar soyayya muhimmancin da jajircewa kan abinda mutum yake so.

2. Daraktan fim din yayi kokari wajen tafiyar da labarin bisa tsari ba tare da ya karye ba, haka kuma yayi kokari wajen ganin jaruman sun taka rawar da ta dace, domin jaruman sun yi kokari sosai.

3. Sauti ya fita radau, hoto ma ba laifi

4. An yi kokari wajen samar da wuraren da suka dace da labarin.

5. Wakokin fim din sun yi dadi kuma sun nishadantar.

Kurakurai:

1. Lokacin da Malam Sada (Ali Nuhu) yaje neman rancen kudi a wajen wani me kanti, da kuma lokacin daya dawo gida sa’in da akayi masa rauni a kafar sa, muryoyin jaruman basu hau da bakin su ba a wuraren.

2. An nuna cewar iyayen Hafiz masu kudi ne kuma suna nuna masa gata da tsantsar kulawa, amma kuma lokacin da Hafiz ya gujewa iyayen na sa ya tafi kauye wajen masoyiyar sa, me kallo bai ga sun yi yunkurin neman shi ba. Ya dace a nuna cewar sun watsa cigiyar sa ko da ta kafafen sadarwa ne.

3. Me kallo yaga Hafiz ya taso cikin gata da sangarta daga wajen iyayen sa, wanda hakan ya ba shi damar da ya ke cin mutuncin duk wanda ya so, musamman na sama da shi, amma sai ga shi kuma lokacin da Hafiz ya gane kuskuren da yayi wajen cin zarafin Malam Sada mahaifin budurwar sa, wanda har Hafiz din ya bar gaban iyayen sa don neman soyayya da kuma yafiyar mahaifin budurwar tasa, duk da ganin faruwar hakan amma ba a nuna cewar iyayen Hafiz sun yi nadama ba a bias tafarkin da suka dora dan nasu na rashin tarbiyya, ya dace a nuna cewar sun yi nadama ko don ganin illar da rashin tarbiyya ta ja wa Hafiz wanda abin ya zamo sanadin da Hafiz ya nisance su.

4. Shin wace irin sana’a mahaifin Hafiz yake yi ne? An nuna cewar Hafiz ya taso cikin gata da tunkaho da dukiyar mahaifinsa, sai dai kuma har fim din ya kare ba a nuna irin sana’ar da mahaifin nashi ya ke yi ba wadda ta sa ya mallaki dukiya me tarin yawan da a ke fada.

MAKALOLI MASU ALAKA:

Karanta Kurakurai 4 da akai a cikin Film din NAMIJIN KISHI tare da Sharhin Fim din

Karanta Kuskure 5 da akai a cikin Film ɗin MATAR MAMMAN tare da Sharhin Fim ɗin

Karanta Kuskure 7 da akai acikin Film din KANWAR DUBARUDU tare da Sharhin Fim din

Karkarewa:

Fim din ya fadakar kuma labarin ya yi nasara wajen rike mai kallo, sannan kuma an nuna tsantsar soyayya gami da muhimmin darasi a kan wasu matasan masu ji da giyar kudi, wanda hakan ke sa wa su wulakanta makaskanta, yayin da daga karshe su ke yin nadama a kan hakan. Wallahu a’alamu!

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



Source: LEADERSHIP A YAU 

Sunday, 31 December 2017

Karanta Kaji: Shin ko kasan Fina-finan Kannywood 12 da suka shahara?

Karanta Kaji: Shin ko kasan Fina-finan Kannywood 12 da suka shahara?

Duk da babban kalubalen matsalar satar fasaha da masana'antar finafinan Kannywood ke fuskanta, amma an fitar da fina-finai da dama a cikin shekarar 2017, da suka kunshi masu kayatarwa da marar kyau da matsakaita.

Kuma kafin shekarar ta kawo karshe ana sa ran fitowar wasu sabbin fina-finai, kamar Juyin Sarauta, Sabon Dan Tijara, Dan Sarkin Agadaz, Mu Zuba Mu Gani, Dan Kuka a Birni da dai sauransu.

Don haka daya ko biyu daga cikinsu na iya shiga sahun Fina-finan 2017.

