Showing posts sorted by date for query Datti Assalafy. Sort by relevance Show all posts
Showing posts sorted by date for query Datti Assalafy. Sort by relevance Show all posts

Tuesday, 9 February 2021

Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (3)

Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (3)

A rubutun da ya gabata kashi na biyu na shiga daku cikin ɗakin karuwa, muka kawo bayanin irin ƙazantar dake cikin ɗakin karuwa da ƙazantar dake jikin karuwa, da yadda karuwa take yaɗa cutuka a tsakanin al'ummah musamman mazinata.


Rayuwar Karuwai


Marubuci:- Datti Assalafy


Wannan rubutun zai ta'allaka ne akan yadda karuwa ko karuwai suke ɗana tarko wa attijirai, manyan sarakuna ko 'yan siyasa mazinata domin su dinga samun maƙudan kuɗin shiga masu yawa, Karuwa kaska ce raɓi mai jini, ba dama karuwa ta zauna haka nan sai inda zata samu kuɗi, shiyasa idan karuwa ta tsufa a harkan karuwanci, wato farjinta ya mutu ya gama aiki, bai kawo mata kuɗi yadda ya kamata, sai ta koma harkan Luwaɗi wanda a yanzu shine abinda yafi kawo ma karuwai kuɗi.


Yawanci haka karuwai na wannan zamanin namu suke sun zama 'yan Luwaɗi, to yanzu sun fahimci Luwaɗin ba zai kaisu ba saboda cutar da yake haifar musu, yanzu su fara ɗana tarko wa wasu manyan attajirai, 'yan siyasa da sarakuna da suke harkan Luwaɗi don neman hanyar samun maƙudan kuɗaɗen shiga, zaku gansu suna walwala suna sayen manyan gidaje da motoci masu tsadan gaske, suna kafa kungiyoyin da suke taimakon al'ummah da kuɗin karuwanci suna alfahari dashi.


Saboda cigaban zamani yanzu karuwai sun baza tarko, suna sayan na'urar sirri mai ɗaukar hoto da bidiyo, suna bin manyan 'yan siyasa da attajirai da sarakuna suna lallaɓarsu da suyi zina dasu don su samu damar da zasu ɗauki hotonsu ko bidiyonsu su mayar dasu hanyar neman kuɗi wato natural ATM, a gidajen da karuwai suke ginawa ko su kama haya su shiga; suna saka na'urar ɗaukar hoto da bidiyo ta ko'ina, daga lokacin da ka iso kofar gidan karuwa har zuwa cikin ɗakinta bidiyo ne take ɗauka.


A matsayinka na attajiri mai kuɗi ko babban ɗan siyasa ko babban basarake mazinaci ɗan Luwaɗi kaji tsoron Allah ka tuba ka dena, imba haka ba zaka faɗa tarkon karuwai, ka sani cewa wannan jakar dake hannun karuwa na'urace mai ɗaukar bidiyo baka sani ba, ɗan kunnenta na'urar ɗaukan bidiyo ne baka sani ba, biron dake hannunta, botil ɗin rigar jikinta, kayan jikinta, gashin dokin da ta ƙara a gashin kanta zai iya kasancewa akwai na'urar ɗaukar bidiyo da hoto, burinta kawai ta samu damar kwanciya da kai a hotel, daga nan  ta gama da kai.


Akwai wata shegiya riƙaƙƙiyar karuwa da na sani tana yiwa 'yan siyasa wannan ta'asa, karuwace wanda kwanaki tayi rubutu anan Facebook tace Datti Assalafiy ɗan ta'adda ne yana kira a cire kan mutane lokacin da nayi magana aka kama kafurin yaron nan Mubarak Bala bayan ya zagi Manzon Allah (S.A.W) a shafinsa na Facebook, sai karuwan ta fito ta min ɓatanci wai ni ɗan ta'adda ne, amma ban kulata ba sai na tura yarana suka aika mata da saƙo.


To waɗannan karuwai haka suke, da zaran sun mallaki bidiyon wani ɗan siyasa ko babban basarake sai su fara takama da barazana, suna ganin zasu iya sa a ɗaure kowa, suna alfahari da jiji da kai, kana taɓata sai tace wai ta san manya zatasa a ɗaure mutum igiya sai ya saura, to wannan shine gadaran karuwa, wataƙila tana da hoton gwamnan jiharku yana zina da ita, idan ka taɓata zata kirashi tasa a ɗaure ka ko a ɓatar da kai, saboda shima yana tsoronta don ta mallaki hotonsa yana zina da ita.


Jama'a wannan shine abinda yake faruwa, yau idan alfarma ko haƙƙinka kake nema a gurin waɗannan manyan mutane ba zaka samu ba sai kabi ta hannun karuwa, sai ka shekara guda kana bi amma rana ɗaya karuwan da ta mallaki hotonsa ko bidiyo yana zina da ita zata samu wannan alfarmar a cikin mintuna.


Na rantse da girman Allah na san karuwan da a yanzu haka tana da bidiyon wani babban jigo a siyasar wata jiha a Arewa tsirara haihuwar uwarsa yana zina da ita, na san karuwan da ta mallaki bidiyon wani gawurtaccen jami'in tsaro mai babban matsayi a ƙasar nan, na san karuwan da ta mallaki abubuwan sirri na 'yan siyasa da yawa tana nan tana ta sheƙe ayarta, suna bata maƙudan kuɗaɗe.


DUBA WANNANKaranta Manyan Siffofin 'Yan Luwadi Da Rayuwar Su Cikin Sirri (1)


Waɗannan karuwai annoba ne, suna daga cikin waɗanda suka jefa wasu shugabannin siyasar mu harkan satar dukiyar al'ummah ana basu, karuwa zata jure wahala da wulaƙanci ta fara kamun ƙafa da yaran 'yan siyasa kawalai suma su kwanta da ita, kafin nan su kaiwa Maigidansu, daga nan tayi ta lallaɓar ɗan siyasar har sai ta samu damar kwanciya dashi ta mallaki bidiyo da hotunansa, shikenan buƙatarta ta biya, sai ya dinga ɗaukar dukiyarku yana bata.