1. There's a Way

Ana ganin wannan ne Fim na Inglishi na farko a masana'antar Kannywood, wanda furodusansa shi ne babban malamin Ingilishi Kabiru Jammaje, sannan Falalu Dorayi a matsayin darakta.

Fim din ya bayar da labari ne akan gwagwarmaya tsakanin masu karamin karfi da attajirai. Fina-finan Kannywood 12 da suka shahara a 2017
An fito da halayyar wasu 'ya'yan attajirai a Jami'a da kuma rayuwar mata, wanda a haka aka tsara labarin.

Soyayya ce tsakanin Isham (Nuhu Abdullahi) Dan talaka amma hazikin dalibi da kuma Fadila (Hajara Jalingo) 'yar wani babban hamshakin attajiri Alhaji Mahdi (Sani Mu'azu) wanda ba ya kaunar hada zuri'a da talaka inda ya bi duk hanyoyin da zai bi domin ganin ya raba su.

Ana sa ran This is the Way, zai fito kafin karshen shekara. Raunin Fim din shi ne karshensa da kuma amfani da salon harshe mai sarkakiya.

Amma tsarin fim din baki dayansa ya kayatar wanda hakan martani ne ga sukar da ake wa masu shirya finafinan Hausa cewa jahilai ne, da ba su iya da turanci ba.

2. Umar Sanda

Kamal S. Alkali ne Daraktan Fim din, labarin ya mayar da hankali ne a kan mai ra'ayin rikau Umar Sanda (Ali Nuhu) da iyalinsa.

Ko da yake ma'aikaci ne, kuma yana kokarin ganin iyalinsa na cikin wadata. Ana zaman lafiya har zuwa lokacin da 'yarsa ta hadu da wani abokin karatunta Dan shugaban 'Yan sanda da aka shagwaba, wanda kuma ta kashe shi a kokarin kare kanta.

Umar Sanda ne ya binne gawar a yayin da 'yan sanda ke bincike mai tsauri.
Duk da cewa an kwaikwayi fim din ne daga wani fim na Indiya, amma yadda aka tsara shi zai iya kasancewa daya daga cikin mafi shahara a bana. Ya nuna girman gaskiya da hadin kai da dabi'u masu kyau.

3. Ankon Biki

Ali Gumzak ne daraktan Fim din, kuma Ankon Biki ya mayar da hankali ne a kan muhimmin batu da ake fuskanta a yanzu.
Mubarak (Adam Zango) da Fa'iza (Sadiya Bulala) suna shirin aure, sai Fa'iza ta kawo batun "Anko" da bukatar a hada wani babban bikin kasaita a wani wuri mai tsada.

Mubarak da abokansa sun yi iya kokarin ganin sun biya bukatar Amarya da kawayenta amma sun gagara, amma Amaryar ta dage a kan bukatar har ta bayar da kanta a madadin kudin kama wajen da za a yi bikin.

Ya fasa aurenta a ranar bikin bayan asirinta ya tonu, kuma a madadinta ya auri kawarta ta kud da kud. Fim din ya nuna girman nisan da wasu mata ke dauka don cimma bukatunsu.

Duk da yake wasu wuraren a fitowar fim din na da tsayi amma an yi amfani da Hausa mai kyau da salon magana.
Sauran taurarin fim din sun hada da Hafsar Idris da Umma Shehu da Al Amin Buhari da dai sauransu.

4. Rariya

Yaseen Auwal ne Daraktan Rariya, kuma fim na farko da Rahama Sadau ta dauki nauyin fitowarsa, wato matsayin furodusa.

Labarin Fim din ya danganta tasirin wayar salula ta zamani da ake kira "komi da ruwanka". Fim din ya shafi yadda wasu 'yan matan Jami'a ke amfani da wayar salula domin janyo hankalin maza.

Yadda aka hada fim din ya kayatar. Babban muhimmin abu shi ne yadda daya daga cikin 'yan matan ta banbanta da saura inda har ta yi kokarin kammala karatunta.

Mutane da dama ba za su so haka ba, musamman iyaye da ke da'awar karatun 'ya'ya mata. Amma duk da haka linzamin labarin ya shafi abin da ke faruwa kuma ke shafar jama'a.

Taurarin Fim din sun kunshi Ali Nuhu da Rabiu Rikadawa da Rahma Sadau da Fati Washa da Hafsar Idris da sauransu.