Don haka karuwai ta kowace fuska annoba ne, kuma illane da suke cutar da al'ummah, karuwai su dena baku sha'awa yaku bayin Allah, karuwai su dena burgeku.


Yaa Allah Ka karemu daga sharrin karuwai Amin.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin

aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Thursday, 17 December 2020

Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (2)

Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (2)

Mai karatu kayi haƙuri da wasu kalmomi masu nauyi da zaka karanta cikin wannan rubutu na Datti  Assalafiy, idan buƙata ta kama domin a fahimtar da mutane musamman ga waɗanda basu da cikakkiyar fahimta na kalmomi to dole sai an fito da kalmomin a zahiri don a fahimta.


RAYUWAR KARUWAI

Marubuci:- Datti Assalafy


Ita dai Karuwa jakar gayu ce, duk wata karuwa jaka ce, domin yadda jakuna suke taruwa a kan jakanya guda suna jima'i da ita haka karuwa take, zaka samu akwai karuwa guda ɗaya da tayi jima'i da maza sama da dubu a rayuwarta, cutuka sun mata katututu a jikinta, idan ka tambayeta zatace ita rayuwar duniyar sam baya mata daɗi.


Rayuwar karuwai abin ƙyama ne, kuma rayuwa ne na ƙazanta, duk wanka da duk adon da karuwa zatayi ƙazamiya ce sai kaji tana wari da ƙarni, kuma yawanci karuwai ba sa yin wanka sai dai kwaskwarima sakamon cuɗanya da take da mazaje mabanbanta, wato warin da karuwa keyi yana bi har jinin jikinta, da kuma kasancewar miniyyi na mazaje mabanbanta dake shiga cikinta, shi yake haddasa mata irin wannan warin.


Karuwa bata da kunya, duk wani abu na rashin kunya da rashin mutunci karuwa zata iya aikatawa, duk wani marar kunya bashi da imani da faɗin Manzon Allah (S.A.W) imani bai zama a jikin mutumin da bai da kunya, hakanan kunya bai zama a inda babu imani, imani da kunya a haɗe suke, idan anaso ayi ma wani mutumin kirki sharri sai an haɗa da karuwa, na san wani Limamin Masallaci da aka shirya masa tuggu da wata karuwa, idan ya fito da asuba zai je masallaci ta rungumeshi ta sa ihu, da ƙyar Allah ya kubutar da limamin.


Karuwa kamar akuya take, dole tayi yawo tsirara domin ta janyo hankalin mazinata, dole ta sayi kaya masu bayyana tsiraici taje daƙin hoto a ɗauke ta a hoto ayi mata kwalliya a Photoshop Application wanda zata dinga ɗaurawa a kafofin sada zumunta na yanar gizo domin ta nemi kwastoma da abokan zina, kunga ta zama akuya.


Karuwa ƙazama ce, bata wanka, kun san yanayin jima'i musamman a lokacin zafi, ana yin zufa sosai idan ana yin jima'i, zufan jikin mutum yana ɗauke da cutuka, ko a binciken Likitanci ana so da zaran an kammala jima'i aje ayi tsarki da kuma wanka, amma karuwa bata wannan, zata share farjinta da tsumma ne, wani na waje yana jira, na ciki na fitowa na waje zai shiga ya ɗaura, kuma dole fatar jikinsu ya haɗu ko da sun sa kororon roba, anan zai kwaso cuta yaje ya yaɗawa iyalinshi ko abokanshi, shiyasa taɓa jikin mazinaci bai dace ba, domin zai iya yaɗa cuta da ya ɗauko daga jikin karuwa.


Karuwa kullun a cikin rayuwar takuri take da kuma ƙunci, shiga cikin ɗakin karuwa ka gani, ɗakine ɗan ƙarami tsukakke sai wari da hamami duk da ta kunna turaren wuta, zagaya gurin da suke wanka, babu wani tsayayyen toilet, idan wanka zatayi haka nan zata tsaya daga bakin ɗakinta ta watsa ruwa, ko bawali zatayi sai dai tayi a cikin baƙin leda a cikin ɗakinta ta goge da tsumma ta jefar a kwalbati, idan fitsari zatayi sai dai tayi a cikin bokiti ta fita waje ta watsar, haka mazinaci zai zo ya yabi guntun kashi da fitsari a jikin karuwa.


Ina mazinata masu zuwa gidan karuwai suna zina? Ku sani cewa yanzu matsafa suna amfani da maƙudan kuɗaɗe suna sayen miniyyin mazinata daga hannun karuwai suna tsafi da shi, wato maniyyin da aka zuba a cikin kororon roba, wanda idan mazinaci ya gama zina da karuwa zata cire ta saka a bokiti, da zaran an tafi da maniyyinka kamar sun tafi da ruhinka ne, za'ayi tsafi da kai a bayar da rayuwarka wa baƙaƙen aljanu, ko su nakasa rayuwarka, ko kuma su rabaka da duniya, wannan sabon abune da ya bayyana.


Mai son sanin wasu daga cikin sirrukan 'yan Luwaɗi ya je yayi hira da karuwai masu zaman kansu, musamman magajiyar karuwai, nemi kuɗi kayi mata kyauta zata lissafa maka manyan mutane a garinku waɗanda suke 'yan Luwaɗi, domin yanzu karuwan da tafi sauran karuwai kawo kuɗi itace karuwan da ake Luwaɗi da ita, akwai mazan da a yanzu ba suna zina da karuwai ta farjin su bane, haka nan ba suna auren mace don jima'i da ita ta farji ba, sai dai ta dubura.


Jama'a ku dena ganin waɗannan manyan 'yan mata 'yan boko masu zaman kansu a Abuja da sauran manyan birane suna sayan manyan gidaje masu tsada, suna hawa mota masu tsada, suna hawa jirgin sama su ɗauki hotuna suna fita ƙasashen waje suna yiwa mutane kallon ƙasƙanci da wulaƙanci, suna kafa kungiyoyin tallafawa marayu suna alfahari dashi don su yaudari al'ummah, wallahi yawancinsu riƙaƙƙun karuwai ne da ake Luwaɗi da su, domin yanzu fa zina bai kawo kuɗi sosai sai Luwaɗi.


To ƙarshen duk wata karuwa cutar kansa ne mai kisa, saboda irin mayukan shafawa da sabulun wanka masu ɗauke da sinadari da suke amfani da shi, da kuma miyagun ƙwayoyin da suke sha, anan cutar kansa zata kamasu, ba zai rabu da su ba sai sun mutu.


DUBA WANNAN: Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (3)


Don haka rayuwar  karuwa sam ba abin burgewa bane, kuma ba abin sha'awa bane, domin ƙarshen duk wata karuwa mai zaman kanta, ko wanda take gidan iyayenta, ko wanda take gidan kanta shine yin mummunan ƙarshe na wulaƙanci.


Ina muku albishir da wani rubutu da zan wallafa mai taken MUMMUNAR MANUFAR YAHUDAWA AKAN MATA rubutune mai matuƙar fa'idah, kada ku bari a baku labari.


Ina roƙon Allah Ya kare matan Musulmi daga faɗawa harkan karuwanci, Allah Ka tsaremu Ka tsare mana imanin mu Amin.


Zamu Ci gaba Insha Allah.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin

aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Tuesday, 13 October 2020

Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (1)

Karanta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (1)

Karuwanci tsohowar sana'ace ta iskanci da lalata wanda ya shafe shekaru masu yawa yana wanzuwa a duniya, mace ta mayar da farjinta gurin neman kuɗi, ta guje wa yin aure tana karuwanci a gida, ko ta tare a gidan haya tana sana'ar ta na karuwanci, ko matar aure mai cin amanar mijinta tana karuwanci.


Rayuwar Karuwai Cikin Sirri


Marubuci:- Datti Assalafy


Abubuwa da yawa ke jefa mata sana'ar karuwanci suna da yawa, amma manya daga cikinsu shine rashin tsoron Allah da rashin tawakkali, wasu saboda talauci da rashin haƙuri, auren dole, buri da kwaɗayin abin duniya, rashin sanin hatsari da ƙarshen makomar duk wata karuwa ko mazinaciya.


Rayuwar karuwa cikin sirri rayuwa ne na takaici, rayuwa ne na ƙazanta, rayuwa ne na cututtuka, rayuwane na rashin kunya da rashin imani, rayuwa ne na rashin daraja da rashin albarka, kuma rayuwa ne na ƙasƙanci da wulaƙanci, rayuwa ne na tsadar rayuwa, rayuwa ne na tsageranci walau ga karuwan da take karuwanci a gaban iyayenta, gidan mijinta ko karuwan da take karuwanci a gidan haya ko gidan da ta gina tana zaman kanta.


Duk wata karuwa mai zaman kanta kullum a cikin takaici da ɓacin rai take, hankalinta yana ga kwastomomi, duk wanda yazo ƙazami ne ko mai tsabta zata bashi jikinta indai yana da kuɗi, ga rashin daraja, alade ma yafi karuwa daraja, mai son tabbatar da wannan ya lura da yadda ake yiwa karuwa idan ta mutu a gidan karuwai.


Karuwa kullun a cikin tsadar rayuwa take, kuɗin da take samu baya mata albarka, saboda kuɗi ne da aka sameshi ta ƙazamiyar hanya, kullum a cikin sayan sutura da mayukan shafawa masu tsada take domin ta yiwa jikinta kwalliyar da zata janyo hankalin kwastomomi, duk wata karuwa ɓarauniya ce kuma maƙaryaciya, karuwa tana samun dama zatayi sata, ga ƙarya kamar aljana, zaku ga karuwai yanzu sunci gaba suna yaɗa hotunansu har a kafafen sada zumunta suna ƙarya da damfara, yanzu sun ɗan samu sauƙi saboda application na ado da kwalliya da suka bayyana a playstore.


Karuwa kullum a cikin jinya da cuta take, babu wata karuwan da take da lafiya kowacece ita, kuma karuwa ta fi komai da kowa yaɗa cuta mai hatsari ga lafiyar mutane, da zaran karuwa ta lura da lokacin jinin al'ada na zuwa mata sai tasha kwayoyin da zai hanata jini, wanda hakan cutarwa ne ga lafiyar jikinta, dole karuwa mai zaman kanta zata dakatar da jinin al'ada don tayi karuwanci ta samu kuɗin sayen abinci da biyan haya.


Daga cikin cuta da karuwai ke haifarwa kanta shine: Allah cikin hikimarSa bai halicci jikin mace don ta dinga karɓan miniyya daga maza mabanbanta ba a lokaci guda, sai dai ga namiji shi kaɗai, macen da maza da yawa suke jima'i da ita a tsakanin kwanuka ko a lokaci guda suna zuba mata miniyya yana bin jikinta; to hatsari ne ga lafiyarta, wannan bincike ne da ilmin Likitancin zamani ya tabbatar.


Na daga cikin dalilan da ya sa Allah Maɗaukakin Sarki yace mace ta auri namiji ɗaya, ba kamar yadda Allah Ya bawa maza damar auren mata har huɗu don ya rayu da su a lokaci guda ba, idan ya kasance mace zata auri maza biyu na farko za'a iya samun saɓani tsakanin mazajenta idan ciki ya shiga, na biyu miniyyinsu da yake shiga jikinta a lokaci guda illa ne ga lafiyar jikinta, wanda masana ilmin kiwon lafiya suka gano hakan.


Yanzu karuwai ɗin sunci gaba, suna da kayan gwajin cutar ƙanjamau, kwastoma na zuwa zata gwadashi idan yana son yin jima'i fata da fata (skin to skin), wanda ba sai mazinacin ya sa kwaroron roba ba, amma wannan karuwan tana da tsada, karuwai ɗin kuɗi-kuɗi ne kuma mataki-mataki, mafi rashin darajar karuwanci itace karuwan Naira 200 a yanzu, wannan ga wanda ta kusa zama guzumar karuwai kenan, cututtuka sun mata yawa a jika, tana neman abokin tafiya lahira.