5. Mijin Yarinya

Ali Gumzak ne Darakta, kuma Mijin Yarinya ya shafi labarin wani Dattijo Attajiri Bashir Nayaya (Alhaji).

Wata rana ya ji matansa guda biyu da Allah bai ba su haihuwa ba suna ma shi addu'ar mutuwa domin gadon dukiyarsa kuma don su aure yara samari, su yi sabuwar rayuwa.

Saboda haka ne ya je ya auri budurwa Maryam Yahaya bayan ya saye imanin iyayenta da saurayinta da kudi.

Wannan ne ya fusata manyan 'ya'yansa Aminu Sharif da Sadiya Bulala, inda suka taya iyayensu mata kishi.

Bayan shafe lokaci ana makirci da takaddama, Alhaji ya yanke shawarar sakin dukkanin matansa, hadi da amaryarsa. Fim din na kunshe da darussa masu yawa a yadda aka tsara fim din.

Sabuwar 'yar fim Maryam Yahya ta yi kokari a fim din mai kunshe da gwanaye. Ba tare da zuzutawa ba fim din na cike da ban dariya da ilmantarwa.

6. Kalan Dangi

Wannan ma wani fim ne na barkwanci da Ali Gumzak ya bada umurni wato a matsayin Darakta, Fim din ya nuna yadda talakawa ke neman arziki da kuma attajirai.

Yayin da kuma masu arzikin ke kaskanta Talakawa. Ali Nuhu da Aminu Sharif da Sadiq Sani Sadiq da Jamila Nagudu da Fati Washa da Aisha Tsamiya na rayuwa ne ta nuna arziki da karya da makirci da nuna karfin iko. Idan kana neman nishadantarwa, to ka nemi Kalan Dangi.

Sai dai an raba fim din biyu, na daya da na biyu. Amma an takaita labarin da kuma karshensa, wanda ake sa ran fitarwa a shekara mai zuwa.

Kamar taken fim din Karshen Kalan Dangi zai iya kawo karshen duk wani rikici.

7. Makaryaci

Kamar sauran shahararrun fina-finan barkwanci da aka fitar a 2017, Ali Gumzak ne daraktan Makaryaci.

Sadiq Sani Sadiq ne da Allah ya ba basirar wasan kwaikwayo, ya daukaka fim din a matsayin daya daga cikin fitattu a bana. Labarin Fim din ya shafi yadda kwadayinsa na dukiya ya kai shi ga samun kudi ba tare da ya sha wata wahala ba.

Yakan je ya yi hayar tufafi ya harde cikin babbar motar mai gidan Rabiu Daushe ana tuka shi zuwa wurare har zuwa cikin Jami'a. Yakan yi wa dalibai karyar cewa shi dan gidan minista ne ko ambasada.

A hakan ne ya fara soyayya da daya daga cikin daliban Hafsat Idris. Ba tare da bin umurnin kakanninsa ba, ya je ya kadar da dabbobinsa na gado, domin ya kashe wa budurwarsa kudi wacce daga baya ta gano asalinsa.

Taurarin Fim din sun kunshi Sulaiman Bosho da Mama Tambaya da Mustapha Nabaruska da Musa Maisana'a da sauransu.

8. Husna ko Huzna

Husna (Jamila Naguda da Abdul (Adam Zango) sun shirya yin aure, yayin da kuma Huzna (Fati Washa) ta yi kokarin hana auren saboda matukar son da ta ke wa Abdul.

A yayin da suke hamayya, wata rana Husna ta watsa wa Huzna guba a fuska, ba tare da sanin cewa ashe fatalwa ce. Washegari Huzna ta tafi gidansu ta mallaki Husna.
Wannan ya bude wani sabon babin hamayya tsakaninsu inda Huzna ta shiga jikin Husna kuma ta ci gaba da zama a gidanta. Yadda aka tsara fim din ya ja hankali.

Amma duk da akwai matsaloli da aka samu, Fim din na iya zama daya daga cikin manyan fitattu finafinai a Kannywood.

Fim din dai bai kasance wani abin muni ga mata ba, kamar yadda aka tsara labarin fim din irin na ban tsoro, a rikicin rayuwar aure tsakanin mata don mallakar namiji.
Rawar da Washa ta taka ya kayatar. Falalu Dorayi ne Daraktan Fim din.