DUBA WANNANKaranta Manyan Siffofin Karuwai Da Rayuwar Su Cikin Sirri (2)


Wanzuwar karuwai a cikin al'ummah ya taimaka wajen lalata tarbiyya da ƙaruwar munanan laifuka da ta'addanci, gidajen karuwai da manyan hotels da ake karuwanci ya zama babbar mafaka ga tsageru, jami'an tsaro sunsha bin diddigin manyan ɓarayi da masu garkuwa da mutane suna kamasu a gidajen karuwa da kuma hotel.


Zan cigaba a rubuta na gaba, zan shiga daku gidan karuwai, hotel  ɗakin karuwa kuji abinda yake wakana idan mazinaci yazo zaiyi zina da kuma bayan ya gama zina, zan kawo muku labarin wasu cases na karuwai da kashe-kashen da sukayi a junansu.


Zamu Ci gaba Insha Allah.


Allah Ka shiryar da karuwai mata da maza, Ka tsare al'ummar Musulmi daga sharrinsu Amin.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin

aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.


Friday, 20 December 2019

'YAN AREWA SUN KAFA TARIHI A YANKIN KUDU MASO KUDANCIN NIGERIA SUN GINA JAMI'AR KIMIYA DA FASAHA

'YAN AREWA SUN KAFA TARIHI A YANKIN KUDU MASO KUDANCIN NIGERIA SUN GINA JAMI'AR KIMIYA DA FASAHA

Wannan shine hoton ginin katafariyar cibiya na horarwa a kan fasahar sadarwa wanda hukumar NITDA ta gina a cikin jami'ar jihar Rivers dake birnin Fatakwal, kwanaki biyu da suka gabata Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami yaje ya kaddamar da cibiyar a madadin gwamnatin Nigeria.

Yayin Bude Makarantar Kimiya da Fasaha


Marubuci: Datti Assalafy

Abin farin ciki garemu masoya Malam Dr Isah Ali Ibrahim Pantami, shine mutum na farko da ya fara gina wannan katafariyar cibiya a tsakiyar kudu maso kudancin Nigeria, sannan sai amintaccensa wato Malam Kashif Inuwa yazo ya karasa, wannan wani abu ne na tarihi.

An yiwa cibiyar lakabi a turance da "The Information Technology Innovation and Incubation Park Building" an kashe miliyoyin Naira kafin a gina cibiyar, mutanen yankin kudu maso kudancin Nigeria gaba dayansu sune zasu amfana da cibiyar.

Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Pantami a gurin kaddamar da cibiyar yace; lokacin da nake shugabancin hukumar NITDA, shugabanta na yanzu Kashif  Inuwa yana matsayin mai bani shawara akan harkokin gudanarwan ma'aikatar, na kawo batun gina irin wannan cibiya a kusurwa shida na fadin tarayyar Nigeria ta yanda za'a samarwa matasa aiki, a farfado da tattalin arzikin kasa.

Yayin Bude Makarantar Kimiya da Fasaha

Maigirma Ministan yayi la'akari da gurin da yafi dacewa a fara gina wannan cibiya saboda yawan masana'antu da yankin ke dashi, wanda zai inganta tattalin arzikin Nigeria, sai ya fara a yankin kudu maso kudancin Nigeria ba tare da la'akari da ya fara a yankinsa ba, saboda kyakkyawar manufa da kishin Nigeria.

Ministan yaci gaba da cewa, na tabbata idan aka gudanar da wannan cibiya bisa gaskiya da rikon amana yadda ya dace, cibiyar zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Nigeria, shugaban Kasa Buhari yayi alkawarin yin adalci a kowani sassa na Nigeria, shiyasa hukumar NITDA zata tabbatar da wannan muradi na shugaban kasa wajen gina irin wannan cibiya a kusurwa shida na fadin tarayyar Nigeria.., inji Ministan

A nasa jawabin, shugaban hukumar bunkasa fasahar sadarwan zamani na Nigeria (NITDA) Malam Kashif Inuwa  a gurin kaddamar da cibiyar, yace an gina wannan cibiyar ne a cikin jami'ar Portharcourt don daliban ilmi, manyan masana'antu da kanana, 'yan kasuwa da sauransu akan manufa na inganta tattalin arzikin Nigeria .

Malam Kashif Inuwa yaci gaba da cewa, gwamnatin tarayyar Nigeria karkashin shugabancin Muhammad Buhari tun a shekarar 2016 ta kafa kwamitin kwararru a harkokin kasuwanci da aka yiwa lakabi da "Presidential Enabling Business Environment Council" tare da taimakon bankin duniya (World Bank) domin kwamitin ya cimma matsaya akan abubuwa guda uku, na farko; a farfado da tattalin arzikin kasa, na biyu: a gina hanyoyin inganta tattalin arzikin kasa, sannan a gina al'umma.

Gwamnati ta fahimci cewa kimiyyar fasahar sadarwan zamani zai iya kawo mafita ga matsalolin tattalin arzikin kasa, shiyasa ta bada muhimmanci a kai, a sakamakon haka, yanzu bangaren bunkasa fasahar sadarwa a Nigeria ya wuce man fetur da gas wajen inganta tattalin arzikin kasa.., a cewar Malam Kashif Inuwa shugaban hukumar bunkasa fasahar sadarwan zamani na Nigeria (NITDA).

MAKALOLI MASU ALAKA:

Kalli Yadda Soyayya ta sa Wani Bawan Allah ya Sauya Sunan Shi Zuwa na Shugaban Kasa Muhammadu Buhari

Kalli Yadda Wani Dan Sanda Ya Harbi Wani Matashi Dalibin Computer Science Har Lahira

SHIN TA YA YA KAKE JIN MAGANAR DA WANI KE FURTAWA?

Ina kira ga 'yan uwana na arewacin Nigeria mu dinga sanya wadanann bayin Allah cikin addu'ah na fatan samun nasaransu, manufarsu mai kyau ce, babu shakka akan sun rike amanar da shugaba Buhari ya damka musu da gaskiya.

Muna rokon Allah Ya daukaka darajarsu, Ya sa dukkan jama'ar  Nigeria su amfana da rayuwarsu Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode





Friday, 15 November 2019

KARANTA SHARHIN DATTI ASSALAFIY AKAN BAYANIN SARKIN KANO GAME DA SACE YARAN MUSULMAI

KARANTA SHARHIN DATTI ASSALAFIY AKAN BAYANIN SARKIN KANO GAME DA SACE YARAN MUSULMAI

Wannnan rubutun ba raddi bane, sharhi ne da tunatarwa ga Mai martaba Sarkin Kano Malam Muhammadu Sunusi II, game da batun da yayi na cewa da yana da iko da ya kama iyayen da suka bari inyamurai suka sace yaransu, saboda wai sakaci ne a fahimtar Sarki Muhammadu Sanusi .

Sunusi II

Marubuci: Datti Assalafy

A fahimtata wannan maganar da Mai martaba yayi babban kuskure ne da tuntuben harce, iyayen nan da aka sace musu yara akaje aka canza musu addini da suna aka sayar dasu don aikin bauta, a tawa fahimtar basu cancanci irin wannan kalamai daga Mai martaba ba, saboda suna fama da radadin ciwon zuci da kuma bakin ciki, don haka bai kamata a musu barazana da cewa Sarki zai kamasu ba!

Batun garkuwa da mutane a Kasarnan Nigeria; tarihi ya nuna; tarihi ya tabbatar da cewa inyamurai sune suka fara yin garkuwa da safarar mutane a Nigeria, daga baya suka koyawa 'yan Arewa, duk wani mugun aiki da mugun laifi inyamurai suka fara aikatawa a Nigeria, don haka tsohuwar sana'arsu ce wannan.

Sannan a Nigeria babu wanda yafi karfin ayi garkuwa dashi, domin har babban jami'in tsaro wanda ya taka matsayin GENERAL a gidan soji anyi garkuwa dashi aka hallakashi, an taba yin garkuwa da soja mai mukamin Kanar aka hallakashi, an taba yin garkuwa da babban jami'in 'dan sanda mai mukamin mataimakin Kwamishinan 'yan sanda kwanannan aka kubutar dashi, ko wata guda ba'a yi ba.

Ba da dadewa ba akayi garkuwa da babban basaraken gargajiya magajin garin Daura, an saceshi tun daga garin Daura aka kawoshi cikin birnin Kano, birnin Sarki Muhammadu Sanusi II aka boyeshi kusan wata biyu, daga bisani jami'an 'yan sanda suka kubutar da shi a hannun masu garkuwa da shi.

Wannan yana nuna mana cewa hatta su kansu manyan jami'an tsaro masu rike da makami na tsaron rayukan 'yan Nigeria basu fi karfin ayi garkuwa da su ba a Nigeria, haka suma manyan sarakunan gargajiya masu daraja ta farko ba su fi karfin ayi garkuwa da su ba, to balle kuma 'dan talaka wanda babu mai gadinsa sai Allah, babu fadawa da suke gewaye dashi, babu jami'an tsaro dauke da bindigogi da suke gadinsa a gida da duk inda zai je.

Masu hikimar magana sunce; duk wanda yake son kayanka ya fika dabara, masu garkuwa da mutane ko masu satar yara basa kama mutum ko satar yara lokaci guda face sai sun kiwaci mutum ko yaran da zasu sace, yaran nan suna fita daga gidan iyayensu su tafi makaranta, iyayensu suna iya aikansu waje, lokacin da za'a sace yaransu ba su sani ba, kuma haka kawai da gangan iyaye ba zasu bari a tafi musu da yara ba, ko karuwa ce da ta yadda tayi cikin shege ba zata yarda da wannan ba, balle iyayen da sukayi auren sunnah.

DUBA WANNAN: Shin dagaske Ne duk 'Yam Matan Jami'a Lalatattu Ne?

Na tabbata yaran da Mai martaba Sarkin Kano Malam Muhammad Sunusi ya haifa idan zasu fita daga gida sai da rakiyar jami'an tsaro ko fadawa don su samu kariya daga miyagun mutane, yaran talakawa fa? wa yake rakasu idan zasu fita daga gida?

Allah Ya jikan Al-marhum, Al-mufassir shahid Insha Allah Sheikh Ja'afar Mahmud Adam Kano, Malam Ja'afar yayi wasu maganganu game da Sarki Muhammadu Sanusi II akan mas'aloli irin wannan tun kafin ya zama Sarkin Kano lokacin Malam Ja'afar yana raye, to amma ni Datti Assalafiy zan iya yiwa Mai Martaba Sarki Muhammadu Sanusi II uzuri akan cewa; "Dan Adam mai iya canzawa ne a kowani lokaci", iyakarta kenan! imba haka ba da sai nace Malam Ja'afar Kano ya hutar dani game da haskaka mana waye Sarki Muhammadu Sunusi II

Allah Ya jikan Sheikh Ja'afar
Allah Ya taimaki Sarki Muhammadu Sanusi II Ya bashi ikon fadin daidai da aikata daidai Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



ALLAHU AKBAR: Shin Kana da Abinda Zaka iya Saka ma Mahaifiyar Ka dashi a Duniya?

ALLAHU AKBAR: Shin Kana da Abinda Zaka iya Saka ma Mahaifiyar Ka dashi a Duniya?

Abinda na karanta ya RATSA duk jikina.

Tun kana cikin mahaifiyarka Allah Ya kareka daga dukkan cuta, ya saka maka hanyar abincin ka ba tare ka sha wahala ba.

Mahaifiya da Yaron ta

Marubuci: Datti Assalafy

Mahaifiyar ka tayi naƙuda tana zufa, ihu, kuka da hawaye, kana fadowa duniya cikin radadin zafin haihuwa zata yi murna tana murmushi tana godiya ga Allah da Ya baka ikon fitowa lafiya.

Bayan an haifeka sai Allah ya janyo maka jijiyoyi guda biyu a kirjin mahaifiyarka da suke dauke da mafi tsaftar tatacciyar madara, mai dumi a lokacin sanyi, mai sanyi-sanyi a lokacin zafi, don ka sami hanyar yin ƙoto.

Ka shigo duniya baka da ƙwayar haƙori, daga lokacin da hakori ya fara fito maka kake fara azabtar da mahaifiyarka dashi, amma ko da yaushe tana murna tana nuna wa jama'a tana cewa yarona ya fara hakora.