9. Burin Fatima

Wasu za su yi mamakin yadda wannan fim ya shigo sahun fitattu. Ya cancanta. Labari ne akan wata matar aure da ta fada tarkon shawarar kawarta.

Aisha Tsamiya tauraruwar fim din ita ce kuma ta dauki nauyin fitowarsa a matsayin furodusa.

Fim din ya ba da labarin wata mata (Tsamiya) da mijinta, Adam Zango a yayin da ta ke makaranta, wata kawarta ta ba ta shawarar ta zubar da juna biyu da take dauke shi don ta samu sukunin karatu.

Ta karbi shawarar kuma ta yi wa mijinta karya cewa cikin ya bare, ba tare da sanin cewa ba ta kara haihuwa ba. Ta fuskanci kalubale daga sarakuwarta kan rashin haihuwa inda ta tursasawa Zango ya kara aure.

Ali Gumzak ne ya bayar umurni a fim din da ba a kashewa kudi ba. Sannan bai samu karbuwa ba.

Amma ba don haka ba da zai kasance daya daga cikin finafinan da suka samu karbuwa ga jama'a.

Wannan dai ci gaba ne ga Tsamiya, kasancewar fim dinta na farko a matsayin furodusa.

10. Mansoor

Fim din Mansoor na FKD yana cikin wadanda ake kururutawa a matsayin gwarzon shekara. Ali Nuhu ne Darakta.
An fara fim din ne da soyayyar wasu matasa daliban makaranta, Maryam Yahaya da Umar M. Sharif.

Amma mahaifin Sharif ne ya kawo karshen abotar, saboda yana zargin Sharif ba ya da uba, wanda wannan ya ba shi kwarin guiwar gudanar da bincike domin gano asalin mahaifinsa, ba tare da sanin cewa ashe gwamnan jiha ba ne mahaifinsa.

Labari ne ya mamaye fim din. Kuma ko shakka babu, fim din ya kasance kamar a zahiri. Baki dayan fim din ya shafi labarin matasan masoya tsakaninsu da iyayensu.
An aiwatar da fim din da kyau.

Taurarin fim din sun hada da Ali Nuhu da Abba El Mustapha da Baballe Hayatu da Teema Yola da dai sauransu.

11 . Dawo Dawo

Fim din Kabuwagawa ne wanda Ali Gumzak ya bayar da umurni.

Dawo-Dawo labari ne game da wasu da suka reni yaro (Adam Zango) tun kuriciya har girmansa inda suka kuma aurar ma shi da 'yarsu (Maryam Gidado).

Amma daren farkon aurensu, amaryar ta yi karyar cewa tana da aljannu, ta tursasa ma shi ya sake ta. Nan take iyayen suka daura ma shi aure da kanwarta (Aisha Tsamiya).
Ita kuma (Gidado) ta koma ga tsohon saurayinta (Zahraddeen Sani) wanda saboda shi ta kulla makircin. Daga baya ya yi watsi da ita, inda ta shiga wani hali ta koma kamar mahaukaciya lokacin da ta fahimci cewa ta dauke da cikin Zaharaddeen.

Fim din na cike da makirci da rikici, kuma taurarin fim din Zango da Tsamiya da Gidado suna yi kokari sosai. Wannan ya sa fim din ya sha gaban takwarorinsa a bana.

12 . Ta Faru ta Kare

Aminu Saira ne daraktan Ta Faru ta Kare, labarin fim din ya shafi rayuwar Hafsat Idris, gurguwa, makauniya amma 'yar attajiri, da kuma Aminu Sharif (Momo) wanda ya aure ta kuma yake cin amanarta yana kawo 'yan matansa a gidanta har zuwa lokacin da dubunsa ta cika.

Inda Adam Zango, abokin wasanta wanda Momo ya yi wa kanwarsa ciki ya yake shi har ya fitar da shi daga gidan.

Fim din na tattare da nishadi. Hafsat Idris da ta fito mai nakasar jiki da kuma Momo sun yi kokari a rawar da suka taka a fim din.

Sauran taurarin fim din sun hada Hadiza Gabon da Hauwa Waraka da sauransu.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki 

Mungode

Source: BBC HAUSA