Kayi mata tunbudi, kashi, fitsari ta wanke ba tare da ta taba ko yatsina fuskarta ba, ka hanata bacci ka hanata sukuni amma tana murna tana yarona akwai shi da kuzari.

Daga lokacin da ka sami kafa wata zubin da kyar ake iya sanin inda kake, mahaifiyarka bata koshi sai ta tabbatar da koshinka, bata sukuni da walwala sai ta ganka cikin walwala.

Shin Kana da abinda Zaka iya saka mata dashi?

Duk wanda mahaifiyarsa ta rasu muna roka mata rahmar Allah.

MAKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA KADAN DAGA CIKIN MUNANAN HALAYEN DA SUKE CUTAR DA AL'UMMA GABA DAYA CIKIN GAGGAWA

ALLAHU AKBAR: TAYI NASIHA MAI RATSA ZUCIYAR DUK WANI MAI IMANI JIM KADAN TA RASU

HANKALI NA YANA TASHI IDAN NA TUNA DA WANNAN

Wanda iyayensa ke raye muna fatan za'a kyautata musu fiye da kowa a duniya.

Allah Ka gafarta mana Ka bamu ikon cikawa da kyau da imani Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku.

Isar da bayanai akan lokaci ba tare da son
zuciya ba shine muradin Mu.

Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke.

Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.


Mun kudiri aniyar tsage gaskiya dalla-dalla , sharhi mai gansarwa da suka hada da
harkokin yau da kullum da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode



Wednesday, 2 October 2019

KARANTA TARIHIN YADDA TURAWA SUKA AZABTAR DA AL'UMMAR YANKIN AREWACIN NIGERIA

KARANTA TARIHIN YADDA TURAWA SUKA AZABTAR DA AL'UMMAR YANKIN AREWACIN NIGERIA

A shekarar 2010 watarana da yamma na ziyarci gidan kakana na wajen mahaifi, muna hira sai na kalli tafin kafarshi, nace masa amma Kaka wannan kafar taka tasha duniya, sai yayi dariya, ya fara bani tarihi kamar haka.

Turawan Mulkin Mallaka

Marubuci: Datti Assalafy

A lokacin turawan Mulkin Mallaka kaf cikin garin Bauchi babu inda ake siyar da kananzir (Kerosene) sai anje garin Jos ake samu, turawan mulkin mallaka suna aikamu daga Bauchi zuwa Jos mu je mu saya musu kananzir da kafa mu dawo.

Kakana yace min suna tafiyar kwanaki shida su je Jos su sayo kananzir su dawo, tafiya kwana uku, dawowa kwana uku, wannan itace misalin azabtarwan da turawa suka yi ga kakanninmu.
Kakana ya rasu a shekarar 2012 yana da shekaru 109 Allah Ya gafarta masa.

Lokacin ina sakandare, bana manta tarihin da Malamanmu suka bamu akan irin azabtarwan da turawa suka yiwa kakannin mu da yadda suka sace tattalin arzikin Nigeria suka gina Kasarsu.

Sun yiwa kakanninmu mafi munin bautarwa da wulakanci, ba su yarda cewa bakin fata halittace ta dan adam ba, shiyasa suka bautar dasu kamar dabbobi, ance idan suka turasu gona noma baka isa ka tashi tsaye wai don ka huta ba, idan ka tashi bature zai kiraka, ya sa ka zare harcenka, sai ya sa almakashi ya datse maka harce a matsayin horo.

Lokacin da turawan mulkin mallaka suka fara jigilar kakannin mu a jirgi zuwa turai aikin bauta, yadda ake jera kifin sadin a cikin kwali wani na kan wani haka turawa suke yiwa kakannin mu, wanda ya isa da rai shikenan, wanda ya mutu sai a jefashi ruwa, ya zama abincin kifaye da dabbobin ruwa.

Turawan mulkin mallaka sun yiwa kakannin mu kisan kai yadda suka ga dama, sunyi sata iya son ransu, sannan sun yiwa mata fyade na wulakanci.

Yadda 'yan ta'adda suke kwantar da mutane su yanka kamar rago, ko su harbe da bindiga, haka turawan mulkin mallaka suka yiwa kakannin mu, Kakannin mu zasu yi noma a gonakinsu bature idan ya gani sai yace ya zama nashi.

Ya kamata ace gwamnatin Nigeria ta mayar da wannan ranar a matsayin ranar tunawa da 'yan mazan jiya, wadanda suka sadaukar da rayukansu suka ceto kakanninmu daga kangin bauta na turawan mulkin mallaka.

DUBA WADANNAN:

Karanta Sharhin Manyan Masifu Da Bala'in Dake Kunshe Cikin Rayuwar Gidan Yari

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN KAFUWAR BIRNIN KANO A AREWACIN KASAR NIGERIA

SHIN DA GASKE NE NIGERIA TA KUBUTA DAGA MULKIN MALLAKA?

Muna rokon Allah Ka jikan Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto, Sir Abubakar Tafawa Balewa da makamantansu Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








Tuesday, 1 October 2019

SHIN DA GASKE NE NIGERIA TA KUBUTA DAGA MULKIN MALLAKA?

SHIN DA GASKE NE NIGERIA TA KUBUTA DAGA MULKIN MALLAKA?

Yau Talata 1-10-2019 Kasar mu Nigeria ta cika shekaru 59 da samun 'yancin kai a shekarar 1960 daga turawan Mulkin Mallaka.

Ranar Samun 'Yancin Kan Nigeria daga Turawan Mulkin Mallaka

MarubuciDatti Assalafy

Ina amfani da wannan damar wajen taya 'yan uwana 'yan Nigeria murna da farin ciki.

Sai dai a zahirin gaskiya har yanzu Nigeria da wasu kasashen nahiyar afirka ba su kubuta daga mulkin mallaka na turawa ba, domin kuwa turawa sun zamanantar da mulkin mallaka a wannan karnin ta hanyar kawo tsarin mulkinsu Demokaradiyyah.

Kafin samun 'yancin kan Nigeria, shekaru da dama kakanninmu suka kwashe suna neman turawa su basu 'yanci su huta daga bauta, turawan da sukaga babu yadda zasuyi shine sai suka bamu 'yanci a takarda, amma sai sukayi wani wayo da dabara cikin ilmi ta yanda zasu cigaba da yin mulkin mallaka a kasarmu Nigeria ta hanyar kawo mana tsarin mulkin Demokaradiyyah.

Shi wannan sabon tsarin salon mulkin mallaka (Demokaradiyya) wanda turawan Amurka suka bijiro dashi, sun kawoshi ne a lokacin da wasu jiga-jigan shugabanninmu irinsu jinin Shehu Usman Dan Fodio kuma jikan Mujaddadin musulunci  Sardaunan Sokoto Sir Ahmadu Bello da su Sir Abubakar Tafawa Balewa (Allah Ya jikansu) suka dinga tayar da jijiyan wuya kan cewa lallai turawa su tashi su bar mana Kasa, shine sai turawan suka amince, amma sai suka kawo sabon salo na dabara a matsayin sharadi wanda zasu zamanantar da mulkin mallaka a ilmance domin Kasarmu Nigeria da Kasashe irin namu suci gaba da tafiya a irin tafarkin da turawan suka daura kasashen namu a kai.

Turawa sukace duk 'Kasar da takeso a bata 'Yanci, to wajibi ne ta rungumi tsarin mulki na "Demokaradiyyah" wanda suke yiwa fassara da cewa tsarin mulkin jama'a ne kuma domin jama'a, a cikin wannan tsarin mulki akwai alheri amma sharrinsa yafi yawa a kasashe irin namu, a zahiri turawa sun baiwa tsarin Mulkin Demokaradiyyah suna mai ma'ana,  a gurinsu duk wani tsarin mulki idan ba na Demokaradiyyah bane koda tsarin mulkin musulunci ne to zasu masa batanci da cewa Mulkin kama-karya, mulkin zalunci, mulkin danniya da take hakkin bil'adama, koda Kuwa Shugaban ya Kasance mai adalci a shugabancinsa wanda ba na tsarin mulkin Demokaradiyyah ba.

Misali da Kasashen Libya, Sudan, Jordan, Syria, Egypt, Kasashe ne da basa tafiya bisa tsarin mulki irin na "Demokaradiyyah" suna mulki ne yadda ya dace da addini da al'adunsu da ra'ayin gwamnati, wannan ne silar da takai ga turawa suka samar da 'yan tawaye/'yan ta'adda a cikin irin wadancan kasashe da basa bin tsarin mulkin Demokaradiyyah tare da basu goyon baya, wanda shine silar ham6arar da mulkin wasu Shugabannin, kuma ya zamo ajalin wasu shugabannin, daga karshe turawa suka kakaba musu tsarin mulkin Demokaradiyyah.

Akwai matsalili masu tarin yawa wanda Kasashe irin namu ba zasu iya yin gaban kansu wajen magancewa ba idan turawa ba su yarda ba, misali da abinda ya shafi matsalar tattalij arzikin kasa da tsaro, akalar sarrafa tattalin  arziki da tsaro yana hannun turawa, hatta abubuwa da suke faruwa na rikicin 'yan tawaye da ayyukan ta'addanci sabon salo ne da turawa suka kawo don su zamanantar da mulkin Mallaka su cigaba da satar dukiya suna kaiwa kasashen su.

Turawa masu zamanantar da mulkin mallaka suna amfani da bankin duniya su karya tattalin arzikin Kasar da suka ga dama a duniya, sannan suna amfani da manyan kungiyoyin kare hakkin bil'adama na duniya su karfafi ayyukan ta'addanci, suna kera manyan jiragen yaki da manyan kayan yaki na zamani, suna sayarwa a kasashe irin namu da ke fama da ayyukan ta'addanci a matsayin babbar hanyar samun kudadensu, wannan ya sa ba zasu taba goyon bayan a magance ayyukan ta'addanci a kasashe irin namu ba.

DUBA WADANNAN:

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN YAKIN BIAFRA

SHEKARU 58 DA SAMUN 'YANCIN KAN NAJERIYA CI GABA KO KOMA BAYA?

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN YAKIN BASASAR NIGERIA

Idan Gwamnati tana bukatar kubuta daga mulkin mallakar turawa na zamani sai ta cusawa matasa kishin Kasa da hadin kai a cimin zukata, sannan a saukaka hanyar neman ilmin boko, a wajabta koyon ilmin kimiyya da kere-kere, kamar misali da tsarin da tsohon shugaban juyin juya hali na Kasar Iran Ali Al-kumaini yayi, idan ya kasance matasa sun taso da kishin kasarsu, sun kware a ilmin boko da kimiyya, duk abinda ake bukata za'a iya kerashi a cikin Kasa, to babu shakka kasar zata iya kubuta daga tsarin mulkin mallaka na turawa.

Daga karshe ina addu'ah Allah Ya daukaka darajar Nigeria, Ya magance mana dukkan matsaloli da suke addabar Kasarmu Nigeria Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








Monday, 30 September 2019

KARANTA TAKAITACCEN TARIHI DR ISAH ALI IBRAHIM PANTAMI

KARANTA TAKAITACCEN TARIHI DR ISAH ALI IBRAHIM PANTAMI

An haifi Maigirma Ministan Sadarwa a Nigeria Dakta Isa Ali Ibrahim Pantami a ranar 20 ga watan Oktobar 1972 a unguwar Pantami dake Gombe, jihar dake Arewa maso Gabashin Najeriya.

Dr. Isa Ali Pantami

Marubuci: Datti Assalafy

Isa Pantami ya kasance ‘da ga Mallam Ali Ibrahim Pantami, mahaifiyarshi kuwa itace Malama Amina Umar Aliyu.

Ya fara karatun Al-Qur’ani a makarantar Allo kafin daga bisani ya shiga makarantar Firamare ta ‘Pantami Primary School’ inda a nan ne ya samu shaidar kammala karatun firamare, ya kammala karatun sakandire a makarantar Sakandire ta Kimiyya ta ‘Government Science Secondary School, Gombe.

Daga nan ne ya samu shigar jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) dake jihar Bauchi, inda a nan ne ya samu damar kammala karatun Digiri a fannin Fasahar Kwafuta a shekarar 2003 tare da samun Digiri na 2 duk a fannin, a shekarar 2008.

Pantami ya kammala karatun Digirin-digirgir a jami’ar Robert Gordon dake Aberdeen a kasar Sukotlan.

Dr. Isa Ali Pantami

Ya fara aiki a jami’ar ATBU, inda yake koyar da ‘Information Technology’ kafin daga bisani ya koma Jami’ar Musulunci dake Madinah a matsayin shugaban Rubutun Fasaha a shekarar 2014.

DUBA WADANNAN:

Karanta Takaitaccen Tarihin Sarkin Musulmi Ibrahim Dasuki

KARANTA TAKAITACCEN TARIHIN SHEIKH JA'AFAR MAHMOUD ADAM

KARANTA CIKAKKEN TARIHIN SHEIKH ABUBAKAR MAHMUD GUMI

A shekarar 2016, Pantami ya ajiye koyarwa, inda a nan ne shugaba Muhammad Buhari ya nada shi ya zama shugaban hukumar ‘NITDA’ a ranar 26 ga watan Satumbar 2016.

Ya kasance babban malamin addinin Musulunci na sama da shekaru 20, ya kasance limamin sallah Juma’a a Najeriya da kasar Birtaniya. - Jaridar Punch Newspapers

Yaa Allah Ka karawa rayuwarsa albarka, Ka gafarta wa iyayensa, Ka hada fuskokin su da nashi da namu a cikin Aljannah Madaukakiya Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








Saturday, 21 September 2019

KARANTA MUHIMMIYAR SANARWA DAGA RUNDINAR SOJIN NIGERIA

KARANTA MUHIMMIYAR SANARWA DAGA RUNDINAR SOJIN NIGERIA

Rundinar sojin Nigeria Operation Lafiya Dole tana sanar da al'umma cewa wasu kungiyoyin da ba na gwamnati ba (NGOs) da suke aiki a yankin arewa masu gabashin Nigeria suna cin amanar yakin da ake da 'yan ta'addan Boko Haram.

Operation Lafiya Dole


Marubuci: Datti Assalafy

Rundinar sojin tace akwai wata kungiyar NGO da take aiki a jihar Borno mai suna Action Against Hunger (AAH) tana taimakawa 'yan ta'addan Boko Haram da abinci da magunguna duk da gargadin da kwamandan rundinar Operation Lafiya Dole yayi mata na ta dakata da tallafawa Boko Haram amma sunki.

A takaice dai wannan ya sanarwan ya fito ne jiya Alhamis 19-9-2019 daga Kanar Ado Isah mataimakin baban jami'in hulda da jama'a na rundinar Operation Lafiya Dole.

Kwana hudu ko uku da suka gabata wani mummunan al'amari ya faru a garin Gajiram, duk da an boye labarin, maciya amana sun jibe magunguna a garin da kayan abinci, kawai sai 'yan ta'adda suka shiga garin, har ma suka kwana, sun kwashe maganin da abinci suka tafi jeji abinsu, ai an san wadanda suka jibge maganin, wani mataki aka dauka a kansu?

Yafi shekara 3 muna bayyana girman cin amanar tsaron Nigeria da wadannan kungiyoyin sharri suke yi a jihar Borno, shekaran da akaci amanata 2017 na rubuta budaddiyar wasika zuwa ga Maigirma shugaban kasa, gwamnonin Arewa, Mai alfarma Sarkin Musulmai da Manyan Sarakunan Musulunci, Manyan Malamai, 'yan majalisar Dattawa da na Dattijai, kungiyoyin Dattawa da na Matasan Arewa.

A cikin waskiyar na wallafa dogon rubutu nayi cikakken bayani akan yadda kungiyoyin sharrin suke taimakon 'yan ta'addan Boko Haram, nace ma wadanda na rubuta wasikar su umarci amintattunsu masana tsaro su gudanar da binciken sirri akan ayyukan NGOs din, a daidai lokacin da na wallafa rubutun hankalin wakilan NGOs yayi mummunan tashi, wani wakilinsu tsinannen Malami Ustazun karya maciyin amanar musulunci da Musulmai daga jihar Kano wanda nake zargin 'dan Luwadi ne, yazo ya kalubalanceni, aka hada baki dashi aka batar dani daga doron duniya a daidai wannan lokacin.

Na rantse da girman Allah babu abinda yake haifar da mummunan cikas a yaki da Boko Haram sama da wadannan kungiyoyin sharri saboda kawai neman kudi, amma wani mataki aka dauka akansu?

Watannin baya rundinar sojin Nigeria ta gano kungiyar UNICEF tana taimakon Boko Haram aka dakatar da su, amma a tsakanin awanni 24 manyan wakilansu na duniya suka zafafa kira ga mahukuntan Nigeria aka tilasta rundinar sojin Nigeria ta janye dakatarwan, suka cigaba da aikinsu na cin amana.

Duniya taji labarin a lokacin da tsohon Ministan Tsaron Nigeria Malam Mansur Dan Ali yayi magana a BBC Hausa yana fadawa duniya cewa kungiyoyin NGOs da suka mamaye jihar Borno suna taimakon Boko Haram saboda basa so a kawo karshen ta'addancin saboda sun mayar dashi babbar hanyar neman kudi da kasuwanci.

DUBA WADANNAN:

KARANTA BAYANI AKAN AIKIN MAMBILA HYDROPOWER PLANT DAKE JIHAR TARABA

KARANTA DALILIN DA YASA GWAMNATIN NIGERIA TA HANA SHIGO DA SHINKAFA TA KAN IYAKOKIN KASAR

Karanta Ma'anar Kalmar VAT a Mahangar Masana? Akan Su Waye Karin Harajin da Gwamnati Take yi Zai Shafa??

Wace kasa ne a duniya zata yarda da irin cin amanar da ake yiwa tsaron Nigeria?

Matakin da muke tunanin ya kamata rundinar sojin Nigeria ta dauka shine dakatar da duk wata kungiyar NGO da aka kama tana taimakon kungiyar Boko Haram ta kowace fuska.

Yaa Allah Ka mana maganin abinda yafi karfin mu Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode









Copyright © 2016 - | MuryarHausa24.Com.NG - All Rights Reserved.